Skip to content

Chapter 31

Chapter 31

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,305 words 0 views Progress saved
Download Book

kiyaye don samun zaman lafiyarki da ci gaba da aikinki cikin gidan nan'' kamar jira ake ya kammala maganarshi haske ya mamaye falon,jdanun zubaida suka sauka kansu yayin da nashi idanu suka sauka kan fuskarta da hawaye ya aoma gangarowa,wani abu ne ya riqe mata maqogaro wanda koda an bata damar maida masa martani ba zata iya ba alokacin,saboda baqincikin da ta hadiya ba kadan bane,tsanarsa da tsanar halayensa uka sake linkuwa cikin zuciyarta ''kai din banza,abokan mu'amalar taka ma din banza,baka isa maryama ta soka ba,saboda daraja mutunci da karamci take bida ba tarin dukiya ko kyau ba''abunda take ta son ta amayar masa kenan saidai abundaya tokare tan ya hanata fada cikin zafi baqinciki da kishi zubaida ta iso gabansu ''abdallah''abunda ta iya ambata kenan cikin karyar da kai hawaye ya soma mata zirya,sam bai damu da ganinta agun ba,duba daya ya mata ya maida idobsa kan maruam ya cire hanunshi yana jan tsaki,ya ja mayafinta ya goge hawayen ta da ya soma taba masa hannu ''indai bakiji abunda na gaya miki ba yanzu kika fara kuka''ya kewayeta da,zafinsa ya fice asashen,ita dinma gyalenta ta ja kawai ta shige sashen nasu,abida ce kawaia falo da tayi zaman kallo tana kuma dakon dawowar abdallah don yace ta zauna ta jira shi batasan gatse ya mata ba lokacin baccinshi yayi,dakinta ta wuce ta danna qofar ta rufe kana ta saki kuka,me tayi masa?,ita tace tana son hisham ne ko kuwa,ahikeban talaka ba komai bane agun wasu masu kudin,talaka bai cika mugum ba,ko talaka baisan ciwon kanshi ba,taqamarshi ta isheta,tana jingidansu zata bar masa shi yafi mata sauqi,ga fargabar yanayin gidansu ga taqama da gadararshi da wanne zata ji? *mrs muhammad ce* [9/17, 12:52 PM] 80k: *ABADAN* *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* *_Daga abu hurairah yarda Allah ta qara tabbata a gareshi yace:manzan Allah s.a.w yace:yana daga cikin kyawun musuluncin mutum,ya bar abunda babu ruwansa_* *_a wani hadisin kuma manzan Allah s.a.w yana cewa:jibrilu bai gushe ba yana min wasiyya da maqoci,har sai da nayi tsammanin/zaton maqoci zai iya gadon maqocinshi(saboda girman haqqin dake kan maqoci akan maqocinsa)_* washegari a makare ta tashi saboda rashin baccin kirki,kitchen ta shiga ta shirya musu breakfast,adana kebabi,tavouk koftesi a abincin turkia sairuwan shayi chips da soyayyen qwai,cikin lkkaci qanqani gidan y game da qamshi,bata bar kit hen din ba baba uwani ta shigo ''af,makara kikayi ne yau maryamu''murmushi tayi tace ''wlh kuwa baba uwani'' gaisawa sukayi sannan ta bar mata kitchen din ta koma dakin sha biyu na rana ta fito tayi sarving nasu mami ce da abida,cikin mamaki abida ke cin abincin tana tantamar yinsa akayi ko restaurant aka je aka siyo?,abincin yan turkey a nijeria,kusan ma har yafi nasun dadi sakamakon banancin spices da muke da shi so take ta sanarwa mami qudirinta na barin gidan saidai ta gaza,nauyinta take ji sosai,alkhairan mamin a gurinta na da yawa,da haka har suka kammala cin abincin ba tare da ta ce mata komai ba kafin ta bar gurin mamin le sanar da ita gyaran gida da canza kayayyakin da suke duk shekara idan ya rage saura kwanaki bakwai azumi ''akwai ma'aikatan dake,zuwa,suna aikin nan da jibi zaki gansu,abunda kawai nake so kimin alfarmarshi shine zaku shiga kasuwa kiyo soyayyar kitchen dukkan abunda ya kamata wanda za'a buqaceshi'' ta dan saki murmushi''diuarki ce ni mami kamar yadda kike fadi,ba alfarma bace umarni zaki bani kawai na bi'' ''na gode diyata Allah yayi miki albarka'' wanna halaye na mamin na daya daga cikin abinda ke sata sake jinta cikin zuciyarta koda ta kammala abincin dare,sashen ta sake bari,gurin baba uwani ta kuma wuni,kiran wayarta da mami tayi da daddare shi ya fiddota ziwa,sashen mamin,a hanya suka ci karo da zahariyya na shirin fita cikin motarta,wani kallo ta jefi maryam din da shi wanda ya tilasta maryam neman tsari da ita cikin shirin fita ta samu mamin ''maryam yau kwanan asibiti zanyi bazan dawo ba sai gobe idan Allah ya kaimu,ga gidan nan na barshi hannunki'' ''to mami''ta fada tana amsar jakar hannunta don yima mamin rakiya zuwa motarta daidai lokacin abida ta fito sanye da riga da wando,kunnenta maqale da earpiece ''mami ina zuwa?'' ''af,na mamce kina cikin gidan'' hara rar maryam abida tayi ''mamee kika manta da ni amma wannan ki kasa mantawa,da ita''bata lura da hararar da take ma maryam din ba tayi dariya ''to ai kece din sarkin kwanciya,klum kina kwance a gado kamar ruwa,zan tafi asibiti ne ina kuma tsammanin kwana zanyi'' ''q'nnnn,si kin dawo''ta fadi tana kwanciya saman doguwar kujera yayin da suka fice ita da maryamu mami na shirin shiga motar taga shigowar abdallah gidan,hakan ya sanya ta dakata har ya iso inda suke ta sanar mishi fitarta ta dora da ''am....abdallah,inason in ganka daman'' ''to mami ai gani'' janye jikinta maryam tayi ta koma gefe don basu damar ganawa,daidai duk da hakan tana jiyo abunda mamin ke cewa ''har yanzu banga alamun jituwa tsakaninka da bida ba abdallah me yake faruwa?'' ''mami ba komai kawai dai rawan kanta ne yake bani haushi,azarbabi rashin aji da kamun kai,kuma ma ban samu zama bane kinga soaai,kwana biyin cases sun mana yawa a office,bainciken wadanda suka saci kudin talakawa'' ''duka naji,saidai inaso ka ajjiye dukka wani uzirinka,ka tabbata kun fahimci juna kai da ita,maganar halayenta kuwa kana da damar canza ta tunda tana sonka,ya kamata ace i yanzu ka ajjiye iyali,don nima ina da buqatar ganin qana nan yara suna gilmawa,ina fata ka fahimceni da kyau abdallah?'' ''na fahimta mami,saidai koda jikokin sunzo ta yaya wadan nan patient,naki zasu barki ki sake da family dinki,suna qwace min ke kina kwanan office''ya qarashe maganar cikin sigar zolaya murmushi tayi don ta san dama sai yayi qorafi,haka take fama da shi duk lokacin da zata kwanan asibiti '?idan na biye maka abdallah sai ka makarar da ni''ta dan daga murya kadan ta kira maryama,cikin nutsatstsen takunta ta iso,gidan baya mamin ta shige sannab maryama ta miqa mata jakar tana cewa ''a dawo lafiya mami'' ''Allah yasa maryama,a kula da gida'' ''insha Alahu mami Allah ya bada sa'a'' mamin ta juya ga abdallah dake tsaye yana jinsu,hannayenshi harde saman qirjinshi,har ga Allah yaji dadin yadda ta nuna caring wa mahaifiyarshi ''abdallah sai na dawo,banda tsokane tsokane?''mami ta fada tana dariya ''mami sai kace yaron goye,zaki jawo a raina abdallahnki fa''ya fada yana shigeqa ahima gidan bayan ''a'ah,ya haka?''ta tambayeshi ''zanje na rakaki ne mami'' ''yabzun fa kaima ka dawo daga aiki,na uafe ka shiga ciki ka huta,abida na parlour tana jiranka'' ''idan ina tare da mami mancewa nake da duk wata mace,a naje asibitin naja masu kunne duk wansa ya barki kikayi aiki duka dare baki runtsa ba ni da shi ne,driver muje''haka drivan yaja sauran securitu dinshi suka dafa musu baya maryam ta dawo cikin gida tana jiniina yawan qaunar dake tsakanin mamin da abdallah a inda ta bar abida anan ta taras da ita,bata tanka mata ba,tana gab da shiga dakinta taji tace ''ke zonan,''tayi kamar ba zata kula ta ba don ta tsani irin wannan kiran sai kuma taga baquwar mami ce ko ba komai taci darajarta ''wai me kika dafawa mutane?''kafin ta kai ga bata amsa kuma sai taji tace ''jeki kawai,sai abdallah soulmate ya iso kyazo kiyi serving namu''

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138