Skip to content

Chapter 4

Chapter 4

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,279 words 0 views Progress saved
Download Book

sai take jinta a takure,gashi daga raliyan har nasir din shiru kamar an shuka dusa ''madam haka ake kula da baqi?'' tajiyo maganar lokaci guda,ta daga kanta don ganin me maganar,shije zaune opposite dinta,sanye yake da shadda hartin da hula,murmushi ta danyi a taqaice ''ai bani bace matar gidan,ku jirayi fitowarta'' ''ke da ita din ai daya ne,don na tabbata yarda ce tasa suka barki da baqinsu'' sai ta maida idonta kan wayarta don bata da abun ce masa,Allah ya taimaketa masu gidan suka qaraso gaishe gaishe ne suka biyo baya da 'yan hirarrki,saidai duk lokacin da bisa kuskure idonta ya kai sashen da wanda ake ka kira da jabir sai ta tsinci idanunsa na bisa kanta,wanda hakan har ya fara damunta,nasir ya musu jagora zuwa dining domin cin abinci hakan yasa ta cema raliya ''to ai na gama ko,bari na wuce gida'' ''tunda ba da mota kika zo ba ki bari mu kammala sai mu wuce tare ko?'' ta jiyo muryar jabir din na fadi ''kasan kuwa kusa da unguwar take ba''inji nasir ''haka,ne fa,shikenan kin huta hawa keke napep''inji raliya ''amma kinsan baxaiyiwu su kaini gida ba,idan mama ta ganni kuma nace mata su waye?'' ''indai mama kike ji zan kira tq na gaya mata''inji raliyar cikin zuciyarta ta ja tsaki, ''wannan jabir dan shiga hanci ne wlh''babu damar musu tunda duka ido na kanta haka ta koma ta zauna tana jira su kammala,yana bisa dining din amma idanunsa na kanta har raliya ta ankara,cike da gulma ta tabota ''ke,inafa tsammanin kinyi tsuntuwa yau a gidannan'' cikin rashin fahimta tace ''ta me fa?'' hararta tayi ''kiji min 'yar rainin sense,kina nufin baki lura da irin kallon da jabir ke miki ba?'' ''shine me?'' ''wlh sonki yake bisa dukka alamu'' wannan karon ita ta maida nata hararar''kijimin mata,kawai daga kallon sarkin fawa sai miya tayi zaqi?'' ''wlh da gaske nake,jabir mutumin kirki ne diyana,kada kice zaki qishi don Allah'' ''a'ah,kinji ta da wani guntun wa'azinta,ashe har yace miki ma yana sona ko?'' ''ni na gaya miki zai fada miki'' Can saman dining dinma jabirne ke cewa cikin qasa qasa da murya ''kai mutumina nifa nazo gidanka a sa'a,Allah yasa bata da wani'' dariya ya saka''tuni na harbo jirginka ai,indai bilkisu ce a iya sanina ba'a tsaida mata miji ba'' ''ai kuwa bazan tsaya kallon ruwa ba,a yau zan kafa kaina'' A bakin layinsu tasa ya tsaida motar,ta bude murfin tana cewa ''na gode'' ''haba madam da sauri haka?'' sai ta juyo cikin mamaki tana dubansa ''eh mana,ya zaki min illa kuma ki tafi ki barni ba tare da kin bani magani ba'' ci gaba tayi da dubansa,sai ya saisaita nutsuwarsa,baiji ko,nauyi ba ya bayyana mata duka manufarshi,da farko ta ja masa yace shikam yace baisan wannan zancan ba,babu inda,zata tafi ta barshi cikin qila wa qala,idan,ko ta tafi to zai tare ne a qofar gidansu har sai ta amsa masa koda zai shekara maganar da sukayi da raliya ce ta fado ranta ''maryam,wlh indai aure kike so kiyi kada kiqi karbar tayin jabir matuqar yayi miki maganar,jabir bazai taba tararki da maganar banza ba,nasan jabir tuntuni,abokin nasir ne da dewa,halayensu kusan daya,hakan shi ya qara danqon abotarsu'' ita kanta a zahirance bata ga wani aibu ba tattare da jabir din,yana da kyau daidai wanda duk hassada ba zaka kira shi mummuna ba,a iya abinda ta gani da bayanan da raliya ta mata ta fuskanci zata iya amsa tayin jabir,ko don ma ran mahaifiyarta yayi fari,ko don ta samu itama ta zauna a nata dakin kamar sauran qawayenta da 'yan uwanta ganin shirun nata yayi yawa yasa ya sake marairaice mata ga tsammaninsa zata wofantar da buqatarsa ne ''shikenan,Allah ya shige mana gaba'' ''um um maryama,wannan ba amsa bace,kice ina sonka jabir shine magana'' kanta ta girgiza cikin alkunya tace''don Allah ka barni na wuce gida,na tabbata zan sha fada gun mama,don na kai magariba a waje,tunda ka kwaahe min numbers ai sun isa'' fitowa yayi ya zagayo ya bude mata murfin yana cewa''shikenan,kin bani izini na kiraki?'' kai ta gyada masa,kafin ta dauko jakarta yayi sauri ya rigata ya bude zif din ya jefa mata kudi,ta noqe alamun ba zata amsa ba shi kuma yace indai bata karba ba to tana nufin bata sonshi,tilas ta karbi kyautar tasa,sukai sallama amma sai taga ya ja ya tsaya,kallonshi tayi ya daga mata gira ''sai na hango,shigarki gida don tsaron lafiyarki da kuma gane gidan naku koda na tashi zuwa'' murmushi kawai tayi tajuya domin shigewa layin nasu katsam idonta kan isyaku,kai ya gyada sannan ya kwasa da gudu yayi gida,la'ilaha illa nata subhanaka inni kuntu minaz zalimin,tasan tamkar a idanun iyayenshi tayi,cikin fargaba taci gaba da takawa jabir na mata rakiya da idanu har ta shige gidan *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚📓✍🏻✍🏻✍🏻 [9/17, 12:49 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺🌺 💖💖💖💖💖💖💖 🌺💖🌺💖🌺 🌺💖🌺💖 🌺💖🌺 🌺💖 💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 💖💖💖💖💖💖💖 *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺💖🌺💖🌺💖🌺 💖🌺💖🌺💖🌺 💖🌺💖🌺💖 💖🌺💖🌺 🌺💖🌺 🌺💖 🌺 ▶4⃣ sai da tayi dira dira a soron kafin ta gano ainihin hanyar wucewa,saboda cike yake da 'yan zance,can hauwa can binta can maijidda kai abun takaicin ma harda zainabu wadda du du du ba zata wuce shekaru goma sha hudu ba kacal a duniya ta tsakiyarsu ta raba ta wuce,taji dadi sosai da babu wadda ta tanka mata a cikinsu cirko cirko ta samesu a tsaye cikin tsakar gidan,inna hadiza ce da baba huwaila sai babansu dake bakin famfo yana daura alwala da alama haramar sallar isha'i yake yi,sai kuma isyaku dake qame a gefe da alama tuni ya gama fesar da abunda ya qunso ''la ha ila ha illallahu,muhammadu dan abdullahi''suka dauko salatin tare yayin da huwaila ta dire ita daya ta kuma dora ''wlh yaya da gaske ne yaro baya qarya,tayani gani don Allah,suturar jikinta ma ai ba da ita ta fita ba,lallai dandi na dada samun gindin zama a gidannan'' inna hadiza dake ta faman gyada kai tana kallon maryamu wadda ke tube takalmanta a qofar dakinsu ba tare da ta dubedu ba tace''qwarai da aniya,ya gama yawon barikin da ita ya kwashi na kwasa ba dole ta canza sutura ba,yo zata shigo mana gida ne da najasa ne'' ''ke meramu zo nan'' kiran baban nata da baqin qazafin da suka jefeta da shi ya daki zuciyarta lokaci guda,a sanyaye ta dawo gabansa ta durqusa kanta a qasa ''wanne dan iska ne ya dauko ki a mota har gidan ubanki?'' muryarta a sanyaye tace''ba dan iska bane baba,gidan raliya muka hadu yace yana sona'' ''yana sonki?'' huwaila da hadiza suka fadi kusan a tare bai biya ta kansu ba ya dora da nashi bayanin ''alhmdl dama ni na gaji,na gaji wallahi kullum rana a unguwarnan sai anyi da ni kan na ajjiye babbar mace a gida,saboda haka ki shaida masa matuqar da gaske yake to na bashi kwana goma ya fito ayi kowa ma ya huta'' ''yo idan banda abunka malam amadu saurayin qwarai ne zai dinga yayibar yarinya yaro kwararo kwararo kuma yace zai aureta,ai qarya ne dan yaudara ne kawai''inna hadiza ta,cafe maganar ''oho,koma dai meye nidai na gama magana,tashi ki bani guri'' jikinta a sabule ta miqe tayi hanyar dakinsu,har yanzu kunnuwanta badu daina jiyo mata qananun magan ganun da suke yi bq marasa

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138