Skip to content

Chapter 72

Chapter 72

Jamaluddeen Book One Complete Hausa Novels 1,201 words 0 views Progress saved
Download Book

jiranshi, tana ganinsu tare taja tsaki yad'anyi murmushi daidai sanda suka k'arasa saukowa falon k'asan, Hannun Mabrookahn ya rik'e suka fito su duka. Bai sake hannayen nasu ba saida suka kai k'ofar falon Abba, ya shiga da sallama suma suka bi bayansa, Chak Ummy ta tsaya ganin Bilal a falon, Jamal ya janyo hannunta suka k'arasa cikin falon sosai, dukansu a k'asa kan Carpet suka zauna, Cike da girmamawa Ummy ta gaishe su, ganin haka yasa itama Mabrookah gaidasu tana yatsine fuska. Jamal ya nuna Abba da Ammi "Alhamdulillah ku tayani murna naga Parents d'ina" Ummy ta d'ago dasauri cike da fara'a "Dagaske?" Ya gyad'a mata kai yana nuna Abba "Wannan shine Abbana" Ya nuna Ammi sannan ya nuna Areef yana cewa "Wannan kuma k'anina Areef" Kallo d'aya zakama Ummy ka gane tana cikin farinciki, Mabrookah ko sai yatsine yatsine take daga gefe. Ya d'an duk'ar dakai yana sosa k'eya "Ummmm Abba wad'an nan Ummmm Ma..Matana neh" Ammi ta rik'e baki da mamaki "Duka matanka?" Ya sake duk'ar da kai yana murmushi, Albarka Abba ya saka musu sannan yace "Baka fad'a mana meya faru ba bayan rabuwan mu dakai" Nan ya gyara zama ya zaiyane musu komai har zuwa ranar, Ammi kuka take sosai na tausayin d'an nata, Jin gagarumar gudunmawar da Ummy taba d'an nata yasa taji ta shiga ranta sosai. Kallanta kawai take tana zubar da kwalla. Ganin yanda Ammin ke kuka sosai yasa Jamal ya rarrafa ya rungumeta yana shafa bayanta "Its ok Ammina, yau ranar farinciki ne garemu duka" Ta d'ago kanta tana mai zubar da kwalla tana shafa fuskansa "We are so sor..." Yayi saurin sa hannu ya rufe mata baki yana girgiza mata kai, sosai Suka burge duka mutanen dake falon. Areef dake gefe yayi murmushi yace "Abba Lil sis fah na gida" Abba yace "Hakane" Ya juya ga Jamal yace "Areef nada k'anwa sunanta Areefa" Jamal ya saki lallausan murmushi cike da faribciki yace "Woaw ashe inada k'anni dayawa" Duka falon sukasa dariya, waya Abba ya d'auka ya kira Areefan tana d'auka ta fashe da kuka tana shagwab'an barinta da akayi ita kad'ai, Abba ya soma lallashinta sannan yace gobe tasa driver ya kawota zaria idan suka iso sai ta kirasa. Cikin wani irin ihun murna ta amsa tare da kashe kiran. Har lokacin Ammi bata daina kallan Ummy bah wacce kanta ke k'asa tana ta murmushi, Ram yace "Bilal kayi hak'uri akan abinda ya faru, rashin sani neh" Bilal yayi saurin girgiza kai yana 'yar murmushi "Babu damuwa, rashin sani ne ai" Jamal ya sake bashi hak'uri, nan ma ya nuna babu damuwa. Sannan ya mik'e ya musu sallama dan zaije gida, driver Jamal yasa ya d'aukesa ya kaisa gidan bayan ya masa kyautar kud'i yaki karba. Gaba d'aya Jamal jinsa yake cikin wani irin farinciki, ji yake kamar an d'auke masa kaya. Mifzal da Ram suka musu sallama suma suka tafi, Jamal ya kalli Areef yace "Bro zo ka tayani wani aiki" Ba musu Areef ya mik'e yabi bayansa, Mabrookah na ganin sun fita ta mik'e tana wani cin magani tabar Falon, Ammi ta kalli Ummy tace "Tashi kije abinki Ummy Allah ya miki albarka" Cikin jin kunya ta amsa ta mik'e ta musu sallama cike da girmamawa. Ammi ta kalli Abba bayan Ummyn ta fita tace "Yau na fara ganin yarinyan nan, anma wallhi ta shiga raina sosai" Abba yace "Nima haka wallahi, kum daga gani tanada natsuwa da kamun kai" Ammi ta gyad'a kai tana murmushi. Mabrookah na fita taga Jamal da Areef sun shiga side d'in Mami, harta juya zata koma nasu side d'in sai kuma ta juyo tabi bayansu. Suna shiga Jamal yace "Wannan side d'in Mami ce itada wicked Sistern tah. Inaso ka tayani mu fitarda komai na ciki inaso Ammina ta dawo nan" Karaf a kunnen Mabrookah wacce take k'ofar falon tana kallansu fuska a had'e, ta k'araso ciki dasauri tana huci "Wallahi bazai yuwu ba Ya Jamal, me kake nufi a fitar da kayan Iyayena asa wani" Ya juyo ya kalleta rai b'ace "Saboda masu gidan wanda suke da iko da komai na gidan zasu dawo nan da zama" Areef ya haura sama abinsa yana tab'e baki dan kallo d'aya yama Mabrookah d'azu yaji sam bata masa bah, "Babu wanda ya isa ya fito min da kayan iyayena, kaje ka aro iyaye ka kawo to wallahi bazai yuwu bah, wad'an nan mutanen basu isa su..." Lafiyaiyan mari taji a fuskanta ta d'ago idanunta da sukayi ja tana kallansa da b'acin rai tana nuna kanta da hannu "Ya Jamal ni ka mara akan wad'an nan banz..." Wani marin ya sake d'auketa dashi ta fashe da kuka tana gagaya masa bak'aken maganganu, Areef ne ya sauko d'auke da Manyan Trolleys guda biyu yana jansu da kyar, ta k'arasa ta sauri ta rike akwatunan "Ina zaka kaisu, wallahi karka sake ka fita dasu" Jamal ya kira sunanta cikin kakkausan murya "Ki shiga taitayinki Mabrookah, ina raga miki ne kawai saboda Alk'awarin dana d'aukan ma Abba bazan rabu dake bah. Karki sake ki kaini bango" Areef iyayen k'eta ya d'anyi dariya ya fisge Akwatin yayi waje, ta k'arasa inda Jamal d'in ke tsaye tana kallansa hawaye na fita daga idanunta "Ka cika butulu Jamaludeen, kai butulu neh, ko me Mami da Mommy suka maka bai kamata ka sakamusu da haka bah, Kai butulu ne" "Karki k'ara kirana da butulu" "Na fad'a kai Butul..." Wani irin shak'a yakai mata dan gaba d'aya takaisa bango ta saki k'ara a wahalce idanunta gaba d'aya sun fito, Areef ya shigowa yaga abinda ke faruwa ya fita dasauri zuwa inda su Abba suke ya shaida musu, a tare suka taho dukansu da sauri. Har lokacin Jamal na shake da ita idanunta duk sun bulluk'o tana kakari kamar zata shid'e "Ban kira Mami da Aunty Faty butulu ba saini zaki kira da butulu, sun kashe min Abbana, sunyi k'okarin kashe min Matata dani kaina, duk wad'an nan ba butulci baneh, bariiii" Abba ya shigo falon tare da kiran sunan Jamal da k'arfi "Jamal! Ka saketa karka kashe musu 'ya" Ya sake mak'ureta idanunsa sai lumshewa take tana cigaba da kakari "Barin kasheki sai ki kirani da butulun da huja" Luuuu tayi zata fad'i Ammi ta k'arasa ta rik'e hannunsa tana hawaye "Ka saketa Jamaludeen, kar zuciya tasa kayi abinda zaka dawo kana danasani" K'in saketa yayi, Abba gaba d'aya ransa ya gama b'aci "Ashe Bamu isa mu hanaka abu ka hanu bako" Ya juya baya fuskansa ba walwala "Hakan ya nuna mana bamu da iko akanka" Sakinta yayi ta fad'i Luuu ta sume a wajan, baga d'aya fuskansa da idanunsa sun koma ja, Ammi ta rik'o hannunsa tana hawaye "Kome ta maka bai kamata kayi mata haka bah" Taja hannunsa ta zaunar dashi sai huci yake kamar zaki "Areef samo masa ruwa" Ruwa ya d'ibo a dispensern dake falon ya mik'a mata ta ba Jamal d'in, ba musu ya kafa baki ya shanye tas yana sauke ajiyar zuciya Abba ya k'arasa inda Mabrookah ke kwance ya yayyafa mata ruwa ta sauke ajiyar zuciya a wahalce tana kakari, dakyar ta mik'e tana rik'e da wuyanta ta fita daga side d'in dasauri. Ammi tace "Areef wai meya faru neh" Nan ya karkace ya labarta musu duk

Table of Contents

Chapters

82 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82