Chapter 137
Chapter 137
amatullah mukayi magana da abdur rahim,shikam yace mai binta mai sunan mamana yarinyar inna hadiza ta masa duk duniya so yake du Allah a bashi aurenta,adda ta taimakeshi kada ta hanashi'' ''ok....abdur rahim abokin hadin bakinka koοΌ''dariya ya qyalqyale da ita itama ta tayashi,din duk lokacin da suka tuno da moments din a yanzu nishadi da dariya yake sasu ''kinsan kuwa sanda yana zuwa mini zance idan yazo din yadda kikasan na mutu sabida kishi,zirga zirgar da nake muku fa take hanashi sakewa maza maza yake tafiya,zaki ga yana yawan duba waya nike masa tex nace ya gaggauta tafiya hakanan fa,ke kuma kiyita jin haushi ke a lallai saurayinki abdur rahim baya dadewa yake tafiya,bakisan abdallah bane a rigar abdur rahim'' dariya ta saka ta kama dogon hancinsa tana ja ''bansan so yakan iya farawa da qi da fada ba sai a lokacin,sam bansan sonka ke yawo cikim jinina ba,a lokacim nayi zaton qinka ma nake ashe wani bala'e'en so ne ya dabaibayeni''wani dadi yakeji,har kullum yakanji sanyi na ratsa zuciyarsa idan maryam na fallasa masa sirrin zuciyarta bai gajiya da jin irin son da take masa,ya dan hade fuska kana yace ''amma fa har yau ina sha'awar in qara aure,mata biyu nakeson nayi''kicin kicin tayi ta motsa mata kishinsa da takeyi mai bala'in yawa,bai ankara ba qwalla ya gani na shirim zubowa,babu shiri ya sanya halshensa ya shanye abinsa tas kana yace yana mai girgiza kafadarta yana murmushi ''haba uwar 'ya'yana,aini tun daga kanki uwaye mata basu sake haifar mace ba,har yau ke kadai nakewa kallon mace a duniya''murmushi ya subuce mata ta boye fuskarta tana cewa ''nikam ban hanaka qara aure ba idan Allah ya riga da ya rubuta cewa qadararka ne,amma ka sani ina tsananin kishinka haka yake cikin jini da halitta ta bazan iya kankarewa ba'' ''please mu bar ma wannan maganar kinji dear na''yayi magabar yana sake boyeta cikin faffadan qirjinsa tare da nuna mata zallar soyayya ππππππ Sai kusan sha daya suka fito falon masaukin nasu,tun takwaa suke jiyo,hayaniyar yaran amma abdallah ya duqunquneta ya hanata fitowa,ko breakfast ya hanata fitowa ta hada musu yace kowa yau yaci haquri sai ya gama hutawarshi shima,haka nan ya biye masa suka sha baccinsu kafin su tashi suyi wanka su fito Duk sun hautsine falon da kayan breakfast abdul ahad nata kai kawon gyarawa,haka yaron yake da qwazo tamkar mace ya iya aiki bakin gwargwado,don sau tari shike kamawa maryam wani abun idan aiki ya hade mata,misali idan zasu tafi makaranta da safe,ya iya hadawa kowa abincin tafiya makaranta cikin lunch boxs dinsa wanda bai wuce chips waina da indomie,hakanan shi zai hadawa kowa ruwan wankansa yaje yayi,wankan ne kawai bata barinsa ya yiwa su amatallah(hakan kuma nada kyau sabida koyawa yara kunya da sanin mutuncin tsiraici tunda akwai bambancin jinsi tsakaninsu shi namiji ne su kuma mata ne),abdus samad ke riqe da gorar ruwa ya hana amatul jabbar sha,sai binsa take suna kewaye falon,da sauri abdul ahad ya cafkoshi ya riqeshi kana ya tsugunna gabansa ''bata tasha abdys samad,bakasan cewa babu kyau baοΌ,akwai matar data tsare mage ta hanata ruwa da abinci har sai data mutu ta sanadin haka Allah ya sanyata a wuta,hakanan akwai karuwar da ta shayar da kare ruwa ta sanadin haka Allah ya gafarta mata ya sanyata a aljanna,ka sowa dan uwanka abinda kake sowa kanka kaji,ka hana kanka abu ka bawa dan uwanka matuqar ya fika buqata sai Allah ya saka a aljanna''jikin abdus samad yayi sanyi ya miqawa amatul,jabbar ruwan yana cewa kiyi haquri Ba qaramin burge abdallah da maryam yaron yayi ba,abdallah ya dubi maryam ''kin ganiοΌ,rainonki,ne fa uwa ta gari abar alfaharin miji da 'ya'yanta''sai ta dora kanta bisa kafadarsa tana murmushi kana tace''harda gudunmawar jajirtaccen uba kamar kai''amatul jabbar ce ta fara ganosu da gudu ta qaraso tana abdallah yasa hannu ya dagata sama yana zagayawa da ita,abdul ahad da abdus samad suma suka qaraso suka kai har qasa suna gaidasu kamar yadda suka saba,hannu suka dira saman kansu suna amsawa kamar yadda suka saba sannan suka sumbacesu suka sa musu albarka(manzan Allah s a w yace duk wanda bai sumbatar 'ya'yansa babu mamaki Allah ya cire rahama tausayi da jin qai daga zuciyarsa,sumbatar 'ya'yanmu sunna ce mai kyau suna ce ta annabinmu bata yahudawa ba,musamman yara qana na tunda a wannin zamani da al'ummarmu bazaiyu ka sumbaci danka babba ba,fitina tayi yawa cikinmu,saidai fatan samun sauqi) abdul ahad ke gaya musu mami da amatul lah sun tafi harami,tace sa biyosu a baya,karyawa suma kawai sukayi suka tasa yaran a gaba sai harami don babu nisa can da yawa tsakaninsu hakan yasa a qafa suka tafi πππππππ kwanansu biyu hudu da dawowa nijeria suna fama da 'yan taya murna,hakana suka gama yanke shawarar bayan abdul ahad din ya kammala secondry dinshi zasu barshi ya tafi madina ya qarasa karatunsa a can don hukumar qasar ta dauki nauyin karatunsa daga matakin degree har illa masha Allahu kwana biyar suka gama watstsake gajiyarsu wanda yazo daidai da lokutan da suke warewa don ziyarar yan uwa da dangi,mami kadai aka bari a tamfatsetsen gidan da abdallah ya narka gari guda ya dauko maminsa ya dawo da ita cikinsu wancan ya barwa mero wadda tuni ta koma maryam dinta ko muce maman sayyid wadda a yanzu yaranta uku,bintu ce ta fari takwarar mami suna kiranta walida,sai hamza wato sayyid sanann zainab,mero ta zama babbar mace sosai itama,don mami bata barta da dubun jahilci ba sai data zuba kudade sosai meron tayi karatu ta koma maryam kabiru hamza sak ba mero ba wasu lokutan da mamin ake tafiyar musamman idan bangaren yan uwan abdallah ne,wannan karon shi ya hana yace ta zauna ta huta hakanan yaushe duka duka suka dawo daga tafiya shikam ba za'a qarasa masa uwa ba,tuni dama ya sanya mamin ta ajjiue duk wani aiki,zaune take kawai aikinta dai research ne kawai kan sabbin cituttuka,tana daga zaune take,bada tata gudunmawar ta hanyar wallafa littattafai da suka shafi bangaren likitanci kamar kowanne lokaci wannan karon ma sun zafa dangi soasai cikin yan kwanaki inda suka yada zango a gudan lubabatu don ayi bikin sunan takwarar maryam da su,suna kam yayi armashi matuqa,maryam tayi rawar gani sosai wanda komai hassadarka sai ka yaba mata,ta zama uwa yaya kuma matar aboki duka ita kadai,hakanan ta nunawa takwararta gata sabida tulin kayan barka da hidima data dinga yi,da daddare abdallah yazo ya kwashe iyalin nasa sai gida don yace ya gaji da zaman kadaici shi da mami,gidan ya musu shiru babu dadi ko kadan,a sashen mamin yaran suka kwana abinsu dom suma sunyi kewar kakarsu kamar yadda tayi kewarsu,hakan ya bawa abdallah da maryam dinshi damar cin karensu babu babbaka don kullum ganin junansu suke tamkar sabon ango da sabuwar amaryarshi *********** Tako ina rayuwa ta musu kyau,dukkan wani abun qi Allah ya kawar musu da shi,hakanan ya shiryar musu da zuriyyarsu kan kyakkyawar turba,a yanzu maryam ta zama mudubin gidan baki daya,bama gidan ba hatta family dinsu kowa cikin inuwarta yake,tuni ta aurar da jamila da kulu yanzu a qannen nata baifi mutum hudu ya rage mata ba,kullum cikin sa albarkar iyaye take musamman babansu malam amadu da a yanzu ya samu rufin asiri fiye da zato,girman nan nata wanda ada aka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138