Chapter 24
Chapter 24
rawa kanki yake,bari in tuna miki idan kin manta,ke ba kowa bace cikin rayuwar abdallah face 'yar aiki wadda bata da maraba da baiwa,babu abunda abdallah zaici dake,gargadinki kuma nake ba shawara bace'' ta mata kallon sama da qasa hade da bangazarta ta wuce,da kallo ta bita harda waiwaye,sai da ta bacewa ganinta sannan ta dawo kallon gabanta sam abun vai bata haushi ba sai ma dariya wanda hakan ya sanyata murmusawa hade da kada kai ita daya,idan banda abun zubaida ina zata kai abdallah?,me zata ci da shi,sam ko kadan ma ita dai dai da second bata taba qyasta wani abu wai tsakaninta da shi ba da wannan tunanin ta qarasa sashen,da qyar ta samu ta iya shiga saboda tun daga qofa ta soma ganin bambanci,hamshaqin parlour ne wanda zata iya cewa bata taba tozali da makamancinsa ido da ido ba saidai ko cikin hotuna kusan shima komai na parlour din fari nesai ratsin maroon kadan da baqi kujeru set uku ya lamushe don shi din ma ba baye bane gun girma da kuma tsari,kowacce kujera na rukuninta daban,girmanshi baiyi yawa ba haka nan baiyi kadan ba,bisa can dining area din dake daura da matattakalar bene ta hangosu wanda hakan ke nuna mata sunyi ready ita suke jira a nutse ta qarasa ta soma serving dinsu mami da abdallanta na hirarsu,ta turawa kowa plate din tuwo da miyarshi ta sona kiciniyar bude flask din patatoes balls din ''meye haka?,wani sabon salon raini ne haka,ta yaya zaki raba mana plate ko yau kija fara sanin tare muke cin abinci?'' abdallah ya fada cikin hade gira yana typing saqo a wayarshi ta saki flask din da niyyar hade masu abincin a plate guda mami tace ''rabu da shi fitananne kawai,kalna mai sauqi kace hada mana sai ka ja wani dogon magana?'' ''wallahi mami ke ke shagwaba yarinyar nan da yawa,shi yasa kullum sai ta yima mutane shirme'' ''Allah ko,ita ce ma kai''inji mamin da daidai ta soma jera patatoes balls din cikin plate,saidai duk wanda ta dago ssi taga ya rabe biyu,tayi tsammanin tauri yayi da yawa yssa yake haka,don haka a hankali ta lallabashi ta gama jerawa cikin plate din ta tura musu,tana shirin sauka qasa mami tace ta zauna ta saka hannu suci tare,ce mata tayi taci nata ta qoshi ''kunyanki yayi yawa maryam,har yau kin kssa daukan kanki a matsayin diyata ko?,shikenan tunda ba zaki ci da mu ba zauna muyi hira tare idan na kammala mu wuce'' tilas ta koma ta ja kujera daya ta zauna kanta na sunkuye a qasa,lokaci lokaci mami na jefata cikin hirar don ta sake cikinsu saidai kaifin idanun abdallah ya hanata,duk tunda ta zauna din qurar da ta kwasota ma bai duba ba duka ya tattara hankalinshi kan maminshi da plate din abincinsu abdalla ne ya soma tsame hannunshi yana fadin ''mami turomin daya plate din''ta tura masan tana ci gaba da cin tuwonta don ita duka wadannan yame yamen basu dameta ba hannunshi ya saka ua dauki guda daya,lokaci guda wata matsananciyar faduwar gaba da sameta,rashin yarda da patatoes balls din ya kamata cikin tazarar lokacin da bai wuce second biyar ba kai balls din bakinsa yayi daidai da saukar hannun maryama kan nashi hannun ta buge da qarfi har yaji zafi,ba 6ata lokaci balls din ya fadi saman teburin cin abincin ya wargaje,wani ruwa yellow din ruwa ya soma fita daga tsakiyanshi wanda idan ba sani kayi ba zaka yi tsammani ruwan curry ne,wannan shi ya taimaka daga abdallah har mami basu kula da shi ba zuciyarta taci gaba da tsananin bugu,tsoro qarara ya bayyana cikin fuskarta,tana tuna giftawar data gani dazu cikin kitchen da ta rasa ta waye?,sa'an nan ta dawo da tunaninta kan dalilin daukota don kula da abincin abdallah,guba ne fa?guba abdallah yaci sau biyu a baya,kada fa ayi amfani da damarta a aikata wani mummunan abu,a zafafe abdallah ya kalleta,ranshi yayi tsananin bacin da har ya gaza tambayarta sai mami ce tace ''a'ah,ya haka maryamu?'' ''barta mami,ai dama daga ganin wannan yarinyar bata da kunya,in banda tsabar rashin mutunci ya mutum yana.....'' dakatar da shi tayi tana kallon maryam wadda ke qoqarin daidaita natsuwarta don lalubo dalilin da zata bada wanda har ya kai ta aikata abunda ta aikata din yanzun ba shiri ta tsinci bakinta na fadin ''mam...mi na manta ne ba gishiri da magi cikin balls din,da muka tafi asibiti ashe ban zuba ba,kada kuma yaci yaji babu dadi a bakinsa'' ''amma banda abun maryamu ai sai kice mishi kawai kada yaci,next time ba haka ake gyara ba kin fahimta?'' da sauri take gyada kai tana cewa''eh mami,kayi haquri'' ta fada tana kallin abdallah,fararen idanunshi da ya zuba mata yana kallonta shi ya kuma sakata rudewa har ta rasa me zata aiwatar,ba shiri ta shiga tattara fasashen balls din dake gabanshi tana niyyar kwashewa taji ya riqe tsintsiyar hannunta a razane ta dago idanunta suka shiga cikin nashi,ta danyi kusa da shi hakan ya sanya yaji kaifin idanun nata har qwaqwalwarshi ''daina kallona da idanu sai kace na mage''maganar ta subuce masa ya maye gurbinta a dan tsawace da fadin ''qarya kike,wannan bai kai dalili ba,na gano wani abu daban cikin ranki,akwai dalili amma ba wannan ba'' tuni qwalla suka cika mata idanu,cikin son kare kanta tace ''da gaske nake,ba qarya nayi ba ka yadda yaya abdallah'' ''akan me zan yarda dake,bayan ire irenki biyu sun so ganin qarshen numfashi na a baya,kema kin biyo sahu ne?''ya fada yana huci tuni qwallan da ta tara a idanunta suka cika suka zama hawaye,ba b'ata lokaci suka soma gangarowa kuncinta,kuja ta qwace mata,tsoro da rauni suka mamayeta ''me kakayi haka ne abdallah,sakar mata hannu''mami ta fada cikun fushi ''mami yarinyar nan ban yarda da ita ba,baki ga reaction dinta bane?,aikina kenan mami nasan reaction din masu laifi'' ''ina ce nan ba a office din SS muke ba,ai kin naka baka gwadashi a baya ba sai akan maryam,comon bani son sakarci sakar mata hannu tun kafin in sabar maka''dolenshi ya saketa amma duk da haka bai barta ba binta yake da ido ''oya maryam,tattara kayan nan ki tafi kije ki kwanta gani nan tahowa''jikknta na rawa ta dinga hada kwanukan,tausayinta fal zuciyar mami tana ganin abdallah ne ya tsoratata ''abdallah,ka saurareni da kyau,ba da ka zan dauko maka maryam a matsayin cook ba,nayi bincike mai kyau game da ita,nasan halayenta gaba da baya,baya ga haka nasha yin istihara game da zamanta da mu jikina na bani alkhairi ce ita,saboda haka ina mai tabbatar maka maryam ba zata taba iya cutar da wani dan adam ba balle mu,ni maminka nake gaya maka wanna maganar ba wata ba ka fahimceni?''a ladabce ya amsa mata ''kada ka sake mata irin haka,gaba daya ka tsoratata,ka kiyaye gaba,'' ''insha Allahu bazan sake ba''tafiya taso yi amma ya kasa ya tsare ya hanata,sai da ya sata dariya kana ya mata rakiya har bedroom dinta sannan ya dawo bangarenshi maryam kuwa jiki na rawa ta isa dakin baccinta bayan ta tabbatar ta yiwa patatoes balls din mugun boyon da babu mai ganinshi sai ita,sam bata qaunar tashin hankaki a rayuwarta,kuka ta zauna tanayi riris a bakin gadonta,lijaci mai tsawo ta dauka a haka kafin ta gane cewa kuka babu abunda zai amfanar da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138