Skip to content

Chapter 129

Chapter 129

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,284 words 0 views Progress saved
Download Book

kula da tattali lubabatu ke ce mata ''babu wani dan gyara ne haka adda da zakiyi?''batasan sanda ta harareta ba don sarai ta fuskanci me take nufi ''halan wannan karon so kuke abdallah ya kaini kushewa ba asibiti ba''ta fada a zuciyarta,a fili kuwa cewa tayi ''uhhmmm,baku fa da kunya sosai yaran yanzun''dariya lubabtu tayi tana toshe bakinta tare da cewa ''Allah ya bawa adda haquri'' Lubabatun ke mata zancan girki dane dame za'ayi?,sam ba wanda ta yadda ta bawa girkin don tace da kanta zatayi,sabida wannan ne karo na farko da zata yiwa mijinta girki cikin gidan aurensu,abinci ta tsara zata masa kala uku baya ga kala kalar farfesu shima uku,sai drinks don haka tun sha biyun ta fara ragewa don kada lokaci ya qure mata zuwa la'asar ta kammala komai sai miya da bata qarasa ba guda biyu su din ma suna kan wuta saura kadan su kammala dahuwa,tana falo tana dan hutawa saiga baaba uwani dauke da yar jakarta,cikin mamaki maryam ta dubeta ''a'ah,baaba ne zakiyi da jaka da ranar nan?'' ''gida mana meramu,zan koma gidan hajiya,tunda yau abdullahi zai dawo ko'' ''haba baaba,ai kwa bari sai gobe tunda baku san zai dawo din na sai dazu da safe fa''bakinta ta kama ''rufamin asiri meramu,haba don rashin hankali sai in zqune muku gotai gotai,hajiya ma ta riga da ta aiko direba,ya iso ma yana waje yana jira na''tana mita ta miqe ta haura sama ta daukowa baban atamfa mai kyau turmi daya,sinqin sabulu da turare sai plate din takalmi guda daya,godiya sosai baaban ta dinga mata har ta sata jin kunya,hijabinta ta zura saboda umarnin abdallah na sanya hijabi ta rakata har bakin get suna yiwa juna godiya Tana dawowa ciki saiga lubabatu itamq da nata kayan,hararata tayi tace ''wallahi baki isa ba,kada ma kice min tafiya zakiyi,ku barni ni kadai bayan sai magariba zasu shigo''dariya hindatu tayi ''wallahi ya hisham ne yace da naji zaku dawo na bar muku gidanku,idan kuma na zauna duk abinda nq gani nina jawowa kaina,kai take gyadawa ''shi hisham din ya gaya miki haka?,to babu inda zaki kuma zai shigo tamu ni da shi''haka ta tare hindatun ta hanata tafiya qarfe shida ta fito daga wanka ana ta shiye shiryen kiran sallah magariba,duk bayan mintina sai ta duba wayarta ko zata ga kira ko saqon abdallah amma shiru,a haka ya qarasa gaban madubi ta tsara kwalliya mai cike da tsari bayan ta mulke jikinta da nau'in turaruka kala daban daban,gaban sif dinta taje ta bude cike da tnanin wacce shiga zata yi ma,ta jima tana nazari kafin daga bisani ta fidda wata gown mai bala'in kyau,ashe ce wadda aka mata ado da jajayen dutsina daga gin breast din da kuma furanni,ta gyara gashinta tayi masa kanta daurin V shafe da jan dankwali,fashion ta saka na jajayen sutsina take ta fito gaba daya kamar wadda aka sauya Babban hijabi ta saka zata tada salla kenan taji knocking ta tambayi waye lubabatu ce tace ta jirata sallah zatayi tana fitowa,tana idarwa ta sake duba lokaci gari har ya dan fara duhu,ta cire hijabin ta sake gyara daurin nata kana ta fito falon,burner ta kunna dake lunguna na gidan duka ta sake sa turaren wuta daidai lokacin da lubabaatu ke fitowa da shirin ta na tafiya,mutuwar tsaye lubabatun tayi ''adda maryam!,kinganki kuwa,shan kyau irin wanann daukar magana haka?''dariya lubabatu ta bata ta dinga darawa,da qyar ta tsata suka fara sallama,ta tambaueta ta me takeso ta bata ''kome kika bani adda maryam yayi,ni ko zaman ma da nayi gidan nan ai ya isheni,ac din da nasha ta kwana goma bakiga har na canza ba,ga kuma babban kamu nayi ya hisham...'' ''munafukai,ai dama daga yadda naga kuna wani kallin juna elh ma san da walakin kuma bari yazo sai na tsigaleshi''da sauri lubabatu ta rufe mata baki ''don Allah kada ki masa maganar,bai furta da bakinsa ba,yace kawai dai zamiyi maganar idan ya dawi zaizo gidanmu''hannunta ta cire daga bakinta ''ni kinga kada ki goge min janbakin tun kan wanda aka sa donshi ya gani''ta fada tana dariya kana ta shiga ta dauko mata itama atamfa saidai ita ta hada mata da kayan kwalliya ''inason in bada doguwar riga ki kaiwa binta amma ina tsoron halinsu,ni ko ganinsu a gida ma banayi anya ma kuwa suna nan'' dariya lubabtu ta sheqe da ita ''wallahi sunana,ai yanzu ko nawa za'a basu su miki rashin arziqi ba zasuyi ba,bakisan ya abdallah ne yasa aka debe su aka rufe ba suka kwana aka tsoratasu kan rashin mutuncin da suke miki keda mama?da suka dawo wallahi ko qofar dakin maman ma daina bi sukayi bare su kallshi,kuma da amincewata yasa akayi hakan,dama iskancinsu ya ishemu,yanzu kuwa idan kinji suna rashin mutunci a gidan uwarsu data koya musu suke saukewa''ta qarashe maganar tana cin dariya abinta mamaki ne ya kamamaryam,a gaida abdallah,shikam halinshi ne idan dai zaiyi abun alkhairi ba wanda yakr gayawa saidai idaniyarka ta gane maka ko a baka labari,qimarsa ta sake daduwa cikin idonta,babu shakka duk wanda zaiga qimar mahaifanka ya tsare maka mutuncinsu ya girmamasu ya gama maka komai koda kuwa yankan naman juna kuke kai da shi,har harabar gidan ta rakata itama bayan ta sa driver ya dauketa zuwa gida tsuru ta dawo tayi cikin falon tana ta duba lokaci,qarar wayarta taja hankalinta,dagawa tayi da sauri ganin sunan abdallah ne ''hello baby,kimin afuwa bazan samu danar dawowar yau ba,wani muhimmin abu ya tsaidamu,amma din Allah kada ranki ya baci,ki leqo yanzu compound na aiko wani yaro zai kawo miki saqo,idan bai iso ba ki jirashi a nan don bana so ya shigo min gida''kafin tace komai ya katse wayar,galala tayi da waya a hannunta ta rasa nayi ma,jikinta ba qwari ta zari hijabinta data tuna yace ta fito yayo aike har tsakiyan gidan ta fito bataga kowa ba don haka ta tsaya nan wajen minti goma tana jira taga ko zai iso,ganin tsaiwar tayi yawa yasa ta yanke shawara komawa falo ta zauna bakin window ta jirashi a nan tunda tana iya ganin harabar gidan daga nan,jikinta ba qwari haka zuciyarta babu dadi tana rungume da hannayenta a qirji kanta a qasa har ta iso qofar falon Cak taji anyi sama da ita baki dayanta,a tsorace ta soma laluben fuskar mutumin saidai tun kafin takai ga tozali dashi turatensa ya gaya mata *ABDULLAHINKI NE*,falon ya shige da ita wanda suna shigar wasu qwayaye masu launin ja da fari suka kama a take rubutun *AM BACK I LOVE YOU* ya bayyana,murmushi ya subuce mata bayan da suka hada ido,shima mayar mata da martani yayi kana suka zube kan kujera ya hau aika mata da saqonnin kewarta da yayi,da qyar ta lallabashi yayi wanka yayi sallar isha'i,kadan yaci abincin don baki daya hankalinsa na kanta,tana cikin gyaran gun da suka ci abincin taji baki daya an sungumeta bai sauketa ko ina ba sai bedroom dinshi wanda ayau suka fara amfani da shi Rikice mata yayi kamar wancan karon sai hakan ya tsoratata,shima kuma ahankali sai ya dinga qoqarin daidaita nutsuwarshi ganin ta fara tsorata,cikin salo da qwarewa na namijin da yasan abinda yakeyi ya dinga tafi da ita,tamkar wani corse yayi a tafiyan tashi,saidai ba wani corse tsabar iya soyayya ne da tattalin mace,wata duniya ya jefasu wadda

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138