Skip to content

Chapter 112

Chapter 112

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,279 words 0 views Progress saved
Download Book

maryam din kana suka ajjiyeta a gida sannan suka nufi nasu gidan 🍃🍂🍃🍂🍃🍂 kwana bakwai mami bata bari an dakayar da gyaran da ake mata ba,tamkar ana shirin canza mata fata,ita kanta mai gyara ta yaba yadda gyaran ya karbi jikin maruym di sosai da sosai,baaba uwani kuwa zama take kawai tana kallon maryam din ''gaskiya meramu anya ba canza miki fata hajiyar nan me gyaran jiki take ba?''duk sanda ta fadi hakan dariya take basu ita da mami Kusan tun ranar da sukayi waya da abdalla kan zuwanta gida basu sake samun kiranshi ba,ana gobe kwanaki bakwai din da ya diba zasu cika mami ta nemeshi don taji goben zai dawo,saidai ta nemi layin nasa yafi sau goma bata sameshi ba,har cikin dare tana iransa bata sameshi da safe ma hakan ce ta faru,damuwarta ta kasa boyuwa ta tadda maryam a kitchen tana goge freezer tare da sake jera kayan ciki don mamin ta hanata yin kowanne aiki ''ni kam maryam kina samun abdallah a waya kuwa''maryam din ta waiwayo ta dubi mamin sai ta rasa amsar da zata bata,don ita kanta tasha kasa kunne cikin dare lo da rana taga ko zata samu koda texs nasa,Allah ya taimaketa tin kafin tace wani abu mamin tace ''sam ba'a samun wayanshi,na kira na kira duka akashe'' jikinta taki yayo sanyi gaba daya,gabanta ya dan fara faduwa kada kadan ta juyo gaba daya ga mamin tace ''to mami ni cewa nayi ko chargy ne babu a wayoyin nashi?'' kai ta girgiza ''bana jin haka,saboda ba cikin wani qauye bane cikin tsakiyar abuja ne fa,kusa da villa,kinga ta yaya za'a rasa chargy a wayoyi?'' sbiru ya sake ratsa tsakani,bayyanar damuwa kan fuskar maryam wadda ita kanta batasan ta bayyana bayasa mami riqe hannunta ''kada ki damu in sha Allah he is safe'' kai ta gyada asanyaye,sai ta kasa qarasa ci gaba da aikin ta biyo bayan mami ta fita a kitchen din ta koma dakinta ta kwanta Maganganunshi na qarshe ta dinga tunawa _''Allah ya qaddara saduwarmu,sai Allah ya dawo da ni,kimin addu'a don muhimmin aiki zan gabatar,wanda ko shine aiki na na qarshe da zan aiwatar in sha Allahu sai na gabatar da shi,ki sakani a addu'o'inki,idan kuma na mutu shikenan sai a darus salam''_ Wani irin juyi tayi cikin matsananciyar faduwar gaba ta tashi ta zauna sosai kan katifarta,sai taji kanta ya sara ta dafe goshinta da sauri kana ta maida jikinta fuskar gadon ta jingina kusan wuni tayi sukuku zuciyarta ba dadi,duk motsin da tayi maganansu ya qarzhe a airport ke mata amsa kuwwa a kunnenta,ko falon bata sake fitowa ba saboda rashin kuzari,mami keta leqota don kada ta takure ranta ta sa damuwa,ta karanci wani kalarson abdallan mai qarfi cikin zuciyar maryam din,da taga ta leqo ta sai ta qirqiri murmushin dole,gaba daya walwalarta ta ragu,ta dinga kiran layin abdallah a jejjere kamar wadda aka bata aikin yi amma ko da wasa bata shiga ba is switched off computer keta faman gaya mata, Cikin kwana biyu duk yadda taso hana kanta damuwa zuciyarta tace batasan wannan ba,bata taba jin damuwa irin ta wannan lokacin ba,bata taba jin ta damu da wani abu a rayuwarta ba kamar wannan lokacin cikin kwana na uku ta gaza daurewa fitowarta a wanka kenan wanda tun safe ta kasa yinsa sai kusan daya na rana ta samu tayi,mai kawai ta shafa ta fesa turare ta zira doguwar riga ta nade kanta da mayafinta,takalmanta plate ta jawo ta saka kana ta fito,babu kowa bangaren don mami ta fita asibiti don haka ta fito waiting parlour ta zauna tana kallon shigewa da ake tayi da sabbin furniture bangaren nene a da,bata cikin nutsuwarta batasan wa zai zauna anan ba bata kuma damu data sani din ba,abinda ke cunkushe kadai a ranta ya isheta jarraba number din hisham ta laluba ta kirashi,daga yanayin yadda taji sun gaisa har yana zolayarta ta tsinke da lamarin,sai kawai ta fasa tambayarsa ta kashe kiran,lambar abdallah ta sake trying wanda ta maida kiran tamkar ibada a gareta saidai amsar daya ce kamar kullum is switched off,ita kanta ta fuskanci yanayin damuwa kan fuskar mamin duk da bata kai tata ba,jin zuciyarta take kamar ana hura mata wuta son abdallah kewar abdallah duk su suka mata rubdugu,kalamansa na qarshe a gareta ke sake sanya mata karaya,kawai sai ta zame a gun ta kwanta rub da ciki,batasan ya akayi ba ta tsinci kanta ne kawai tana kuka tuquru,bakinta na fadin ''kada ka yimin haka abdallah,kada ka guje ni,kada ka tafi ka barni''take furtawa a hankali cikin kuka,Allah ya taimaka mutanen dake aikin kafa kayan furniture din sun kammala sun fice Kuka tayi mai yawan gaske har yasa idanunta suka kumbura baya ga zafu da radadin da suke mata amm hakan baisa ta haqura ba,sai da bacci ya lallabo ta taimaketa ya saceta,bacci ne mara dadi wanda tana yinshi tana sayke ajiyar zuciya ma kukan da ta yi Hannu taji kan wuyanta a hankali ta soma bude kumburarrun idanunta wanda hasken daya cika falon yasa ta gaza budeshi gaba daya,mami ta gani tsaye a kanta tana fadin ''bacci kuma a waiting parlour maryamu?''ta tambayeta ba tare data lura da yadda idanunta suka sauya kala ba ''tashi ki koma daki idan baki gama ba kiyi a can amma nan ai yayi waje'' sosai tayi qoqarin tashi amma ta kasa,ga zaton mamin magagin bacci ne don haka ta kama hannunta don tayata tashin,zafin da taji da hucin zazzabi ya sata furta ''subhanallahi,maryam me ya sameki haka?''sai a lokacin ta lura da yadda idonta ya suntume fuskarta tayi jawur ''ya salamu ya Allah,maryam''mamin ta fada a rude,zare wayar hannun maryam din tayi don ta miqar da ita,number din abdallah ta gani kan scrren din wayar,sai ta dubi maryam din ''abdallah dai maryam?duka a kanshi kika yiwa idanunki haka?,sai kace an ce miki ya mutu ne''kalmar mutuwa data ambata wa abdallan sai ta sake karyar mata da zuciya,take taji ko,mutuwar ma yayi ne tunda gashi mami ta fada?,sabbin hawaye suka soma tsiyayowa,sai mamin ta dafe kanta don ta fuskanci abinda ya sakata kukan ''babu abinda ya samu abdallah maryam,tashi maza mu shiga ciki ki je ki watsa ruwa ki karbi magani,zafin zazzabin nan yayi yawa kada ya zama wani abun kuma daban'' mamin ce ta taimaka mata har ta shiga toilet kana ta fita ta bar mata dakin ta haye samanta don tayi wanka,itama ta hada mata magungunan da zata sha da zai saukar mata da zazzabin,zuciyarta fal da fafinciki jinjinawa da yaba tsaftatacciya kuma ingattaciyar qauna kuma mai qarfi da ya samu daga gun matarshi,wanda tayi imanin koda bafa duniya zai samu kyakkaywan kulawa a rayuwarshi Ta kammala watsa ruwan ta canza kaya,da qyar ta iya bada sallar azahar da la'asar da suka shigeta ta dawo ta nade a gado,har yanzu zazzabin tana jinsa cikin qashinta,a haka mami ta taras da ita Sai data tilastata taci abincin da ta shigo da shi sannan ta bata maganin ta sha,tana nan a gurinta har bacci ya sake daukarta sanann ta fita dakin Bata farka ba sai da wani amai mai zafi ya farkar da ita,da gudu ta miqe kanta na sarawa ta shiga bandakin ta dinga kwarashi,mami wadda ta idar da sallar magariba tana jiran isha ta dawo

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138