Chapter 89
Chapter 89
ya qara matsawa da shi gaban innar kadan sanann cikin qasa da murya ya fara mata maganar lokacin da taji sallamad meron sai da taji wata faduwar gaba,haka siddan ta kasa zama sai ta miqe ta yaye labulen window din dakin,shi abdallah yake fuskanta don haka ta sake lafewa sosai don kada ya hangota Tare da mustafa suka shigo,tana ido biyu da abadallah ta fara sussunne kai cikin duqunqunan nan hijabinta,inna wuron ce ta dubeta ''au,to kuma meye hakan,wa kike kunya neοΌkinga bani na kiraki ba dama tunda kin gujeni kinga mai kiran naki'' gaban abdallah tazo ta zauna kana ta gaida shi ''bani amsawa tunda bamusan laifin da muka yi miki ba kika gujemu'' qara dunqule kanta tayi guri guda wani dadi ya rikito mata kamar ta tashi tayi rawa ''ni dai babu komai''haka ta fada,abdallahn ne ke janta da hira abunka da gwanar surutu tuni ta saki jikinta suka fada hirarsu,daga bisani maryam taga inna wuro ta tattre kayanta ta shige daki ta barsu qasa qasa suka koma magan ta yadda bzata iya jiyosu ba,sai fuskar mero da ta gani ta fadada ta fara'a tana sake boye kanta,ji tayi ta soma jin juwa juwa sabida haka ta saki labulen ta koma kan sofa tana dafe da qirjinta ''kada ki jawomina bunda bazan iya ba,kada kimin irin wannan rashin adalcin,ki rabu da abdallah bai dace da ni ba,wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa,abdallah ba mate dina bane''abibda ta ringa fada kenan qasa qasa wani hawaye mai zafi na bin kuncinta tun tana duba agogo har ta haqura,sai da ya buga qarfe sha daya daidai har ya dora da mintina sannan ta sake jiyo muryarsu ''ki tabbatar gobe tare zamu fita rafi dake kinyi alqawariοΌ''kai ta gyada kamin tace ''eh nayi alqawari'' shima kan ya jinjina ''to shikenan sai da safe goodnight sweet dream''duk da bata fuskanci mai yace ba sai ta saki dariya tana waiwayensa har ta fice ya janye idonsa yana sauke ajiyar zuciya,har yazu nauyi da zafin da yake ji a qirjinsa yana nan babu ainda ya ragu duk da faman turereniya da yake masa amma sam ya gaza cimma nasara,cike da kasala ya danna madannin tafiya keken ya nufi dakin da shi cikin wani rin yanayi na jin kadaici da zazzafar qauna *mrs muhammad ce*π πππβπ½βπ½βπ½ [8:50pm, 9/30/2017] Hugumaπ: [3:02pm, 9/30/2017] Hugumaπ: ππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊ ππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊ ππΊππΊ ππΊπ πΊπ π *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πΊππΊππΊπ πΊππΊπ πΊππΊ ππΊ π Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*π‘ *_home of expert and perfect writers_* 5β£1β£ *_Allah S W A yana fada cikim alqur'aninsa mai girma''haqiqa ji da gani da zuciya dukkansu abubuwan tambayane (ranar alqiyama)_* *_cikin wata surar kuma yana cewa''ku cika alqawari lallai alqawari abin tambaya ne (ranar qiyama)_* Da sauri sauri mami ke tafiya har ta isa ga sashen nenen,nenen ta taras kwance male male tana zabga ihu saboda tashi data kasa yi,zubaida da danan na durqushe kanta suna qoqarin dagota ta qarasa gabansu tana shirin taba nenen tana tambayarsu ''me ya sameta,lafiyaοΌ''zubaida ta bude baki dom bata amsa,da sauri nene ta sake saka wani ihun tana fadin ''wayyo Allah na,kada ku kulata,kada kuyi mata magana'' itadai zubaida da batasan me hakan yake mufi ba tayi zaton ko qwaqwalwar nenen ce ta samu matsala ''wallahi faduwa tayi ne,bamusan me ya sameta ba''ta bawa mami amsa da haka don batasan me zata ce mata ba idanu adnan ya zq aro don yasan babu shakka a yau dai asirin jikin mami ya gama karyewa don sun qetara sharadinsa ''Allah ya tsine miki dai albarka zubaida,haihuwarki bata qare ki da komai ba,kin sake jawo mana wata asafar,kin karya mana asiri''nenen ta fada hawaye shabe shabe,kallon rashin fahimta mami da zubaida ke mata,tuni adanna ya juya ya fice mami ta bishi da kallo ta dawo da kallonta ga zubaida zata mata magana ifanunta ya sauka kan cikinta sai ta kasa magana ta tsaya kawai ta zuba mata idanu,udon zubaidan ya cika da qwalla don kusan duk gidan babu wanda take ganin mutumci mituncinsa kamar mamin,babu wanda yace komai nenen ta sake sakin ihu ''adnan kaje ka duba min yata zahariyya,kada su hallakamin ita''cikin tashin hankali,mami ta kalli zubaida ''kamata mu kaita sama na mata allurar barci ko zata dawo hayyacinta'' ''wallahi bintu kada ki sake kice zakimin allurar bacci,lafiyatq qalau,jikina ne kawai yayi nauyin kuma zai warke,na tsaneki wallahi bintu taurin ran danki abdullahi duk shi ya jawo mana wann masifar da muke ciki'' kiran sunan abdullahi ya sanya gabanta faduwa har sai data kirq sunan Allah,haka suka kinkimeta da qyar suka iya haurawa da ita saboda azanar nauyinta,mamin ta yi mata allurar barcin,tana ta surutanta da su basu fahimvi komai ba ciki saboda basu san me ta qulla ba da haka bacci yayi awon gaba da ita Ta fito daga sashen nene ta nufi sashenta tana dafe da kanta don tun sanda ta kira sunan abdullahi kanta yake mata ciwo,suna take ta nanatawa cikin zuciyarta ta qarasa bedroom dinta ta shiga tayi wanka ta daura alwala ta bada faralin sallah,har yaznu ciwon kan uaqi saukar mata don haka ta balli magani ta sha ta kwanta,babu jimawa nannauyan bacci ya dauketa Yana zaune kan kekensa yayi kyau cikin jallabiyya fara sol,fuskarshi qunshe da murmushi yana kallonta,itama shi take kallo,a hankali ya fara tahowa gabanshi tana miqa masa hamnu saidai duk sanda ta kusa zuwa dab da shi keken da yake kai sai yayo baya da shi taga ya mata nisa Sai ta fara binsa da gudu keken na sake tafiya da shi saidai yana fuskantarta fuskarsa kuma dauke da murmushi,sai da sukayi tafiya mai nisa kana keken ya tsaya cak,sai taji an,dafa kafadarta da sauri ta waiwayo,maryam ta gani tsaye kusa da ita tana murmushi,ta nude bakinta zata kira sunanta bat taga sun bace mata gaba dayansu,dube dube ta dinga yi amma ta nemesu sama ko qasa ta rasa,wani rami ta gani a gabanta ta tafi a hankali ta keqa sai ta hangosu ciki suna zaune,ji tayi luuu ta tafi itama zata fada ciki firgigit ta farka tana ambton sunan Allah gami da dafe kanta dake sara mata kamar zai tsage gida biyu,tafi minti talatin a haka sannan taji sannu a hankali ciwon kan yana raguwa yana raguwa har ta daina kinsa gaba daya,sai ta jita sawai kamar wadda aka kunce daga sarqa ''abdallah,maryam''ta fada a hankali Kamar wadda aka tsikara ta dago da kanta ta miqe da sauri ta sanya hijabinta ta fito,hanyar sashen abdallahn ta nufa kanta tsaye tana tafiya wasu abubuwan da suka faru suna fado mata tamkar mutumin da yayi mafarki yake tuna abunda ya faru,kallo daya ta yiwa sashen nasa jikinta ya gaya mata ba lafiya ba,qofar na nan a lallauye yadda su muugu suka yi mata ranar da suka zo nemansa,jikinta babu qwari ta shiga ciki ta dinfa duba ko,ina da ina ta,iya qurar da bangaren yayi kawai ya isheta amsar cewa gidan ya dade babu mai rai a cikinsa,hotunan abdallahn ta dinga bi tana kalla bata ankara ba kuka ya subuce mata,zaman dirshan tayi saman carfet hawaye masu dumi suka shiga turereniyar fita daga idanunta ''ina ka shiga abdallah,ina ka tafi ka barni''abinda ta donga fada kenan a hankali cikin kukanta mafarkin da tayi dazun ya dinga dawo mata tar kamar a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138