Skip to content

Chapter 100

Chapter 100

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,273 words 0 views Progress saved
Download Book

ta tsinci bakinta yana furta ''ahamdulillahil lazi bini'imatihi ta timmus saalihaat kana ta limshe idonta tana sake gaskgatawa da miqa dukkan imaninta ga Allah,shine mai kun fa ya kun,yadda duk yakeso haka yakeyi haka kuma za'ayin'' Tana kallonshi yana tura wutar iccen tuni hayaqi ya bulbuleshi sai gashi ya fito da sauri daga rumfar idanu jajur hawaye na diga,dariya taso kamata,dama idan banda rigimar sa ina shi ina wutar icce,wataqila ma tunda gake bai taba zuwa gaban murhu ba balle ayi batun girki,yana goge qwallan yana fadin ''kai kai kai,yanzu baby haka kike shaqar wannan abun kamar kanka zai juye,gaskiya daga yau kin gama''dauke kanta tayi kamar bata jishi ba bayan kuma ta gefab ido take satar kallonshi Baikai ga zama ba nero tayi sallama ta shigo gidan,turus tayi ta tsaya tana kallon abdallah,gani take kamar ba shi ba,sam ta kasa dauke idonta daga kanshi ''wannan kallon fa?''yace da ita sai ta sunne kai wai ita kunya,qarasowa tayi tana fadin ''yaushe ka warka abdullahi?'' ''kinga ga girki can inna ta bari jeki qarasa tukunna kya zo muyi hirar'' miqewa tayi ta isa nufi cikin rumfar tana sake mamakin warkewar tasa har ta gaza boyewa tana zaune a rumfar girkin tana waiwayensa hakanan maryam taji wani abu ya takoreta,ta dade tana qaryata kanta akan irin abunda takeji idan mairo ta rabi kanta da sunan kishi ne saidai a yanzu a yadda abun yaqi barinta ta tabbatar cewa kishin ne baifi saura awa daya a kira magariba ba inna wuro ta dawo gaggauce don bata kaiwa magariba a unguwa itama dai da mamakin take kallona abdallah dake tsaye kan maryam ya harde hannayensa a qirji yana kallonta kamar wanda aka baiwa gadinta ''bawan Allah?,Allah mai iko,kaine a tsaye da qafafunka?'' kyakkyawan murmushin nan nasa ya saki kana ya qarasa ga innar yana karban daurin buhu dake hannunta ya sa mata shi daga gefe ''ni ne inna wuro'' tana kame da bakinta tace ''bari malam yazo yaga ikon Allah,Allah gwanin iyawa ya amshi addu'ar bayinsa,kai Allah mun gode maka,sannu bawan Allah,Allah ya qara lafiya'' ''ameen ameen inna'' ta dubi maryam dake zaune ''ita kuma wannan fa,meron ta barwa girkin kuma?'' Ya juya ya dubi maryam da ta dan hade rai don tasan yanzun innar zata sako wani abu kuma daban,ita kam gani take sam bata sonta yanzun tafi son abdallah da mero kawai dariya ta tasowa abdallah,bai iya hadiyeta ba sai da ya dan dara ''inna targade tayi,Allah ma ya soni ya rufan asiri saura kadan tayi iyo cikin rijiya'' cikin tsoro innar ta zaro ido ''rjiya?,garin yaya ni 'yasu mairamu?''sai ta sake yin fuskar shanu ita ala dole sai ta nuna haushi take ji,sai abdallah ne ya bata amsa ''ina tsammani santsin lakar can ne,ba shiri inna na qarasawarkewa naje na tarota'' ''to Allah ya rufa asiri''ta fada tana dan masa magana da ido,shi ma ya maida nata amsa ta hanyar langabe kansa da daga hannunshi alamun ban haquri mairo ko dake bakin wuta cikin zuciyarta take cewa ''shi kuma baya tashi warkewa sai ranar da wani abun zai sameta,haka ma fa bakinsa yayi'' (hmmm,abdallah na maryam) 🍂🍃🍂🍃🍂🍃 Washegari da hisham suka wayi gari cikin garin ni'ima cikin kuma gidan inna wuro,dukkansu tare suka zauna karin safe,kowanne ka dubi fuskarsa zuwa zuciyarsa cike take da farinciki mara misali,hira suke a tsakaninsu har suka kammala,maryam ta kwashe kayan ta gyara gurin tsoho alhaji yace ''to alhmdlh abdullahi,kaga dai yadda ubangiji ya karbi addu'armu cikin lokaci qanqani'' kanshi a qasa yace ''hakane,malam naga darasi cikin rayuwa sosai,naga abunda da can bansan da shi na sai da Allah ya jarrabaceni da lalura,rayuwa abar tsoro ce haka duniya ma abar tsoro ce,darasi ne babba na koya cikin lalurar da Allah ya jarabceni da ita'' ''gaskiya ne,dama wani abun baka saninsa ko gane shi sai ka shiga wata jarabtar,Allah ka bamu ikon cinye jarrabawarsa'' dukkaninsu suka amsa da ameen tsoho alhaji ya dubeshi ''yanzu sai shirye shiryen tafiya gida kenan'' murmushi ya saki kana yace ''banjin barin garin nan da wurwuri haka,garinku ya yimin malam sosai,yaci sunanshi ni'ima,bazan taba mance wa da garin nan cikin tarihin rayuwata har abada,baya ga haka neman aure nake malam cikin garin naku'' dum kunnenta taji gaba daya yayi tamkar ba zata iya ci gaba da sauraren komai ba,sai ta rasa gane a wanne bigire take a zaune?,duk wata laka ta jikinta ta daina aiki,so take ta tashi ta bar dakin amma haka ya gagara ''a cikin karkaran nan tamu kuwa?''tsoho alhaji ua fada cikin mamaki,cike da tabbatarwa ya gyada kansa ''eh malam'' *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽 [5:05pm, 10/4/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 💖🌺💖🌺 💖🌺💖 🌺💖 💖 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺💖🌺💖🌺💖 🌺💖🌺💖 🌺💖🌺 💖🌺 💖 © *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *_home of expert and perfect writers_* ▶5⃣5⃣ *Daga abdullahi dan mas'ud Allah ya yarda da shi yace:Manzan Allah S A W yace ''duk wanda yayi nuni(fara aikatawa) akan wani aiki na alkhairi yana da kwatankwacin ladan wanda ya ya kwaikwayeshi(ba tare da an tauyewa kowa cikinsu daga ladansa ba''(haka yake ga wanda ya qirqiri wani aiki na sharri kuma wani koyi da shi shima yana da zunubi kan duk mutum daya daya aikata irin aikin kwatankwacin zunubin wanda ya aikata aikin)* *An karbo daga abu ayyubal ansari Allah ya yarda da shi yace:naji Manzan Allah S A W yana cewa''duk wanda ya raba tsakanin uwa da danta,Allah sai ya raba tsakaninsa da masoyansa ranar qiyama'',a wata ruwayar ta abi musa yazo da lafazin ''Allah ya la'anci wanda ya raba tsakanin uba da dansa,da dan uwa da dan uwansa''* tuni ta miqe sabida kunnuwanta ba zasu juri jin abinda zai fada ba,saidai kafin ta kai ga ficewar har tsoho alhaji ya sake tambayarsa ''wacce yarinya ce abdullahi ka gani din,yar wajen wace?'' ''ba wata bace ba malam,ta gida ce,mar........'' cike da gaggawa ra qarasa ficewa daga dakin don tuni zuciyarta ta riga ta bata sunan wadda zai kira din,dakin inna wuro ta wuce ta haye can quryar gadonta gami da cusa kanta tsakanin filalluka ''me abdallah yake so na masa ne da zai fahimceni,wacce hanya zan biyo masa da zai fahimce ni?ta yaya abdallah zai nemi auren wata?watan ma mero?eh tasan bazai wuce ita din ba don duka take takensa ya gama nuna mata haka''tambayar data ringa nanatawa kanta kenan tana nan kwancen kimanin minti talatin da wani abu ta jiyo maganarsu,muryar inna wuro ta fara jin ''Allah ya tabbatar da alkhairi a tsakaninku,ni dama tuwo na maina ne,da kai da itan duka daya ne a guna'' wani irin abu taji ya tsirga mata da bata taba jin makamamcinsa ba,babu shakka kishi bala'i ne,bata sake gasgata kanta cewa tana kishin abdallah mai tsananin zafi ba kamar ranar,take ta yankewa kanta daga yau bata sake kwana a garin tunda ta gama iya abunda zata yi din,cikin qanqanin lokaci zazzabi mai zafi ya rufeta Duk yadda inna wuro ta so fa fito ta qiya,gani take duka basu sonta,har,hisham wani irin haushinsa take ji,ko kowa zai goyawa abdallah baya ai bai kamata shima yabi yarima yasha kida ba,kwanciyarta tayi kan gadon tana jin yadda jikinta ke fudda hucin zazzabi ta kuma qi yarda ta gayawa kowa,sallar magariba da isha ne kawai ya tasheta daga gadon shima din sai taga innan ta

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138