Skip to content

Chapter 22

Chapter 22

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,200 words 0 views Progress saved
Download Book

tana gyaran d'aki su tayana, wani lokacin kuma suna d'akinta suna hira. Ba yanda Aunty Faty batayi ba akan ta hanasu anma sunk'i ji. Ranar Juma'a da safe akayi ma ma'aikatan albashi, bakin Ummy har kunne musamman dataga wannan karan shima dubu d'arin aka biyata. Dak'yar Mami ta yarda ta barta ta tafi gida weekend gida. Hankalin su twins sosai ya tashi ganin Ummyn zata tafi dan saboda ita gidan ke musu dad'i. Har bakin gate suka rakota suka koma cikin gida a sanyaye. Napep ta tara ta shiga, suna karyo kwanan layinsu ta hango gidan su da masu aikin gini kamar gyara yake a gidan. Da mamaki ta shiga tana bin ma'aikatan da kallo, dakunansu taga an had'e an fitar da two bedroom mai kyau, Mama ta fito daga Falor ganin Ummy yasa ta rungumota cikeda murna. "Mama wannan aikin fah" Hannunta Mama ta kama suka shiga cikin Palourn, nan Ummy ta saki baki tana kallan yanda gidan nasu ya koma, had'adden set d'in kujeru ta gani, ga tiles da aka malale falon dashi, sosai falon yayi kyau, tabi Plasman dake jikin bango har lokacin idanunta a warwaje "Mama wannan kayan daga ina" Baba ya fito daga d'aki yana dogara sandarsa yana murmushi "Muryan wa nakeji kamar na Ummyna" Dasauri ta k'arasa ta rungumeshi tana dariya "Baba ni ce" Ya shafa kanta yana cewa "Ba abinda zamuce ma yaron nan sai Allah ya mai albarka" "Baba Ya Bilal ya dawo neh? Dama nasan bai mutu ba zai dawo" Mama tace "Duk wannan abubuwan da kika gani, duk aikin Jamaludeen neh, kuma yace yayi dan Allah ne ba wani abu bah" Yatsine fuska Ummy tayi tace "To an gode" Ta shiga bedroom, nan ma taga an gyara shi tsaf harda sabon funitures, ta tab'e baki ta aje jakanta sannan ta fito. Albashinta ta mik'ama Baba kamar yanda ta saba, Albarka ya saka mata yace "Wannan karan ki adana kud'inki dan munada komai dangane ga kayan abinci" Ummy tayi murmushi tace "Tho Baba, anma yakamata mu sake komawa asibiti ka sake ganin likita" "Hakaneh" cewar Mama "Aa Ummy, nikam Alhamdulillah naji sauk'i, yanzu babban burina bai wuce naga kin daina bauta bah, kin koma makaranta ko kinyi aure" Mama tace "Komai Lokaci ne Mallan, Fatan mu ka samu lapia, komai yazo daga baya" Murmushin takaici kawai Baban yayi baice komai bah. Washe gari lahadi, masu aikin ginin basu zo ba suna hutu, yau D'anwake Ummyn tayi musu dan Baba nasan d'anwake sosai, bayan ta zuba musu nasu ta d'au nata ta fito tsakar gida kan tabarma tana ci. Ta saka loma kenan ta jiyo sallaman su Twins, dakyar ta iya had'iyewa suko mai zasuyi in ba dariya bah. Mik'ewa tayi dasauri ta rungumesu tana dariya "Sannunku da zuwa, ya akayi kukasan gidan mu" "Ya Jamal ne ya kawo mu yana waje" cewar Najma Ciki ta shiga dasu suka gaisa da Baba da Mama, sannan suka dawo waje dan ciki akwai zafi, d'an waken ta zubo musu suka soma ci suna santi, Ummy ko me zatayi inba dariya bah. Mama ta lek'o tareda rik'e hab'a "Oh ikon Allah, ashe ku nan zama kukayi kuka bar Yayan naku a waje" Sai a sannan suka tuna ashe da Jamal suke, Mama tace Ummy ta tashi tace mai ya shigo, turo baki tayi taja hijab a igiya ta fita, cikin mota ta sameshi yana waya, ta k'arasa ta juya fuska gefe tace "Ance ka shigo" Bata jira mai zaice ba ta koma ciki, shi dariya ma abin ya bashi Ummy sai kace mai Juju, wani lokaci ka gansu Lafiya suna shiri, watan kuma a yini ba'a masa magana bah. Da sallama ya shiga ciki, Najma da Najwa na zaune tsakar gidan suna cin abinci "Dama nan kukafi auki, Ci, Ci!" Najma ta b'ata fuska, Najwa ko Dariya tayi ta sake kai loma tana kallansa. Dariya yad'anyi ya girgiza kai ya shiga falon da sallama. Har k'asa ya tsugunna ya gaidasu, Ummy ta had'o mai d'anwaken. Ba ko kunya ya soma ci suna hira da Baba, Ummy sai binsu da kallon mamaki take ganin yanda suke hira kamar wad'anda sukayi shekara da sabo. Waje ta koma suka cigaba da hiransu da Twins, bayan sun gama Jamal yama su Mama sallama yace ma su twins suzo su wuce, Mama ta lek'o tace "Ummy ina ce kema yau zaki koma, kizo ki d'au kayanki mana ki bisu" Baki ta zungure tace "Mama ni sai anjima" Jamal yayi murmushi ya fita, har bakin mota ta rakosu tanata d'agama su Twins hannu, har yayi gaba ya dawo yayi parking ya fito "Wai Twins kad'ai kika gani neh" Ta galla masa harara "Ni su kad'ai na gani" "Koh" Ta kauda kai gefe "Zaki sani neh ai" "Zamu sani zakace" Yayi murmushi yana girgiza kai ya shiga yaja motan yabar anguwan. Sai bayan la'asar Ummy ta shirya tsaf dan komawa bakin aikinta, d'aki ta samu Baba dan masa sallama, ya rik'o hannunta yana cewa "Jamaludeen, Bahar da mahaifiyarsa duka ba abin yarwa baneh. Ki rik'esu Hannu bibiyu kinji" "Insha Allahu Baba" "Ki zama mai hak'uri a duk inda kike, ki kare mutuncin ki, ki zama mai biyaiyya da girmama nagaba dake, ki rik'e addininki, In kikayi haka insha Allahu bazaki tab'a tab'ewa bah. Kin faranta min Ummy, tunda na haifeki baki tab'a min abinda kika b'atamin bah, Allah ya miki albarka Ummy" "Amin Baba, Kai kuma Allah ya baka lafiya" "Ameen!" Ta fito sukayi sallama da Mama ta fita ta tari adaidaita ta hau ta koma gidan aikinta. Tana shiga dasu Twins tayi arba sunata murna, jakan hannunta suka amsa suka shigan mata dashi d'aki. Duk abinda sukeyi Aunty Faty na kallo, ranta sosai ya b'aci ta haura sama zuwa d'akinsu Tana mita. A ranar Aunty Zainab mahaifiyarsu Twins ta koma, su kuma zasu d'an yi hutu, Aunty Faty ko cewa tayi ba yanzu bah. Babban abinda ya d'aurema Ummy kai bai wuce rashin ganin Laurat bah, dan tun sanda zata tafi ta fad'a mata sati d'aya kawai zatayi gashi yau kusan kwana Shad'aya kenan. Da daddaren ranar Mami da Abba suna falon side dinshi, Mami tace "Alhaji magana nazo muyi" Yace "Ina jinki" D'an jim tayi tace "Alhaji har yanzu bakace komaiy kan alkawarin auren Jamal da Mabrookah bah" "Tho mai kikeso nace Maimuna" "Yakamata ace yanzu anyi auren nan, tunda ya samu Lafiya ga kuma aiki ya fara" Abba yad'anyi murmushi "Maimunatu kenan, abinda nakeso ki gane a nan shine, yanzu ba d'ah baneh, yanzu an daina wannan had'in. Gwara a bar yara su zab'i abinda sukeso" "Haba Alhaji yanzu ya za'ayi da alkawarin da aka d'aukan ma Yaya Faty, kuma itama Mabrookahn tana sanshi sosai, shima nasan yana santa" "Sanda kukayi alkawarin ai bana wajan, ba sai daga baya kike gayamin da alkawari bah" Fusata Mami ta fara ta juya fuska gefe "Mafita a nan shine, zan tarasu na tambayesu idan har duka suka amsa suna san juna shiknan" "Anma Alhaj...." "Aa Maimuna, wannan shine magana" Mik'ewa tayi tabar falon ta nufi side d'insu, Aunty Faty ta samu a falo ta sanar da ita yanda sukayi da Alhajin "Maimuna kina bani mamaki, yanzu ke bazak'i iya tank'wara d'anki bah" Shiru Mami tayi ta haura zuwa d'akin Jamal, bata ganshi

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82