Chapter 72
Chapter 72
baku dama ku gaggauta warware harqallar da kuka qulla dani'' ya juya zai wuce adnan yasha gabansa cike da taurin kai da jin shima karansa ya kai tsaiko yana ciccije lebe cikin son nuna shima jan wuya nebayan shi kansa yasan fanko ne lamba daya,kafin yace komai yasa kan wuqar hannunshi ya daki kanshi saiga adnan din a qasa,ihu nene ta saka tayo kansu,da tsinin wuqar ya juna ta ta koma baya tayi luf sai da suka kammala ficewa ta saka kururuwa ta biyo bayansu ko Allah zaisa taci sa'a wani daga cikin security din sun dawo suyi ram da su,saidai ina,babu wanda ta samu bakin get din kamar yadda ta watsa su don gabatar da aikinta ππππππ ta kai ta kawo tayi hakan ya kusa sau goma sha biyar,ji take kamar zata hau bori ko hauka kafin ta samu guri ta iya tsugunnawa,ta dubi adnan da kanshi yasha dauri da bandeji da zaharkyya wadda ke zaune tana faman hade fuska,babu wanda take ganin laifi sama da nene,don ita kam ta gaji da wanna jeka ka dawo din,ta riga da ta yanke ma kanta hukuncin abinda zata aikata matuqar wannan karon haqarsu bata cimma ruwa ba kamar sauran lokutan baya ''babu shakka cikin hisham da maryam akwai wanda ya fidda abdallah daga cikin gidan nan,ko kuma daya daga cikinsun ya aikata hakan,kuma nafi zargin wanna shaidaniyar ce marya,tabbas kuwa''ta fada tana guada kai hadesake tabbatarwa kanta ''qwarai kuwa nene,nima na zargi haka tunda kinga fitarsu ana gobe za'a gudanar da aikin,cikinsu akwai wanda yake da hannu kan tsirar abdallah''inji zahariyya,shikam adnan ya kasa magana ta kanahi yake,tsanin ciwo yake masa kamar zai tsage gida biyu har zumbur nene ta miqe tana fadin ''wallahi basu isa ba dukkansu,duk wanda yaci tuwo da ni miya yasha'' ππππππ Tana cikin kitchen tana qoqarin hada masu abincin rana ta jiyo hisham na qwalla mata kira,cike da mamaki ta ajjiye abinda take yi din ta fito don bata taba jin ya mata makamancin irin wanna kiran ba tashin hankali ta gano qarara cikin idanunshi ''dauko duk abinda kika san kina da buqata ki sameni a mota na riga da na kai andallah ciki,babu lokacin bayani na miki shi a hanya'' bata tsaya tambayar ba kuwa,ta koma kitchen din a gurguje ta kashe gas din ta ahiga dakinsu da suka sauka ta dauki iya abinda take jin zata iya buqata ta fito ta taddasu cikin mota Tafiya yayi ta kusan mintina hamsin har suka fara barin ainihin qwaryar birnin kano sanna yayi parking a nutse ya dubeta ''maryam,na samu bayanan sirri daga daya daha cikin security din gidansu abdallah wanda nake biyanshi bayan barinmu yake samin ido kan duk wani motsi da yanayi da gidan ke ciki,don na tsammaci dama lallai wani abu na iya faruwa kan barinmu gidan da abdallah da mukaui,hasashena kuwa ya tabbata ya zama gaske iya,suna na ne ma farko cikin jerin mutanen da nene ke tuhuma,don ta saka amata bincike kan inda nake,yanzu haka mutanen na kan hanyarsu ta zuwa gidana,dalilin barowarmu gidan kenan'' kuka ne ya qwacewa maruam,wannan wace iriyar mace ce neneοΌme ta dauki rayuwar duniya,baza'a mutu baοΌdawwama kowa zaiyi yana abinda yaga damaοΌ,me take nema ne cikin duniyar da dukkanta bata kai qima da darajar fika fikin sauro ba agun Allah,wanne jin dadi ne a ginta ta kashe ran mumini wanda qimatsa tafi ka'aba agun AllahοΌ,tana tsammanin idan ta aikata hakan taci bulus ne ko kuwa,zata taira daga hisabi da zabar Allah neοΌdukkan amsar itace a'ah,babu ''a halin da muke ciki maryam kuka babu amfanin da zai mana,ki tsaida kukan mu nemi mafita'' tabbas maganar hisham haka take,ba bata lokaci ta ciro wayarta ta sake kiran mama wadda basu yi awa biyu da yin waya ba,magan sukayi ta kimanin minti talatin da ita kana ta kashe wayar ta dubi hisham kasancewar handsfree ta saka yaji komai kansa ya gyada ''maganar mama gaskiya ce,kuma tsarin nata yayi,nima da mun isa gobe zan wuce katsina hometown namu''ya fada yana mai gamsuwa da bayanin maman yana kuma sawa motar key,ta juya ta sake kallon abdallah har yanzu idanunshi a lumshe yake,babu baki balle ya bayyana abinda ke cin ransa,ta tabbata ba magana daya ke dawainiya da zuciyar abdallah ba,suna da dama,koda bao jude idonsa ba,koda baiyi,magana ba tana ki a jikinta zuciyar abdallan a quntace take,takan tashi kokawa afili da boye duk da shi din tsananin jarumtarsa bai taba barinta taga hawayensa ba Da taimakon bayanin da mama ke masu a waya suka kai ga isa qauyen NI'IMA dake cikin qauyen gaya,tun daga shigowarka garin zaka bawa kanka amsa,tabbas qauyen yaci sunanshi ni'ima,qauye ne da Allah ya wadata su da yawaitar korayen shuke shuke qoramu dabbobi da lullumi ma'ana rashin haske da zafin rana duk da haka sai da sukayi tambaya kafin su kai ga isa ainihin gidan da suke nema,gaya garin kakanninta ne tana zuwa lokaci bayan lokaci saidai qauyen ni'ima din zata iya irga iya adadin zuwanta tunda bata da wani shaqiqin da zata zo gunsa face wannan tsoho qwaya daya da yake qanin kakanta *mrs muhammad ce*π πππβπ½βπ½βπ½ [6:27pm, 9/22/2017] Hugumaπ: ππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊ ππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊ ππΊππΊ ππΊπ πΊπ π *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πΊππΊππΊπ πΊππΊπ πΊππΊ ππΊ π Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*π‘ *_home of expert and perfect writers_* βΆ4β£5β£ *_Mazan Allah S A W yace:ku umarci 'ya'yanku da yin sallah suna da shekaru bakwai,sannan ku dakesu saboda ita idan suka kai shekaru goma,kuma ku rarraba musu gurin kwanciya(ma'ana ya zama gurin kwanan maza daban gurin kwanan matan daban yayin da suka cika shekaru goma)_* Gida ne ginin qasa kamar yadda yake kasancewa ginin gidajen qauyuka,saidai wannan ya dan banbanta da nasu damin uasha shafe da ruwan makuba,hakanan ginin sumul sumul yake sakamakon fulastar kar qasa da aka yi masa da kuma makubar da akabi aka shafe ginin da ita. Maryam ce ta fara shiga,kamar yadda muka sani yan uwanmu na karkara basa gini quntatacce hakan ce ta kasance ga wannan gida,babban tsakar gida ne mai girma wanda babu sumunti a qasan sa,turbaya ce saidai ta sha shara fes da ita,ga alamun shatin tsintsoya ne,daga can quryar katangar gidan garkene na dabbobi dake a tsaftace shima,sai rijiya daura da shi wanda lema ce duk a bakinta da tukwanen qasa da aka kikkife da alamu wanke wanke aka gama agun babu jimawa. ta sake yin sallama kin shiru ba'a amsa ba karo na uku,cikin daya daga dakuna hudin dake jere taji muryar matashiya na amsa mata,ta fito sanye da roga da zani na atamfa wadan da suka danyi haske saboda dan jimawar da sukayi a duniya,maryam ta duba itama ta kalleta ''don Allah inna wuro faοΌ''maryam ta tambaha,sai ta juya ta kalli dakin kana ta kalli maryam ''tana ciki salla take amma yanzu zata....''' ''wake sallama ne mero,a shigo mana'' muryar inna wuro ta katsesu ''inna wuro baqi kikayi'' ''kaddai ace su meramu ne har sun iso haka da wuri''ta fada tana yunqurin fitowa,kasancewar ta san zasu zo din mama ta kirata awaya ta mata bayanin zasu zo din ta wayar mustafa jikan gidan. hannunta dauke da tabarmar kaba sabuwa dal ta fito,dattijuwa ce wadda aqiyasce zata doshi shekaru sittin,tsaf da ita cikin cikin atamfar itama da hijabi ruwan madara,fuskarta ta fadada da fara'ar ganin maryam
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138