Skip to content

Chapter 127

Chapter 127

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,287 words 0 views Progress saved
Download Book

kuma mun sake watanni kace zaka je?,tab,aikam,nazan yarda ba''dariya taso bashi,sai ya hade hannayensu ''is ok,indai kina son na tafi to ki share hawayen kinji''da kai ta amsa masa ta fara sharewar yana tayata,sai da yaga fuskar tata tayi fes sanann ya ciro mata hijabi ya saka mata,ya kama hannunta suka sauko,ya dubi fuskarta yadda tasha kuka sai yayi sha'awar tsokanarata ''ashe maryama ta abdallah ce,ashe maryama na mutuwar son abdallah,ashe rabuwa da masoyi da daci''yayi maganar cikin salo na waqa,sai ta fara diddira qafafunta cikin shagwaba,baya yadan ja kana ya kama baki ''iyeeee,naga fa alamar yammata kin warke,irin wannan tsalle haka,kodai na fasa tafiyar nan na zauna aci gaba da daukan darasi mu tsinki fure sosai''ba qaramar dariya ya bata ba,abdallah badai iya tsoka na ba idan yaso,sai ta fada jikinsa cikin dariya,shima baiyi qasa a gwiwa ba ya tarbeta ya rungume abarsa tsam yana jin duminta da qamshin azababben turarenta,sai da ya gama bata hot kisses sannan suka fito Tana kan kafadarsa daya kafadar tata rataye da briefcase dinshi haka suka jero har harabar gidan,bai damu da securities dinshi ko hisham dake tsaye agun ba ya sake qwaqume abarshi,duk da kunyar da take ji amma ya hanata motsawa a haka har suka isa motar da zasu tafi din,ko kallo hisham dake waje a tsaye shida lubabatu yana zabga masa harara bai isheshi ba,sake janyita yayi ta mata kiss a kumatu da goshinta,yasa dan yatsansa yana dauke mata hawayen da ya fara silalo mata ''no baby,no,hawayenki karyamin duk wani qwarin gwiwa yake,ki bar kukan nan haka,bari na gaya miki abunda zaki min qwaya dayq da zaisa na kuma gamsuwa lallai kina sona kuma kinyi kewata bayan tafiyata''bakinsa ya sanya a kunnenta cikin kashe murya da iya salon sace zuciya da tada tsohon miki yace ''kimin wani kyakkyawan tanadi yadda zamu bargaje amarcinmu sosai bayan dawowata,idan so samu ne ma mami taga alama,ki mata guzurin jika''wayyo kunya kashe maryam,sai ta maida kanta kafadarsa tana dariya qasa qasa ''zan baka mamaki kuwa,kasha kuruminka''itama ta maida masa cikin nata salon 'ido ya dan zaro yana murmushi ''Allah tawan,kai wlh ke ta musamman ce dear na''dariya suka saki tare a hankali ''kaga malam,idan an fasa tafiyar nan ne ka gaya min,don me zaka shanya mutane kuzo ku bude wa mutane filin soyayya''kunu abdallah ya dan sha ''kaga malam,ya zaka shiga haqqin masoya,miji da mata fa sai Allah,musamman ma ni da maryam kafi kowa sanin cewa mu na musamman ne,don haka ka shafa mana lafiya tsohon gauro kawai''dariya hisham ya fashe da ita ''dududu yaushe Allah ya 'yantaka,naga tare muke fama da gaurancinmu,har gwara ni na fika qarfin zuciya ma.....'' ''ko yanzu Allah ya 'yantani dai na fika''yayi sautin katseshi don kada ya masa tonon silili yana yafito lubabatu dake can gefe tana kallonsu tana murmushi ''amana zan danqa miki,ki kularmin davrayuwata,idan har kika bata kulawa yadda ya dace ni kadai nasan tukuicin da zan miki,zan baki wannan tsohon gauron ki taimaki rayuwarshi''dukkansu sai da abdallahn ya basu dariya,itakam lubabatu hannu tasa ta rufe fuskarta Wani dogon hot kiss ya bata wanda sai da yasa hisham da lubabatu dauke kan don kunya kana ya kama hannunta yana fadin ''ki kula min da kanki,zanyi kewarki fiye da kike tsammni ko hasashe,kana ki cikamin alqawari na idan na dawo''kai take daga masa kafin daga bisani itama ta juya tafin hannunshi ta sumbata,ita da lubabatun na tsaye har motocin suka kammala ficewa daga gidan security ya maida get din ya rufe. . By *mrs muhammad ce*πŸ‘‘ BH πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½ πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’– πŸ’– *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊ πŸ’– Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* β–Ά6⃣6⃣ *An karbo daga abu hurairah,R.A yace: Manzan Allah S A W yace:((MUSULMI DAN UWAN MUSULMI NE,KADA YA HA'INCESHI,KADA YA MASA QARYA,KADA YA TABAR DA SHI,KADA YA WULAQANTASHI,KADA YA ZALUNCESHI,KADA YA TOZARTASHI,KOWANNE MUSULMI A KAN DAN UWANSA HARAMUN NE(YA TABA)MUTUNCINSA,DA DUKIYARSA,DA JININSA,TSORON ALLAH ANAN YAKE,(SAI ANNABIN RAHAMA YAYI NUNI DA QIRJINSA SAU UKU)YA ISHI MUTUM SHARRI YA WULAQANTA DAN UWANSA MUSULMI* _Allah ka tsaremu,Allah ka tsaremu,Allah ka tsaremu πŸ™πŸ½_ _qarin haske_ _ANTY SIS ta janyo hankali na game da wani abu cikin page din baya,wato da yawa makaranta sun dauka ina nufin sixs hours abdallah yayi a first night dinsu,ba haka nake nufi ba,ina nufin after sixs hours ya fahimci barnar da yayi,abinda nake nufi kenan,don bazaiyiwu mutum yayi sixs hours din yana abu daya ba kamar yadda anty sis kika ce,hakan yake,GODIYA NAKE_ Tana zaune saman yagalalliyar daddumarta bayan ta gama karanta fatiharta da suka yi alqawarin karantawa malam na hayi duk salla ita da habiba,shiru tayi tana nazarin rayuwa,wato duk lokacin da Allah ya maka baiwa kaqi gani to idan ya tashi baka zato ba bakayi aune ba zai rabaka da ita rabuwa ta har *abada*,ba duka mutum bane yake wasa da damarsa ba karon farko bayan Allah qwace ya sake dawo masa da ita bankado jibgegen labulen ta,da akayi ne ya sata dagowa da sauri,habiba ce tsaye tana haki tana fadin ''taso zahariyya,taso,ina zaton yau Allah ya karbi addu'armu ne,zoki ga malam''ko nauyin jikinta bata ji haka tayi wuf ta miqe suka fice a sukwane,kai tsaye dakin nan nasa mai azabar kyau da shi kadai ke shiga suka kutsa,kusan dukka mata da yaran na tsaye ne daga waje suna leqensa,gaba daya an sauya masa kammanni ya koma wani abun tsoro,kwananshi dama bakwai baida lafiya a cikin dakin,sai wani fisge fisge yake da surutai marasa kan gado da ma'ana,jini ne kawai ke fita daga bakinsa,duk shimfidar dakin ya tuttujeta saboda azabar da yake dandana,ya kusa aqalla awa guda cikin wannan halin babu wanda yayi yunqurin taimaka masa don gaba daya sun kasa motsawa kamar wadanda aka kafe a gun,abu na qarshe da yayi shine wata gigitacciyar qara da qwala wadda dukka gonakin dake maqotaka da su saida suka amsa kana kuma jikinsa ya saki baki daya bisa dukkan alamu ya wuce gidan gaskiya(haka mala'iku ke tsiga suke fisgar ran fasiqi kafiri wanda ta bijirewa umarnin Allah,haka Allah ya gaya mana cikin qur'aninsa,sabanin mumini mai biyayya wa Allah da manzansa mala'iku kan cire ransa ne cikin nishadi da tausasawa suna zara suna barinsa yana hutawa har su kammala cirewa,Allah ka sanya mu cikin muminan bayinka),mutuwa abace maisa kashe jiki da zuciya hakan ne yasa kowanne cikinsu jikinsa yayi matuqar yin sanyi suka hau kallon kallo sannan suka fara komawa tsakar gida suna shawara ya za'ayi da gawar tunda tuni suka amince cewa ya riga da ya mutu wasu cikin yaransa masu wayon ne wadanda baiwa kafi ba suka haura can hayinsu don nemo jama'a don su kam,basu da maqota daga su sai ginakin dake kusa da su,kimanin awa guda sai gasu sun dawo jiki a sabule don ko kare bai yarda ya biyosu ba balle bil'adam,qarshe ma jama'ar qauyen hayin nasu bigewa sukayi da farinciki kowanne gida suna taya junansu sam barka na mutuwarsa,don ba qaramin tsanarsa sukayi ba,dalili kenan da yasa ya baro cikinsu ya dawo hayin ruwa Kafin cikar awa uku da mutuwarsa saiga gawa ta fara kumbura tana fidda wari mai azabar doyi da wasu irin tsutsotsi,hakan ya sanya kowa ya fara hada karonsa dom gujewa muhallin nasa,tawagarsu guda suka yo qofar gida kowacce

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138