Skip to content

Chapter 71

Chapter 71

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,254 words 0 views Progress saved
Download Book

azo gamawa da kai yunwa da qiahirwa sun zama ajalinka''ta wuce sashenta tqna wani irin taku cike da nishadi da jiyo qamshin nasara *mrs muhammad ce*πŸ‘‘ πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½ πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’– πŸ’– *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊ πŸ’– Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* β–Ά4⃣4⃣ *_An karbo daga abu hurairah R A yace:Manzan Allah S A W yace:babu wata rana da gari zai waye face sai mala'iku biyu sun sauko,sai daya daga cikinsu biyun yace ''YA UBANGIJI KA BAWA WANDA YAKE CIYAR DA DUKIYAR SA NINKIN ABINDA YAKE DA SHI'',dayan kuma sai yace''YA UBANGIJI KA BAWA WANDA YAKE QIN CIYAR DA DUKIYARSA ASARA A CIKIN DUKIYAR (WANDA YAKE ROWA BAYA CIYAR DA ITA GA MABUQATA DA MASU NEMAN TAIMAKO)_* πŸ•‹πŸ•‹πŸ•‹ *ina taya daukacin al'ummar musulmi murnar shigowar sabuwar shekarar musulunci,dukkan wani alkhairi na duniya da lahira dake cikin shekarar ka hadamu da shi,ka kare mu da dukkan wani musulmi da sharrin dake cikinta,ka bamu lafiya da zama lafiya da kwanciyar hankali da yalwar arziqi ameen* Daf da zata qarasa bangaren nasu tana ci gaba da babaka dariyarta suka ci karo da baaba uwani,wata uwar tsawa ta daka mata ''ina zaki je uwar kinibibi?'' jikin baaba uwani na rawa tace ''ah....ummm...zani mi gaisa da hajiya ne?'' tsatstsareta nene tayi da idanu ''me nace dake tsohuwar banza?'' ''ahh...kince....kince ne kada ki sake ganina bangaren ku indai ba inaso ma rasa aiki na ba'' gyara tsaiwarta tayi ''kin shirya rasa aikin naki kenan?'' girgiza kai ta shiga yi ''a'ah,don Allah hajiya nene kiyimin afuwa'' ''kinsan me nakeao dake?,matuqar bakison rasa aikinki cikin gidan nan kada na sake ganin qafarki a harabar gidan nan,daga yau ziwa gobe jibi ke har gata ma,kina jina ko?'' da sauri take gyada kanta ,kana ta bata umarnin ta koma inda ta fito hawaye ne kawai ke zuba daga idon nene tana sharewa,idan banda darajar mami da take tausayawa babu abinda zai zaunar da ita a gidan,abubuwa marasa dadi da idanunta ke gane mata wanda ke faruwa shine ummul aba'isin zamanta cikin gidan badon wani abu ba πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚ babu wanda ya sake cewa komai har suka qarasa gidan hisham din,gida ne madaidai ci mai kyau wanda ke dauke da makeken falo kitchen dining area sai dakunan bacci guda hudu A falo suka tadda abdallah kan kujera,gwiwarta a sanyaye ta qarasa gurinshi kanshi na duqe a qasa,a gabanshi ta durqusa ta sanya hannunta cikin nashi tana kallonshi,sam yaqi daga idanunahi ya kalleta,hakan na nuna mata cikin tsananin bacin rai yake,ta leqa fuskanahi idanunahi biyu don tana iya ganin qiftawar idanunshi,sai zuciyarta ta karya ta tura kanta tsakanin cinyoyinsa da fuskarsa sai a sannan suka hada idanu,ya zuba matq idanun naahi da suke har yanzu kalar ja shigowar hisham falon ya sata miqewa,ya taimaka suka shiga da abdallah daya cikin dakunan dake falon,dakine mayalwaci mai hade da toilet,gado madubi side bed sai cupboard da kujera doguwa qwaya daya da carfet da ya malale qasan dakin da shi a maimakon tiles ''zan fita amma bazan jima ba zan dawo'' ya qarasa gaban abdallah yace ''abokin sai na dawo mintina kadan zan dawo''kai kawai ya gyada masa ya miqa masa hannunshi sukayi musabaha πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„ Qarfe goma na daren ranar suka fito daga maboyar da nene tayi musu cikin dakunan barcinta,gaba dayansu baqaqen kaya ne ajikinsu hatta da mask din da suka sanya,kowannensu wuqa ce boye a jikinsa taku daya biyu nene tayi ta tsaya a gabansu,dukkansu sun fita tsawo nesa ba kusa ba,ta dubesu daya bayan daya ''banason a samu kuskure ko sabani cikin aikin nan,shekaru na kwashe masu yawa ina neman wannan damar,saboda haka ku tabbatar komai ya tafi yadda ake so'' dqya daga cikinsu wanda da alama shine oga ya buda hanci ya shaqi iska ''haj,sanin kanki ne munsan aikin mu dalilin da yasa kema kika neme mu kenan'' gyada kai tayi ''haka ne kam'' da daya da daya suka dinga fita har suka isa sashen abdallah,jijjiga qofan suka yi suka jita gam hakan ne ya tabbatar musu a kulle take,don haka kansu tsaye ba tare da wani tsoro ko shayi ba tunda sun san cewa babu security ko daya cikin gidan bare su jisu duka nenen ta bawa kowa aikin da har su gama abinda zasuyin ba zasu riskesu ba,take suka hau lallauya qofan da wani shegen qarfe suka ajjiyeta saahe guda kana suka kutsa ciki Sau uku yama luma wuqa kan tarin filallukan dake tare a kan gadon ganin qamas babu alamun jini ya sanya su yaye bargon,a mamakance suka kalli juna kana daya daga cikinsu ya ciro waya ya kira nene,da zumudinta ta daga kiran ga tsammaninta sun cika aikinsu cikin mamaki da fushi take fadin ''wanne irin babu kowa?kada ku gauamin maganar banza mana,yaron da ko motai bai iyayi ina zaije?,kuma tun jiya babu kowa a tare da shi balle ace ya fidda shi?'' cikin ciccijewa ya maida mata amsa ''kinga hajiya duk ke kika san wannan,kizo kawai idonki ya gane miki'' da azama tq fito ita da zahariyya da danan suka bazamo bangaren abdallan,surutai take tayi kamar wadda ta samu matsala a qwaqwalwarta don bata taba sawa cikin lissafinta cewa wannan karon akwai cikas din da zasu samu ba cirko cirko sukayi cikin dakin bayan kammala duba ko ina na cikin gidan ciki har uwar dakin mami wadda batasan me ake nema ba,ta dai ga nenwn kai tsaye ta ahige mata daki tana dube dube daga bisani ta fito ''taya ya abdallah ya fita daga cikin gidan nan'' ''ke za'a tambaya hajiya''cewar ogansu yana maida locker da tasa ya balle ta dakin abdallan wadda basuyi katarin samun komai ba sai rafar din dubu hamsin ''miqo min wadan nan kudaden,yanzu hatta da takardun kadarorinsa ma ace babu su cikin dakin nan,anya wani baisan abinda muka shirya ba kuwa cikin gidan nan,anya banu mai,mana labe da leqen asiri?''ta fada tana zare ido kamar wata zautacciya kudin ya kalla kana ya dubeta ''ban fajimci me kike fada ba,wannna kidi ai namu ne ladan zaunar damy da kika yi nuka kwana cikin gidanki,ai lissafi zamuyi kawai ki cika mana sauran miliyan dayan da mukayi da ke zaki cika mana'' ''idan aiki yayi kyau ba,ana ta kai wa yake ta kaya,kwananku kuma cikin gida na ai ku kuka qaru da ni bani na qaru da ku ba asara ce ma ta hauni goma da goma,tunda har 'yata na baka ta tayaka kwana ko?baya ga haka ma ni a yanzu bani da miliyan daya bani da dalilinta,da aiki yayi kyau ne ma na tabbata cikin dukiyar da zamu samu ba komai bane cire miliyan daya daga ciki ''ta fada tana matsowa gabansa tare da zazzare idanuwa,don ji take su suka ma ja mata duk wata asara da ta fada matan Dariya ya sheqe da ita ''haba hajiya,kinci qarya kin kwana da yunwa,muba qananan makasa bane ba irinnu akewa haka ba''ya sake matsowa inda take har tana jin warin wiwinshi na dukan hancinta,yatsunshi ya daga guda uku ''kwana uku kacal na baki ki turo mana ragowar kudinmu,wlh wlh wlh ko ke kikayo naqudata matuqar baki turo da sauran kudin nan ba ke da 'ya'yanki ki tabbatar kuna cikin masifa,domin duk ranar dana waiwayeku sai kun buraci mutuwarku akan rayuwarku,na

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138