Skip to content

Chapter 98

Chapter 98

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,252 words 0 views Progress saved
Download Book

na manta''ya fada yana kissing goshinta kana yaja musu bargo ya rufesu,tun tana a darare a jikinsa har ta saki jikinta jin shiru bai qara motsawa ba,da alama ma bacci yayi awon gaba da shi,don dole ta saki jikinta amma still tana jin yadda zuciyarta ke gudu,daga bisani ita din ma wani daddadan bacci ne ya sureta *mrs muhammad ce*πŸ‘‘ πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½ πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’– πŸ’– *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊ πŸ’– Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* 5⃣4⃣ *_Allah yana cewa cikin alqur'aninsa mai girma''haqiqa ji da gani da zuciya dukkansu akwai tambaya a kansu''(ranar qiyama game da abinda suka ji ko suka gani)_* lokacin da mami ta koma gida ita da baaba uwani bayan tayi horn an dage mata makeken get din gidan ta wuce ciki sai ta lura duka ma'aikata da security na gidan na tsaye ne cirko cirko a guri guda kan ta fito daga cikin motar ibrahim ya qaraso cikin girmamawa ''lafiya ibrahim,me ya faru na ganku a tare guri guda?'' mamin ra fada tana kashe motar tare da qoqarin fitowa daga ciki ''wallahi mami hajiya nene ce?'' ''nene?,me ya faru?''ta tambaya don wata irin tsanarta tame ji na mamaye zuciyarta,macan da ta jefa tilon danta cikin bala'i,macen da taso ganin bayan su ita da yaran da tafi qauna abdallah da maryam,ta mata alkhairi ita kuwa ta maye gurbinsa da sharri,ta zauna da ita zuciya daya yayin da ita take zaune da ita da ziciyoyo barkatai marasa kyawun manufa,ko a mafarki daidai da rana daya bata taba qullatar nenen da sharri ba sai gashi abun mamaki ita din taso abzata cikin wani rami mai tsananin hadari badan Allah ya dibi ysarkin zuciyqrta ba ya tsallakar da ita daga dukkan wasu tarakuna data dana wa rayuwarta ''ina baya ina rangadin gidan su husaini kuma suna nan zaune da sauran abokan aiki,kawai saiga husaini yazo yayi kirana waiga nene can babu ko kaan arziqi sai daurin qirji ta fito a guje daga bangarenta wai fita zatqyi nemansu adnan,kuma idan ta gansu sai ta kaagesu don sun cuceta sun ha'inceta sun gudu da dukiyarta,da farko na zata ma qarya yake saboda naga ko motsi bata iyawa komai sai an mata,amma da na bisi sai na gasgata maganarsa,to muna shawarar yadda zamu hanata fita sabida kowa yana tsoron tabata tunda ba muharramrsa bace kawai sai ta faki ido ta fice a guje,muka bita tuni har ta fita daga gidan,muna daf da zamu cimmata wata mota ta tsaya,wadan nan mutanen da kika ce kada mu sake barinsu kwanaki su shigo gian nan sune aahe a ciki suka figeta suka jefata ciki,na sa bindiga na harbi tayar har sau biyu saidai ban samesu ba'' shiru mami tayi tana jinjina kai,ibrahim ya kuma cewa ''amma mun dauki nimber din motar,gata''tsaidashi tayi ''babu bin sahunsun da zamuyi ibrahim ka qyaleta da su,qila hakan da Allah ya mata shine mafi alkhairi a gurinmu,bata dace da zama cikin mu ba shi yasa Allah ya hadata da mutanen da suka dace da ita''tana maganar ne yanayin fuskantar ya sauya saboda bacin rai da tashin hankali,ibrahim ya dubi mamin,shekara da ahekaru suna zaune tare,macace mai tausayi jin qai da taimako ga na qasa da ita,ya tabbatar ba qaramin abu bane zai sanyata tace a qyale nene ba,duk da idanuwansu sunga wasu muggan ayyukan na nene da yadda ta so maida uwar dakin tasu mamin amma ya tabbata da abinda ta aikata din yafi haka,take kuwa ya cukuikuye takardar ya yagata gutsi gutsi ''ku koma bakin aiminku ibrahim,kowa yasa cikin zuciyarsa tamkar ma baiga abinda ya faru,irin nata hukuncin da Allah zai mata kenan,don na tabbatar ba mutanem arziqi ne suka dauketa ba,kowa ya shuka na gari kai nasa'' ''gaskiya ne mami,Allah ya shige gaba'' ''ameen''ta fada tana juyawa cikin gidan,cikin zuciyarta tana qara jin imani kan cewa duk abinda zakayi kayishi domin Allah,matuqar kace don wani zakayi shi to kana tare da wahala,zaka kyautatawa mutum iyakar iyawarka da zuciya daya amma shi sam bai gani,qarshe ya buge da cutar da kai ko ya shiga sahin manyan maqiyanka na farko,amma idan kayi ne don Allah koda shi din wanda ka yiwan bai gani ba baka da kaico ballantana asara zaka samu ladan aikinka ne gaba ga Allah,Allah kasa mu dace,ka bamu ikhlasi Sai data sake wanka tayi sallah tana kan abun sallar ta dau wayarta ta kira daya cikin qannenta sa'adiyya sukayi magana kan saukar qur'ani da aka raba makarantu makarantu,ko dq can lokacin marigayi alhj abdul-kareem mai nasara an musu,bayan mutuwarshi ne daga baya ta watsar,a yanzu kam ta dauki dambar ci gaba da sawa ana mata don ta fuskanci duk yadda kakai ga kirkinka kamun kai da kayuatatawa mutane wani yana nan duk duniya babu wanda yaqi jini sama da kai koda naman mahaifiyarka zaka dinga yanka kana dafawa kana bashi yana ci tsabar so,sadiyyan ta gaya mata an kammala kaso na farko gobe zasu dora kana sukayi sallama cikin 'yan uwan nenen mami ta nemo matar babanta tace suzo su kwashe duk wani abu da ya danganci nene daga gidan don tuni kowa ya sani alfarma karamci sa darajar zaman tare yasa mami ta bar nenen a gidan,matar baban nata cewa tayi gaskiya babu abinda ya shagesu da kayan nenen,don bata manta irin cin mutuncin da tayi musu kan gadon mijinta na farko,hatta da mahaifinta ya dade da zare hannunsa cikin lamuranta mamin tace dole kam su debe don sun gama zama tare da nene matar baban nata ma yaba mata sukayi zaman datayi da ita don sunga namijin qoqarinta ma data zauna da ita ba dangin iya babu na baaba tsawon shekarun nan Da qyar suka zo suka debe komai na natan suka loda a kodi kura,part din ya koma wayam babu ko tsinke nata bare na 'ya'yanta,sai a lokacin mamin ta fara jin sanyi cikin zuciyarta ''na barki da Allah nene,ko iya haka ma ya ishi yan baya ishara''abinda mamin tace kenan πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒ Qal gidan yake a share kamar kowanne lokaci,rairayin filin gidan tas kamar an zauna an tsince dattin cikin,banda shati shati na tsintsiya da alamun yayyafar ruwa da suka sa qasar ta danyi danshi da qamshi babu komai gidan shiru yake kasancewar babu kowa sai ita da abdallan kawai,inna wuro ta je cikin garin gaya bikin sunan wata jikarta,tsoho alhaji kuwa kano ya tafi karbo jakarsa a hajj camp da yake kayan sun dan samu tsaiko sai ranar suka iso,ya dauki mustafa suka tafi tare don yafi jin dadin tafiyar qasan rumfar yake a zaune kan wheelchair dinsa sanye da baqar t.shirt da red din trouser mai sulbi da kyau,yayin da maryam keta kai kawo na hada abincin dare idan ka dubeshi a haka sai ka zaci tabbas karatunsa yake tuquru saidai ina zaman sa'ido yayi don da zarar ta kuya zqi zuba mata ido har sai ya fuskanci tana shirin sake waiwayo wa,wani kyau yaga ta yi masa cikin baqi da ja din pakistan riga da wando,duk da rigar har gwiwa take amma gefe da gefe an tsaga shi wanda hakan ya sake taimakawa wajen fidda sharp dinta,ta nanade kanta da baqin dankwali da ya sake fidda hasken fatarta muraran,sau tari yakan raya cikin zuciyarsa kodai

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138