Chapter 5
Chapter 5
dadi akanta ba,taimakon da Allah yayi mata daya yau baban nasu bai bi ta kansu ba yayi ficewarsa masallaci,wannan wace iriyar masifa ce?,tamkar ita ke da ikon rubutawa kanta qaddararta?,ita ta hana kanra aure ne?,shikenan a rayuwa babu dama Allah ya qaddara maka wani abu sai jahilan cikin mutane su dinga ganin tamkar kai ka jawowa kanka ko da amincewarka hakan ta faru?, mamanta na cikin rumfar a zaune amma tamkar bata a cikin gidan,wannan dabi'arta ce,tana da dauke kai da yakana akan 'ya'yanta,da wuya ka taba mata yaro kaji bakinta,da wannan damar mutanen gidan ke amfani suke cin karansu babu babbaka a kansu,duk da wasu lamuran hindu na masu tambotsai idan taga cin kashin yayi yawa,don ma mama na kwabarta yanzun ma baqinciki ne ya hanata motsi da kuma umarnin maman,don tana zaune ne tana karatun waec da fitilar qwai a gabanta,sallamar ta kawai hindun ta amsa ta dora da cewa ''yanzu fisabilillahi yaya maryam haka zaki ci gaba da zama ana miki cin mutunci ba zaki kare kanki ba?'' ''kinci gidanku nace hindatu,nace kinci gidanku,da baban nata zatayi sa'insa ko da matan ubanta?,ke maryamu,ina kika samo kayan jikinki?'' kai ita kam dai ta shiga uku,wato ko ina cikin tuhuma take ''mama tsarabar da raliya ta bani ce,na tayata aiki tace bazan taho ba sai nayi wanka,shine aciki na cire nasa wannan'' ''madalla,amma daga yau kada ki sake ki sake kaiwa magariba a waje kina jina ko?'' ''to mama'' dakinsu ta shige ta ajjiye jakarta saman katifarta,qoqari take ta shanye dukkan wani bacin rai,batason ta barshi yayi tasiri a ranta,tunda idan da sabo ai yaci ace ta saba,sau nawa ake ruwa qasa tana shanyewa,ta zare rolling din kanta ta dawo tsakar gida ta daura alwala,sai da tayi nafila raka'a biyu ta kaiwa Allah kukanta,ta dade saman carfet tana jan,hasbunallahu wa ni'imal wakeel sannu a hankali taki sauqi na zuwar ma zuciyarta kira ne ya shigo wayarta data duba agogo sai ta tabbatar jabir ne don bata da alaqa da wani da zai kirata a irin wannan lokacin,shi dinne kuwa,awanni kusan biyu sukayi akan wayar har ta soma gajiya don bata saba doguwar hira irin haka waya ba,cikin awanni tayi amanna da kyawawan halayen jabir,bayan ta,jada da wanda raliya ta gaya mata,a yanzun mafita kawai take nema,koda wanda bai kai jabir din ba zata iya aurenshi matuqar zaya riqeta da daraja sunayin sallama hindatu ta shigo dakin da tarin litattafanta ta watsasu tata katifar,kasancewar dakinsu daya don maryamu bata da sha'awar raba daki da 'yar uwar tata,doguwar hamma ta ja,maryam ta dubeta tana dariya ''boko wahala'' ''mtsw,ke dai bari yaya maryam,yanzu a haka kukayi degree?'' ''me kayi da maza inji karya,idan banda abun hindu ke,da sai yanzu ma zaki bar secondry din'' ''gaskiya ne kuma fa''ta fada tana fadawa kan katifar tabayan ta ture liattatafan da ta watsa gefe ''yauwaaa''maryayam ta gada tana janyo jakarta ta ciro kudin da jabir ya bata dazu ''ungo irga kiga nawa ne'' ''an biya ku salary ne ya maryam?''tace lokacin tame lissafa kudin ''a'ah jabir ne ya bani'' ''ya maryam Allah ya tsaida jabir din nan mu sha budiri''murmushi itadai kawai tayi ''ten thousand ne'' ''ok...to ko riqesu,zan cika miki kudin rigistration din exam dinku'' ''na gode ya maryam,na gode'' ''don mind,ni dake duka daya ne,kawai ki tayani addu'a hindu'' ''ai babu fashi wannan ya maryam'' 🎄🎄🎄🎄🎄🎄 cikin sati,guda kacal sabo ya shiga tsakaninsu da jabir,yana da sauqin kai,fara'a da haba haba da jama'a,yan sonta ji da ita da tattalinta,cikar satin ta isar masa da saqon baban,murna da farinciki tamkar zai goya ta,washegari kuwa magabatansa suka iso,a take aka tsaida magana harda sa rana,farincikin mama bazai misaltu ba duk da tana boye wa,yayin da huwaila da hadiza sukejin kamar an musu transfer zuwa jahannama 🎄🎄🎄🎄🎄🎄 shiye shirye tuni suka fara kankama domin sati biyu kacal ya rage,cikin yammacin gab da sallar magariba jabir yazo gurinta kawo mata invitations kasancewar akan hanya yake yasa bai shiga daga cikin gidan ba,suna tsaye jikin motarsa taga kamar an wulgasu,ta dago kanta don ganin me wucewar,maraqisiyya ce har ta gota su taga ta dawo,da baya,qare musu kallo tayi sannan ta gyada kai ta shige cikin gidan fuuu da uban akwatinta dake rinjayarta wani faduwa taji gabanta yayi wanda yasanya har sai da ta rufe idonta,duk lokacin da maraqisiyya tazo gida to babu alkhairi a zuwanta,don bata taba komawa inda ta fito sai ta assasa wani bala'in cikin gidan ''lafiya?''jabir ya tambayeta cikin kulawa murmushi tayi wanda yafi kama da na yaqe ta girgiza kai''babu komai'' *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [9/17, 12:50 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺🌺 💖💖💖💖💖💖💖 🌺💖🌺💖🌺 🌺💖🌺💖 🌺💖🌺 🌺💖 💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 💖💖💖💖💖💖💖 *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺💖🌺💖🌺💖🌺 💖🌺💖🌺💖🌺 💖🌺💖🌺💖 💖🌺💖🌺 🌺💖🌺 🌺💖 🌺 ▶5⃣ Babu sallama sam bisa tsarin maraqisiyya,don kaf gidan tafi kowa lalacewa,jamila ke rufa mata baya,a tsakar gida ta iske uwarta hadiza da 'yar kanzaginta huwaila,basu ga shigowarta ba sai yif kawai sukaji na warbar da akwatinta da tayi da zamanta jabar kusa da su inna hadiza ce ta dafe qirjinta''na shiga uku ni dije,kada dai kice min yauma korokin yayi?'' fuska ta yatsine ''yau ba shi ya kore ni ba ni na taho,don na gaji da zama da matsiyaci direban babbar mota kuma mashayi'' ''oh ni 'yar nan,auwalu matsiya cine'' ''lamba daya''maraqisiyyan ta qarashe mata huwaila tace ''aini na ma kasa magana,yara duka aure ya zama na tafashi kada,babu daya qwaqqwara?'' matsowa maraqisiyya tayi sosai kusa da su ta ma manta da tata matsalar''wai hadiza ni fa ban gane ba(haka suke kiran iyayen kansu tsaye)idanuna kamar wancan mujiyar nake gani da wani jikin wata qatuwar mota,ko gixo take min'' caraf huwaila ta kama''itace mana 'yar nan,kinga babarku babu yadda banyi da ita ba mu tashi tsaye ko malaman da mata ke shiga muma wannan karon mu fada amma tace bata da kudi,dame zata ji,da matsalolinku ko da kisan kudinta da take nema da qyar?kawai mu qyaleta tunda wancan karon hakanan taqi auruwa to wannan karon ma hakance zata faru'' ''hadiza ai ranar biyan buqata rai ba a bakin komai yake ba,ku yanzu ko kunya bakwaji,ai abun kunya ne a tattarw da ku maryama ta auri irin mijin dai da na ganta tare da shi,wlh dukkanin alamu sun nuna mai akwai ne,yaranku suna zaune?,wadanda ma aka aurar din gamu cikin wahala?,kuma ita tahaye?,si wallahi inaaaa,zaman gida bai qarewa maryam ba,ku matso kuji'' shewa sukayi bayan sun tafa kamar wasu,sa'anni wanda yayi daidai da shigowar maryam din ''sannunku,maraqisiyya ya hanya?''babu amsa sai uban tsaki da taja kamar zata cire harshenta 🎄🎄🎄🎄🎄🎄 washegari ta shirya tsaf don zuwa karbo dinkunanta da kuma yin sallama da uwar dakinta wadda take aiki a qarqashin katafaren kamfaninta nayin girke girke da shirya guraren biki,tayi sallama da maman ta,fito tsakar gidan saiji tayi maraqisiyya na dura ashar,cikin takaici ta,juya don ganin da wa take,ita da hindatu ne ta,sirka ruwanta ta wanke kanta rabi zatayi wanka maraqisiyyar ta,sheqar mata ta,tara wsni don shiga nata wankan ''wannan banzar yayar taki ma bata isheni ba bare ke karan kada miya'' hindatu dama dake qullace da su tace ''dalla gafara can malama,banza a banza kawai,wadda ta kasa zsmsn gidan aurenta,yayar tawa kuma da,kike maganarta kuwa wallahi tako ina ta sha gabanki,aure kuwa nasan bazati irin naku ba auren jeka nayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138