Chapter 102
Chapter 102
cancanci abdallah sai ke maryam,'yar halak ce kw gaba da baya,kin riqe amana da alqawarin da kika yimin tun washegarin ranar da aka kawowa abdallah ke,baka taba sanin masoyinka na asali sai wani abu ya sameka maras dadi a rayuwa,maryam ina sonki kamar yadda nake son abdallah,hakanan ina sake baki amanar abdallah,ki kasance a gefansa *ABADAN* duka tsawon rayuwarsa,na tabbatar cewa matuqar kina tare da shi koda bani duniya bazai shiga mawuyacin hali ba,don Allah maryam kici gaba da riqe abdallah kamar yadda kika yi a yanzun'' Gaba daya maryam taji mami ta rikito mata wani qaton nauyi ta dora mata ne,kamar ta daureta ne da jijiyoyin jikinta,girman mamin na da yawa a idanunta,tana daukarta ne kamar mamanta data haifeta,ta rasa mai zata ce da mamin _kuyi haquri da wannan_ *mrs muhammad ce*π πππβπ½βπ½βπ½ ππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊ ππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊ ππΊππΊ ππΊπ πΊπ π *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πΊππΊππΊπ πΊππΊπ πΊππΊ ππΊ π Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*π‘ *_home of expert and perfect writers_* βΆ5β£6β£ *_Daga abdullahi dan umar Allah ya yarda da shi yace:Manzan Allah S A W yace''mutum bazai gushe ba yana tambayar muta ne(roqo) had sai yazo ranar qiyama fuskarsa babu tsoka daya ta nama(qwarangwal)'',ruwayar bukhari da muslim ce_* *FANS NA ABDLLAH DA MARYAM,YA BANI SAQO YACE NA GAYA MUKU BA'A SHIGA TSAKANIN MIJI DA MATA FAππ,TSAKANIN MIJI DA MATA SAI ALLAH,WANDA YA SHIGAVTSAKANIN MIJI DA MATA QARSHE SHI ZAIJI..........π*ππ Itama kama hannun mamin tayi ''insha Allahu mami muna tare,babu abinda zai raba mu da ke tare zamu rayu'' giriza kanta tayi ''ko ba dade ko ba jima dole wataran na tafi na barku maryam,baya ga haka ma duk musulmi na qwarai ana son ya dinga tunawa da mutuwa ko da yaushe,haka annabi muhammad S A W ya horemu yace mu yawaita tuna mai yanke jin dadi'' ''haka ne mami amma don Allah kiyi shiru,kina tare da mu insha Allahu'' mirmushi kawai mamin ta sake yi ππππππ Kayan sawarsu kadai suka diba amma komai sun barwa inna wuro ''bawan Allah ku cire wannan abar taku mai karbar hasken rana ku tafi da ita''daroya ta basu abdallah yace ''a'a inna,ku barta ai kuma zata muku amfani,kudin shekara guda aka sanya mata kinga idan aka cire ai anyi asarar kudin ciki,tunda mu muna da inverter acan''bata fuskanci me yqce ba dai amma ta masa godiya ''mune da godiya inna,karamcin da kika mana bazai fadu ba'' Kudi mamin ta ajjiyewa tsoho alhajin amma qeme me yaqi karba,yace shi abdallah jika ko da ya daukeshi,ba don a biya shi ya masa aiki ba,ko a hanya ya ganshi yana da buqata irin wannan shi mai taimaka masa ne mamin tace itama ba biyansa tayi ba Allah ne kadai zai iya biyansa amma sam tsoho alhaji yaqi karba bisa dole ta haqura,itama inna wuron qin amsa tayi,sai dabara mami tayi ta cusa mata qasan tabarmarta yadda bazata gani ba har sai sun tafi Dukkaninsu suka rakosu har bakin mota cike da kewa,maryam kam harda qwallanta don tasan zatayi kewar qauyan ba kadan ba ''ka shiga motar hisham kai da hisham din idan yaso ma taho a tawa ni da maryam'' cikin shagwaba irin wadda ya sabawa mamin yace ''gaskiya mami qafata qafarki,a zamu raba mota ba''qememe yaqi yarda kuma ya kasa ya tsare maryam ba zata shiga kowacce mota ba Dole hisham ya shige motarsa shi daya,maryam da abdallah na gaban motar mamin ita kuma mami na baya,gaba daya ta hade gabas da yamma na fuskarta don mami ce tace dole ita zata shiga gaban,shi kam dadi ya kamashi ya dinga satar kallonta yana son ta kalleshi ya tsokaneta,kamar kuwa tasan da hakan taqi uarda ta dubeshin Yana shirin tashin motar mero ta leqo daga soron gidansu da alamu tana labe ne tun dazun a nan,idanh shabe shabe da hawaye,sai abdallahn ya kashe motar ya bude murfin ya fice yana fadin ''ina zuwa'' maryam na kallonshi ya qarasa inda meron take,sai ta rufe fuskarta da mayafi ta hau kuka sosai,tana iya hango yadda bakinsa ke motsi da alamu wani abun yake gaya mata,daga qarshe dariya ta saka,yasa hannunshi cikinaljihu ya fiddo da dubu biyar cikin kudin da jiua hisham ya rakashi cikin gaya ya ciro a ATM machine Sai sata shige gidansu sunan ya juyo ya dawo cikin motar,yana shirin daura belt mami da hankalinta ke kan wayarta tace ''ita kuma waccan yarinyar fa waceοΌ'' murmushi yq dan saki kana yace yana kunna motar ''zan miki bayani idan mukaje gida'' bata amsa masa ba ya tashi motar bayan yayi addu'a ta matafiyi ya soma tafiya La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu kinaz zalimin ta dinga maimaitawa cikin zuciyarta sakamkon wani irin daci da take ji,yana tuqin shima yana satar kallonta,so yake ta kalleshin kuma taqi kallonsa,ya juya ya dubi seat din baya mami ta kashingide abinta tana gyangyadi,ai dole kam sam tunda tazo garin bata yi wani barcin kirki ba tana ta 'ya'yanta Ya cire hannunshi guda daya daga kan sitiyarin ya saka cikin tafin hannunta ''baby,me ya faruοΌ,naga kamar baki farinciki da dawowarmu gida'' zame hannun nata tayi cikin hade rai ''ka kula fa malam da kyau,tuqi kake,kada kaje ka zubar da mu''murmushi ya kuma yi yana qoqarin sake lalubar hannunta ''mutane biyu wadamda duk duniya babu wanda ke muhimmanci a gurina sama da su fa nake tuqawa,kinga ya zamarmin dole na kula iya kulawa'' bai qyaleta ba sai da ya kuma kamo hannun nata yana murzawa a hankali kuma atausashe yana lumshe ido,ta sake zamewa wannan karon tana fadin ''ada ka jimin ciwo bana bayan kai ka adana taka amaryar'' ba don ya daure ba saura kadan ya sheqe da dariya,ya sami sarai abinda ke cin zuciyarta kenan ''anzo gurin kadan kika gani yarinya,nayi alqawari kuma sai ya cika,da bakinki zaki furtawa abdallah kina sonahi,sai kinsam ABDULLAHI ba kanwar lasa bane,a jininmu yake''ya fada cikin zuciyarsa,a fili kuwa shima sai ya janyr hannunshi ya maida kam tuqinshi yana fadin ''au haka ne fa,am sorry''sauran qiris ta fashe amma bangaren zuciyarta ya tausheta πππππππ Dan qaramin biki suka je suka tadda anayi a gidan duk na taryar abdallah,duka 'yan uwan mahaifi da mahaifiyarshi ne da sukasan halin da ake ciki,saidai babu wanda baiyi mamaki ba ganin abdallahn kamar ba wanda ya kwanta cuta ba,ya sani sarai hakan ya samu asali ne daga kyawun weather na garin ni'ima da kuma kyakkyawa kuma cikakkiyar kulawa da ya samu daga maryam Cikin mahalarta taron harda SALMA da JIDDA wadanda ke ta binshi da kallon sha'awa da kishi,kishi kuma na banza,eh na banza mana don tunda ya kwanta babu wadda ta tako qafarta da niyyar gaisheshi,a zatonsu abdallan ya gama aiki ne cutar data sameshi ba qaramar mummunar cuta bace babu ranar warkewa to ko dama can shi ba yinsu yake ba ballanta na a yanzu da yasan ajin kowa babu batun komawa bangarensa a yanzu don mami tace bata yarda da gidan ba ma baki daya balle bangarensa don haka cikin dakunan dake corridor din nan guda hudu tasa aka gyara biyu,abdallah ya dauki daya maryam ta dauki daya,tana sane ta raba musu dakin don tuni tayi magana da hajiya laila ta sudan next weak ta zata shigo nijeria zata yiwa diyar mr presdent gyara jiki na bikinta da za'ayi so zata sauka gidan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138