Skip to content

Chapter 104

Chapter 104

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,274 words 0 views Progress saved
Download Book

mata fuskarta dauke da murmushi,sai da suka bata mintina suna hira a gun kafin ta wuce ko da ta koma dining din tuni su mami sun kusa kammalawa,daman ita tuni taji ta qoshi zuwan hindatu kawai yasa ta qoshi,don haka jujjuya abincin kawai take ''har yanzu banga abun kirkin da kika ci ba maryam'' ''na qoshi mami''ta fada tana mirmushi ''ko a ni'ima ma haka takeyi mami,batason abinci''inji abdallah cikin salon jan fada Ya dan ja kujerarsa baya alamun ya qoshi yana hamdala abayyane ''mami,tun jiya fa aka soma turo min saqon komawa gurin aiki,don watanni da muka diba sun cika,so jiya bamu jima da dawowa ba saiga tex dinsu,zamu zauna da mr presdent gobe a abuja insha Allahu'' shiru mami tayi na dan lokaci kana tace ''anya Abdallah ba za'a haqura da aikin nan ba kuwa?'' murmushi yayi kadan bayan yayi miqa ''ba komai mami,ai duka aikin taimakon al'umma ne,idan lokacin barin yayi za'a barshi,yanzun aikin da na fara nakeso na idar da shi,alhj hamza mai qusa ina da zargi mai qarfi akansa'' ''Allah ya taimaka,yanzun yaushe zaka tafi'' ''da la'asar in sha Allahu,jirgin yamma ne'' ''Allah ya kaimu'' satar kallon maryamun yake yaga ya yanayinta yake saidai sam taqi yarda su hada ido *mrs muhammad*πŸ‘‘ πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½ [7:06pm, 10/6/2017] HugumaπŸ‘‘: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’– πŸ’– *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊ πŸ’– Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* β–Ά5⃣7⃣ *Daga sahal dan sa'ad Allah ya yarda da shi yace''wani mutum yazo wajen manzan Allah S A W,sai yace,ya manzan Allah,nuna min wani aiki wanda idan na aikatashi Allah zai soni mutane zasu soni?,sai manzan Allah S A W yace: KA GUJI DUNIYA(dadin dake cikinta da qyale qyalenta) Allah zai soka,sannan KA GUJI ABUN HANNUN MUTANE MUTANE ZASU SOKA* *_ruwayar ibnu maaja_* Sam taqi dubansa,hidimad gyara gurin da suka kammala cin abinci kawai takeyi,ya san tana sanen rayi haka ''idan kinsan wata baki san wata ba yammata,duk abunki sai na dan more kan na tafi''ya fada cikin zuciyarsa yana danne danne waya,kansa ya dago kamar wanda ya tuna da wani abu da gaske ya dubeta ''af,maryam,taimakamin ki dauko mim wasu takaddu cikin cupboard please''kamar ba zata je ba haka taji saboda kunyar idon mami amma sai taga mamin ma ta sauko daga kan dining din ta koma cikin falo tayo zamanta kan kujeru,ba tare da tace komai ba ta miqe ta nufi inda ya aikata din. Ta kusa aqalla minto goma tana dube dube cikin dakin nasa amma sam bata ga abinda yake fada din ba,dole ta juyo ta fito don ta sanar masa,a kusa da maminta tadda shi yana zaune yana nuna mata abu a waya,ta dan rusuna kadan''ban gansu ba''tace da shi,ba tare da ya dago ya dubeta ba yace ''ki sake dubawa dai da kyau,suna nan ciki ko locker din mirrow dina''a yanzu kam jikinta ya fara bata aiken bogi ne,don iya dubawa tq duba ko ina din,amma sabida bata son musu yasa ta miqe ta koma. Ko minti biyu batayi da komawar ba ya dafe kai yana fadin ''af,na manta asge na sauya musu gu shi yasa ta kasa ganinsu,bari naje na dauka''ya fada yana satar duban mami,bata ko dubeshi ba har ya miqe yayi hanyar dakin,binsa tayi da kallo tana murmushi can qasan ranta tana fadin''dama ai bazan hanaka kebewa da matarka kuyi sallama a abdallah'',tattare itama ya nata ya nata tayi ta haye sama abinta A hankali cikin sanda ya tura qofar dakin ya shiga,tana duqe ta duqufa neman takardu ''har yau maryam ke yarinyace na yarda da hakan ba wuya a miki wayo''ya fada cikin xuciyarsa jingina yayi da qofar ya harde hannayenshi a qirji yana kallonta son ranshi,sai datq gaji da dubawa kana ta dago,ta juyo da niyyar fita amma hankalinta na kan gado tana dubawa ko nan ya ajjiye,dalili kenan da yasa bata ganshi ba har sukayi karo,baya ta ja da sauri,tana yarfe hannunta tace ''na duba ko ina ban gansu ba nikam''. Hannun nata ya kama yana fadin ''ba wasu takardu dama,son ganinki kawai nakeyi dama kafin nawuce,ma tabbata idan ba haka ba bazaki bari na ganki din ba sai a gaban mami'' so take ta qwace amma ya gwada mata qarfi irin na 'yan maza sai da ya kaita gefan gado ya zaunar da ita kana yayi tsalle ya fada gadon,kwanciya yayi ruf da ciki,kanshi ya dora saman cinyarta ya saka hannayenshi ya zagaye qugunta,ya gama kanainaye jikinta bata da ikon motsi ''ummm,baby,har yau bansan matsayina a gunki ba baby kin barni cikin duhu fa?''ta dan hadiye wani abu,yana nufin yace har yau bai fuskanci komai daga gareta na ko so yake sai ya qureta ya sata fadin abunda bata yi niyya ba ''ka riga da ka san matsayinka tuni a gurina ba tun yau ba''shiru ya danyi kana yace''na riga ni kuma da na manta baby,pls ki sake gayamin''. Shiru ta sake yi don ya sakata cikin kokwanto biyu,idan ta buda baki abinda duk zata gaya masa ta tabbatarwa kanta qarya take a yanzu,idan kuma ta fadi gaskiyar wanne kallo zai mata,jin taqi cewa komai ya saka shi juyowa da sauri ya koma rigingine duka akan cinyar tata yana kallin fuskarta,sai tayi saurin runtse idonta,murmushi yayi ya saka yatsanshi ya lakace mata hanci ''yar qauye kawai,shi kenan tunda kin barni cikin duhu,idan kuma na mutu kafin na dawo burinki ya cika kenan ko?'' bata san lokacin da ta bude brown oily eyes dinta ta watsasu cikin nashi ba tana zazzaro su,shima kallon nata ya tsaya yi can qasan zuciyarsa wani sanyi na ratsashi ''mutuwa kum....''sai ta kasa idawa ganin yana sake fadada murmushinsa yana lumshe ido,idanun nata ta sake ja ta rufe ba tare da ta qarasa din ba ''a hakan ake so ace ba'a sona?,bansan lokacin da kika koyi yima kanki da kanki qarya ba''. Bugun zuciyarta ya qara gudu jin yadda ya kama tafin hannunta yana mata tafiyar tsutsa,wani abu take ji yana bin jikinta,da hanzari ta janye hannun ba tare da ta bude idon ba,yana qoqarin sake kamowa tace ''ka bari,ba dadi'' ''da dadi''ya fada cikin wara iriyar murya cikin lokaci qanqani gaba daya yake son burkita mata tunani,hot kises ya dinga aika mata da su wadanda bata taba koda kin labarin irinsu ba,romancing dinta yake sosai kamar ba abdallah,duk da jikinta na amsar saqon amma a tsorace take matuqa hakanan bakinta bai mutu ba da fadar kalmar ''ka bari abdallah,bana so,ka bari don Allah'' ko kadan bai saurareta ba sai da ya ragewa kansa zafi,kallonta yayi idanunshi sun juye tamkar bugagge muryarshi ta koma can qasa sosai,a rufe idanunta suke gashin kanta da ribbom din ya dade ta zamewa ya warwatsu har fuskarta,wata kasala yakeji sosai a jikinsa don haka ya koma ha kwanta kamar dazu kanshi bisa cinyarta kwanciyar rigingine yana maida numfashi. A hankali ta dinga bude idonta kamar mai tsoron cin karo da wani abun,ta dube abdallah dake kwance daidai kan cinyarta,idanunsa na a rufe numfashinsa na sauka a hankali,ta rabbatar bacci ne ya daukeshi,so take ta miqe amma ta kasa saboda gaba daya ya sakar mata nauyinsa,sai ta miqa hannunta ta dauki ribbom dinta ta hada gashinta guri guda ta dauki dankwalinta ta mayar,fuskarsa taci gaba da

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138