Chapter 26
Chapter 26
ta maida idonta kan nasir,cikin rawar murya tace ''ko zan iya ganinka kai daya?'' ''why not?,sadam dan bamu guri'' office din ya rage daga ita sai shi,a hanakli ta zayyana masa dukkan abunda ta sani,ya jima yana jinjina kai kafin yace ''maryam akwai hadari mai girma tattare da gidan,saidai abu guda da ban goyi bayanki ba barin gidan da kike shirin yi,barinki gidan ayanzu dai dai yake da mutuwar abdallah da maharfiyarshi,bayan kin gano matsalar da su basu san da ita ba,shawarar da zan baki shine kawai ki zama mai matuqar kula da takatsantsan,abu na gaba shine ki riqe addu'a,qarfinta da kaifinta ya sha gaban duk wani kaidi da zalunci'' sun shafe fiye da mintuna talatin yana bata shawarwari wadanda syka sa taji hankalinta ya kwanta,nutsuwarta ta dan dawo,da kanshi suka zagaya can bayan asibitin sukayi haqa ya binne ledar patatoes din ''yanzun kuma sai ina?''ya tambayeta bayan sun isa bakin get din asibitin ''gida na nufa inje inga mama'' ''gashi wani aikin yanzu zan koma ciki na qarasa kinga ai da na kaiki'' ''ba damuwa,zan hau adaidaita sahu yanzun zaka ga naje'' a gabanshi ta hau napep din ya biya mata ta wuce bayan ta masa godiya,murmushi kawai yayi ''kada ki damu,ke da raliya duka abu daya ne'' har qofan layinsu dan adaidaitan ya direta saboda babu damar shiga layin nasu,ba dob matsi ba sai don yawan kwatoci da suke da su budaddu wadanda ke wa ababan hawa cikas gurin wucewa,sannu a ankali take takwa har ta isa qofar gidansu Ba laifi akwai ahige da ficen al'umma wanda baka rasa gidan da shi sakamakon yawan 'ya'ya da sana'a da auke da shi,musamman a irin wanna lokaci da ake shirin tada sallar azahar masu neman abincin rana nata hada hadar siya,wanda ayanzun huwaila ce kadai keyi don inna hadiza na ganin yanzun ta girmewa haka da ''zan wuce zan wuce''ta samu shiga cikin gidan saboda yawan mazan dake soron suna dakon a miqo musu abincinsu,can tsakiyar yara ta hango lubabatu da daurin qirji tana zuzzuba abincin a kwano tana mita,alamu dake nuna cewa inna huwaila bata nan kenan ita aka bari da aikin abincin,qofar dakin inna hadiza kuwa labule ne asake qarar music na fita,kada kanta tayi cikin zuciyarta tana fadin''fidan mu,gidan mu kenan,ya Allah ka daidaita shi kamar kowanne gida''ta cire takalmanta tashige dakin mamanta daidai lokacin da maman ta fito daga dakin da suka maida kitchen dauke da farar roba da ta zuba shinkafa danya aciki,da alama girki take wato yau baban nasu yayi tsiyar kenan kowa kansa yau zai ciyar murmushi ya subucewa maman kamar yadda ya bayyana fuskar maryamu,wani farinciki dukkansu suke ji wato da da uwa ba wasa ba,ta isa gaban maman tana niyyar amsar robar hannunta yayin da mamar ke cewa ''maraba,yau kece atafe,a'ah barmin kayana yanu zan kammala ai,daga ahigowarki ko hutawa baki yi ba''dole ta qyale maman ta fita waje ta wanko shinkafar ta ta zuba sanna ta dawo ta zauna hira sosai suke da mamar nata har ta kammala shinkafa da wake da an quli hade da salad tumatir albasa da cocumber,zasu tada sallar kenan hindatu ta shigo,murna kamar ta cinye maryam,cewa tayi itama ba zata zauna ba bari ta fara sallar,ta yada takardun jarrabawarta saman kujera ta fita ta yo alwala Dari biyar maryam ta fitar ta bawa hindatu da kanta taje ta aiyo musu serdine soyayye suka zauna hankali kwance suna cin abincinsu suna hira,hindatu sai santin maryam take ''wallahi adda maryam kada kiso kiga yadda kika koma,kin zama wata hajiya skin dinki tayi wani freah,qiba ce kawai baki qara ba,kinga kiwa da kin dada qiba tsawon nan naki raguwa ziyi'' dariya ma ta basu mama tace ''to sarkin zance,kiyi a hankali dai kada ki qware''cikin nishadi auka kammala hindatu ta guara gurin ta dawo suka sake bude sabon babin hira,da daidai da daidai take jin matsalolinsu,sai taji dadi jin cewa basu da wata matsala mai yawa,mama tana cikin lemonta sosai don haka sai dan abunda ba'a rasa ba,wanda shina mafi yawa kan karatun hindatu ne duka albaahinta ta fidso ta damqawa maman tana fadin ta fadi abunda ya dace ayi da su ''um um maryamu,ke din mai hankali ce,na tabbata ko bance komai ba zaki yi duka bunda ya dace din'' tana lissafawa mama abunda takeso tayi din maman na sa mata albarka,ciki harda aiyqn kayan abinci ta ajjiye agidan nasu tunda albaagin nata ya tasamma dubu dari ''hmmm um''hindatu ta fadactana turo baki,maryam ta juya ta dubeta ''ya akayi bakin ki da magana kenan'' ''wlh akwai,haka kawai zaki narka albashinki ki siyi abincin gida wanda har wadancan mutanen za'aci,jamila ma da suke qaryar arziqi bata taba siyan gallon din mai ta ajjiye tace kowa yayi amfani da shi ba sai ke da kike nema da guminki,a jikinta kawai zaki ga samunta ita babarta da 'yan dakinsu'' _kumin afuwa kuyo maleji da wannan,a bini bashi_ *mrs muhammad ce 👑* 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 [9/17, 12:52 PM] 80k: *ABADAN*22 *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* murmushi maryam tayi ''akwai bambanci tsakanin jamila da maryama,mama ce mu ta haifemu uwa ta gari,mai nuna mana hanyoyin alkhairai da samun dacewa duniya da lahira,yayin da su kuma inna hadiza ce ta haifesu,kowanne mutum da kika gani yana kyauta ne da abunda yake hannunshi yake kuma da shi na alkahairinsa ko sharri,ma'ana duk abunda mutum yayi miki na sharri to abunda ke hannunsa kenan sharrin,ke kuma kada kice za kiyi amfani da abunda yake hannunki na sharri ki maida masa da martani,nuna masa ke alkhairi ne da ke,kada ki damu da sai wani yayi abu zakiyi,idan kina da dama kiyi din,kuma ki qudurce cewa kinyi ne saboda Allah,to sai kiga koda wanda kika yiwa din bai gani ba baki da haufi don kinyi ne domin Allah kuma ahike bada lada da sakamako'' cikin hikima maruam ta ragewa hindatu haushin da take ji na abunda tayi shirin yi a gidan nasu,har ta rakata super market din dake bayan layinsu ta siyi cartoon na macaroni taliya da couse couse,galoon na manja da man quli,dan madaidaicin buhun shinkafa,ta siyawa mamanta kayan tea complete,har da su cornflakes saboda hindatun ledar da mami ta bata ta atamfofine guda biyar ciki da sabulai masu tsada sinqi biyu mamanta bawa guda biyu hindatu daya ta ware biyu zata bawa huwaila da hadiza,yara suka samu suka dauko musu kayan hindati na biye da su yayin da maryam tayi gaba sallamarta atsakar gidan tayi arba da baban nata,cikin fara'a ta nufeshi tana shirin tsugunawa tace ''baba,barka da warhaka''yayin da shi kuma ya tareta cikin hade fuska ba kuma tare da amsa gaisuwar ta ba yana fadin fadi ''lafiya ,ya akayi me kika zo yi?'' ''ya salam,taya za'a raba mjtum da gidan mahaifinshi koda kuwa aure yayi ballantana ita da bata yi aurenba?''take zantawa ita da zuciyarta ''zuwa nayi na gaidaku baba,kusan wata guda ban ganku ba'' ''amma dai maryamu ina cewa.....''maganar tasa ta katse lokacin da yara suka soma ahigo da kayan suna ajjiyewa ''yaya,kai,wannan kuma daga ina?'' ''siyayyar adda maryam ce''hindatu ta bashi amsa lokacin da take sallamar yaran da naira goma goma ladan dako ''uwarta ta siyowa kenan?''baban ya fada yana duban kayan ''a'ah baba,na dukka gida ne,ga wannan baba a sa mana albarka''ta ce tana ciro naira dubu biyar ta miqa masa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138