Skip to content

Chapter 122

Chapter 122

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,308 words 0 views Progress saved
Download Book

zakayi ranar da aziza ta zama taka''har wani sosa kai hisham yayi kana yace ''wlh fa,na barku lafiya to''ya fada ya juya yabi sahun yan uwansa dake zaune cikin mota suna kiransa aballah ya bishi da kallo,yana son hisham mutum ne mai amana wanda samun kamarsa sai an tona,ba duka mutum bane a wannan zamanin zakamasa alkhairi ya saka maka da alkhairi,mafi yawancinsu da sharri suke saka maka sai yan kadan Sai da ya tabbatar sun fice sannan ya isa ya rufe gate din gidan don bai kawo mai gadi ba tukun,bai koma ciki ba sai da ya tabbatar ya rufe ko ina A hankali yake takawa yana nufar cikin gidan,iskar damina na kadashi,wani irin ni'ima ce yau lullube da sararin subhana,iska ake mai dadi da shiga jiki,gefe guda wani tawagar farinciki ne ke shawagi cikin zuciyarsa,jinsa yake cikin wata duniya ta musamman,yau gashi ga maryamunsa,cikar muradinsa cikar burinsa,sashensa ya bude ya ciro kayan bacci farare tas da towel dan qarami kana ya rufe ya dawo sashenta ta cikin parlour din gidan na biyu,a hankali ya,keta har falo na uku wanda daga shi sai wani dogon corridor wanda kana shiga zaka tadda dakunan bacci uku,sai matattakalar bene wadda saman shima ke dauke da dakunan bacci parlour toilets da kitchen,a hankali ya,haura saman kansa tsaye ya tura qofar daya daga cikin dakunan da ya gani a bude wanda hakan ya tabbatar masa a ciki maryam din take ''assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatu''ya shiga da sallama wanda hakan ba qaramin rage mata fargaba yayi ba,gefan kujerar dakin take zaune,kanta na duqe lullube da alkhyabbar jikinta,tsayawa yayi cak kana ya kingina da bangon dakin yana qare mata kallo duk da bai ganin fuskarta,ya kashe a qalla mintina biyar a haka zuciyarta na bugawa a hankali kanta na a qasa,ta tabbatar har yanzu yana cikin dakin saboda qamshin turaransa da ya cakude da nata ya lullube dakin,haka nan ya sake haifarwa da dakin wani irin ni'imtaccen yanayi,sannu a hankali ya dinga takowa gareta bayan ya ajjiye kayan hannunshi duka saman dan qaramin table na glass dake a gaban gadon,ya isa gabanta ya zube duka kan gwiwoyinshi,hannayenta ya kama ya sanya cikin nasa yana qarewa qunshinta kallo,tamkar yasa harshensa ya lashe haka yaji,sai da ya more kallonsa sannan ya dora kansa saman cinyanta yana leqen fuskarta,bai ga fuskar sosai ba sakamakon hular alkyabbar ta sanya ta yin duhu,a hankali ya sanya hannunshi ya janye hular take fuskarta ta bayyana saidai idon nata a rufe dai yake Cikin wata sassanyar murya da bata zaton yana da ita ba taji yace''zan rayu dake zan mutu da ke *ABADAN* dani dake zauna''murmushi ya subuce mata don bata taba jin waqa a bakinsa ba sai a wanan karon,sai taji tafi dadi a bakinsa ma fiye da mawaqin,a hankali ta dago brown oily eyes dinta ta zuba masa,dama abinda yakeson gani kenan,shima murmushin ya sakar mata wanda saura kadan ya narka mata zuciya,ajiyar zuciya ya saki ya lumshe sexy eyes dinshi kadan sannan ya sake budesu''ya Allah ka gafartawa mami na,kayi mata albarka data sauqaqamin hanyar samunki,ta shiga lamarina'' kana ya daga girarsa ''yes....zan rayu da ke har *ABADA* maryam,haka kuma nake fatan koda mutuwa tazo min ta daukemu tare....'' Sake maida kansa yayi yi ya kwanta a cinyarta ''soyayya gaskiya ce baby,haqiqa,babu abinda ya kai so dadi,so shine abu mafi girma dake iya sarrafa zuciya kota wanene,haqiqa so ba ruwanshi da kyau nasaba ko cancanta mulki ko wata dukiya,yakan kama mutum ne kansa tsaye ba tare da qwaqwasa qofa ko neman izini ba,maryam kici gaba da zama tawa ni kadai har *abadan* don Allah''idanunta a runtse suke ya riga da ya gama kashe mata jiki baki daya a hankali ta dora hannunta saman sumarsa ''ni taka ce abdallah,takace ni,ina ji a jikina saboda kai aka halicceni,kaga kuwa har *abada* maryam ta abdallah ce,to ta yaya jiki zai iya rayuwa babu daya barin nasa?,ta yaya zuciya zata iya rayuwa da tsagi guda ba tare da daya tsagin ba?,ka zama ni na zama kai *mutu ka raba*'',qanqameta yayi kamar za'a qwace masa ita yana mata godiya tare da sheqar daddadan qamshinta dake barazanar juya akalar tunaninsa A hankali ya dinga rage mata kayan jikinta tana zaune don ba musua tsakaninsu,a yadda taga mayen sonta cikin idanun abdallah zatayi matuqar qonashi a wanann lokaci idan tayi masa musu,da undeies kadai ya barta kana ya shige bandaki yayi nashi wankan ya fito bayan ya hada mata ruwan,kafin ta fito har ya zura kayan baccinsa ya saka 'yar hularnan tashi ka fiya naci fara ya nutsu saman abun salla,gefe taga nata kayan bacci,sai da ta qare musu kallo tanayi tana satar kallon abdallah dake salla,babu yadda zatayi haka ta juya ta sanyosu,gaba daya bata da maraba da babu dadinta daya akwai babban hijabi dogo a gun shita zura ta koma gefan gadon ta zauna,yayi sallama kana ya mata izini ta taso suyi sallah,raka'a biyu suka gabatar,addu'a mai tsaho suka yi ta neman alkhairai da samun zaman lafiya da haduwar kai a tsakaninsu sannan ya waiwayo ya kama kanta ya karanto addu'ar da annabin rahama ya koyar da mu '' *Allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi,wa a uzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi*'',da salatin annabi ya rufe musu suka shafe tare idanunsa cikin nata wanda a yanzu fargabarta ke dada yawa,girarsa ya daga yana murmushi ''wai duka tsoron nan na meye ne?''cikin nuna dakiya ta noqe kafada ''wanne tsoro?'' ''gashinan ina ganinshi cikin idanunki?,kada kice a'a maryam,ina iya karanta abinda ke zuciyarki kai tsaye ta cikin idanunki,ko kin mance zuciyarmu guda ce?'' murmushi tayi cikin son nuna dakiya da jarumta amma sai ta sake ce masa ''ni tsoron me zanji'' tafa hannunshi yayi sau uku yace ''good girl,naji dadin samunki jaruma,kinsan kuwa irinki,nake so saboda irinkin ne kawai zasu iya jurata,ko da yake....nafa gasgata zancanki,kefa kince yadda kike kallon mace yar uwarki haka kike kallon *abdallah* kinga kenan ya kamata yau mu gane hakan ne ko ba hakan ba,uhmmm....are u ready?'' ta tuna sanda ta gaya mishi hakan cikin jirgi,take sai idanu suka raina fata,qwalla ta tarar mata,tana tsoron kada ya mata mugunta fa,cikin shagwababbiyar murya irinta me sonyin kuka tace ''kaima ba ka tsokane ni bane a lokacin?''dariya ya mata ''wasa nake miki matsoraciya,kwantar da hankalinki,babu abinda abdallah zai miki kinji,bacci zamuyi dukkan mu a gajiye muke,koke baki gaji ba ayi miki?''wata iriyar kunya ta dirar mata sai ta cure guru guda ta cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana dariya qasa qasa,waishi abdallah wanne irin dan kai tsaye ne?''na gaji,na fika ma gajiya''kai yake gyadawa yana sake gano yarinta quruciya da rashin wayonta ''to kin gani,so ki saki jikinki kinji,ni yayanki ne ko?''da sauri ta gyada kai kuma taji nutsuwa ta saukar mata,umartarta yayi ta samo musu plate da cups a kitchen da hijabin jikinta ta miqe har ta soma tafiya ya kirata ta dawo,hannu ya miqa mata kana yace ''ciro min hijabina dama aro na baki ai'' sai ta dan zare ido ''amma fa jikina...'' ya katseta ta hanyar dora yatsanshi kan lips dinshi yace ''shshshsh,i know....haka nakeson ganinki,kin mance ba musu?,idan kika qi kuma to yau....''bata ma barshi ya qarasa ba ta zareshi ta miqa masa ya amsa idonsa akanta a haka ta fice zuwa kitchen din ya

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138