Skip to content

Chapter 135

Chapter 135

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,268 words 0 views Progress saved
Download Book

ne dama idan mukaji da matsala mu miki magana wata uku da ya wuce,to maryam ce tace tana jin abu kamar dutse a mararta''sguru mamin tayi tana nazari,babu shakka zatonta ya fara zama gaskiya,ta dade tana yiwa maryam din kallon mai cikin,jin shiru babu wanda yayi maganar daga ita har shi ua sanya itama ta tsuke bakinta ta bisu da addu'a kai tsaye dakin data ware cikin gidan ta sata ta shiga,ba tare da bata lokaci ba ta fara taba cikinta,kasa gasgata kanta tayi sai data saka na'urar scanning,hoton dan tayin jariri radam ya bayyana kan fuskar na'ura,tsura ido sukayi shida maryam din suna kallon talabijin din,tsantsar farinciki da murnar mami kasa boyuwa tayi har sai da murmushi ya qwace mata ''tabbas,gabunta da wautar dan fari bata barinsa,hakanan tabarar auta ma bata taba barinsa,Allah ya ahiryeku maryam da abdallah,ciki wata hudu amma daga ke harshi babu wanda ya fahimci hakan,wadan nan kam da aqauye kuke cewa zanyi ba mamaki,yarinya ta kusan cinye buhun kwaki amma bai isheku ku gane komai ba?''wani uban tsalle abdallah ya daka sai gashi gaban mamin saura kadan ya kada ita qarfin ba daya ba,ta dafe gadon da maryam ke kai tana fadin ''abdallah yi a hankaki mana'' ''mami zan zama daddy fa kika ce,wayyo Allah na kana sina Allah''ya fada yana daga hannayenshi sama ''janye mijinki maryam kada ya targada min kafada tun kafin jikan yazo na rasa hannun daukarsa''mamin ta fada cikin tsokana,kunya ta kama maryam don ta sadda kanta qasa,tabbas cikin abinda yasa ta kasa gane cikin ko mutanen da take tare da su baya ga na fari ne tsahonta ya shanye cikin sai ya qara mata qiba kadan ta murje fatarta tayi kyau,har wani lokacin abdallah idan yana son tsokanarta zakaji yana ce mata ''diyana 'yar lukuta ta bawan Allah''sosai mamin ta zauna tana musu bayanin yadda zasu kula da cikin don ta fuskanci daga abdallan har maryam din jirgi daya ne ya kwasosu _kuyi maneji da wannan_ *mrs muhammad ce*πŸ‘‘ πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½ πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’– πŸ’– *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊ πŸ’– Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* πŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”šπŸ”š β–Ά6⃣9⃣ *Daga mu'az dan anas R.A yace:Manzan Allah S A W yace:((duk wanda yaci abinci sannan yace:ALHAMDU LILLAHIL LAZI AD'AMANI HAAZA WARAZAQA NIHI MIN GAIRI HAULIN MINNI WALA QUWWAH,an gafarta masa abinda ya gabata na daga zunubinsa* *Manzan Allah S A W yace:((babu abinda yake maida qaddara sai addu'a* *LITTAFIN NAN GABA DAYA SADAUKARWA NE GA DUK WATA BUDURWA DA AURE YA MATA JINKIRI ,DA KUMA DUKKAN WANI MUTUM DAYA TSINCI KANSA KO YA TABA TSINTAR KAN NASA A HALIN SIHIRI,MU SANI CEWA SHI HAQURI WANI ABUNE DA FARKONSA MADA CINE AMMA QARAHENSA ZUMA NE,BABU WANDA YA TABA YIN HAQURI INGANTACCEN HAQURI DAGA QARSHE YA TASHI BABU RIBA,BABU SHI,SAIDAI BA HAQIQANIN HAQURIN KAYI BA* _BAYAN SHEKARA GOMA SHA HUDU_ Abdallah ne a gaba riqe da hannun matashin yaron dan kimanin shekara goma sha hudu suna magana qasa qasa,shi da yaron dukkansu sanye suke da doguwar riga yar asalin saudiyya,kansu lullube da hirahi da kewayayyen abun nam mai siffar zero,a bayansu kuma mami ce riqe da hannun wasu kyawawan 'yammata guda biyu wadanda ba zasu wuce shekara biyar biyar ba,kallo daya zaka yiwa yaran ka bawa kanka amsa da cewa 'yan biyu ne suna tafe suna tsalle tsalle irin na yara,maryam na a gefansu riqe da wani yaron wanda shima irin shigarsu abdallah ce ajikinsa,dukkanau su kuma baqar doguwar riga ce ajikinsu kansu lullube da wadataccen mayafinta Kana kallonsu ko ba'a fada maka ba kasan cike suke da farinciki,haka yake domin shekaran jiya aka fidda sakamakon gasar karatun qur'ani da akayi ta qasa baki daya wadda aka gabatar a qasar saudiyya,ABDUL_AHAD ABDALLAH ABDULKAREEM da ga MARYAM da ABDALLAH shi ya samu zuwa ta daya,abun ya girgiza qasashe da,dama ya kuma bada mamaki,yaro mai qarancin shekaru kamar wanan ya samu irin wanan baiwar ta haddace qur'ani kana ya zubar da duk sauran abokan takararsa da suka fishi shekaru ya daga tutar ta daya Wannan abu ba qaramin daukaka ya sake ja musu ba,kai ba abdul_ahad kadai ba,hatta da maryam ta samu qarin soyayya da qauna daga bangaren mami harma da abdallahnta,kyaututtuka kuwa babu kalar wadda abdul_ahad bai samu ba,ko a yanzun ma sun fito ne somin amsa gayyatar da sarkin saudiyya ya musu don cin abincin dare tare da su ********** Basu suka dawo,ba sai misalin qarfe goma na dare agogon saudiyya,a gajiye suka isa masaukinsu abdallah na sabe da yan biyu da sukayi bacci,abdul_ahad wanda shine babba kuma na riqe da hannun ABDUS SAMAD wanda keta faman gyangyadi,sai da suka isa qofan dakin mami abdul ahad suka ahige shida abdus samad kasancewar dukkansu tare da kakar tasu suke kwana,maryam ta bi bayanau abdallah shima ya bita,kan gado ya sauke yan biyun a hankali,husaina ce ta fara farkawa wadda suke kira da AMATULLAH,tuni ta riqe abdallah da suke kira da ABBU,sarai ya gane me take nufi,so take tace a gunsu zata kwana kamar jiya bayan yau ya riga da yaci burin cin amarci da mamansu ''ya akayi rigimammiya''ya tambaya ''abbu ni a gunka fa zan kwana'' ''a'ah ki kwanta anan,baki gani AMATUL JABBAR anan zata kwana?''maqale kafada tayi ''nidai a gunka zan kwana abbu don Allah''duk yadda yaso lallabata ta qiya,maryam na jinau tana sauyawa abdus samad kaya zuwa na barci,dariyarta take a ciki don yasan amatullah ta gama karya masa budget a yau kam,tana lura tun rana da irin kallon da yake jifanta,har tex ya mata ya kama musu hotel tazo suje sharp sharp yanzun zasu dawo amma ta qiya,don duka wunin ranar suna tare da yaran har ma da mamin,anata ude gifts da abdul ahad ya samu ''ummi ki yiwa diyarki magana,tafa matsanta min''ya fada qasa qasa yadda abdul_ahad dake sanya socks a qafarshi yana shirin nacci da mami dake cikin toilet tana dauro alwala duka ba zasu jishi ba baki ta tabe cikin tsokana tace ''meye nawa?,itaku,ina cewa dazu ka siya mata ice cream ka hanamu kace mamarka ce?'' kai ya dan sosa don kada ta gansu a rana su masu dariya ya sunkuya yana daukarta bisa kafadarsa yace ''haka ne fa,mama na tafi ta kowa ai''ya juya ya fita maryam na qyalqyala musu dariya,ganin yaaran na kallonta saboda dariya da suka ha tanayi da basu san dalilinta ba yasa ta daidaita natsuwarta,ta kammala shirya abdus samad ya haura gadon da abdul ahad ke kai,ta dubi abdul ahad ''idan ka kammala addu'anka ka karanta masa shima kafin ya sake komawa baccin'' ''to ummi'' gadon mami ta koma ta sake gyara mata gami da shimfida mata abun sallah don ta riga ta saba bata kwanciya sai tayi sallah raka'a biyu,har ta koyawa maryam din ma,saida mamin ta fito sannan ta shiga itama ta daura alwalar tana bisa abun sallan mami na zaune gefan gadon tana laranta azkar da bata samu damar yi ba,wayarta na hannun abdul ahad yana danne danne,bata fiye damuwa don ya dauki wayarta ba don ta san hakin yaron indai kaga wayar a hannunshi wani abu mai mihimmanci da zai qareshi yake dubawa,Allah ya zubawa yaron tsantsar basira,hankali da nutsuwa,uwa uba ya samu ingantacciyar tarbiyya ta buga misali,ba qaramar tsaiwa maryam tayi kan tarbiyyan 'ya'yanta

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138