Chapter 32
Chapter 32
ta gama shirin kwanciyarta tsaf ta tuna ta manta da littafin addu'o'inta cikin kitchen,hijabinta ta zura ta fito don ta dauko abdallah ne cikin falon gefanshi abida ce zaune ta sanya ahi a gaba tamkar zasu hade,magana auke qasa,qasa,son bata iya jiyo me suke cewa,tayi kamar ta koma sai kuma ta fasa tayi ahigewarta kitchen,tana qoqarin komawa taji tace ''ke zokiyi serving mutane,kin shige daki kin zauna sai kace baki san aikinki ba'' bata tanka mata ba sai da suka isa teburin,a sanyaye cikin jerartun maganganunta masu cike da nutsuwa ''idan baki sani ba sunana maryam don Allah ba ke ba,aiki kuma ba naki aka umarceni da inyi ba,ba don ke nazo gidan nan ba,so please don Allah mu girmama juna,tunda dukkanin mu 'yan adam ne,halitta mai qima da daraja agun Allah'' ''naqi na kirakin da hakan,kuma ni ba sa'arki bace kada ki kuma hada kanki da ni,ki dubeni ki dubeki mana,tundaga sutura ai kinsan da banbanci,kada ki kuma gigin hada kanki da ni'' shiru tayi mata domin ta fuskanci abidan tayi nisa,gwana ce itama gun girman kai,amma bata jin zata iya jurewa shararta ba sam,da iliminta itama da shekarunta,ba jahila bace bare tace zata dinga shiga gonarta tayi mata kashi ta qyaleta,ta kammala zuba musu tuwon semo miyar kubewa danya sai farfeaun kan rago a plate daban,a yatsine abida ke duban abincin ''meye kuma wannanοΌ''tayi tambayar tana duban maryam,banza tayi mata tamkar bata jita ba,don,kanta da ta gaji da shirun tace ''ni wlh soulmate bazan ci wanna abun ba,na manta wanne lokaci ne na qarshe,da na cishi,kinga malama ki ahiga kitchen ki dafa min wani abun'' ''awoyin shiga kitchen dina na yau sun qare,amma babu damuwa idan zaki iya jira zuwa gobe'' daga haka ta miqe tabar musu teburin,ahi kansa abdallah dan binta yayi da kallo ganin yadda yai take maida raddi babi kinkiri,fana iya jiyo ihun abida na zage,zage da hausa mixs da,harshen nasara wani lokaci harda turkanci ''oh god,pls don Allah ki yiwa maqogoronki afuwa,baki gajiya da fadaοΌ''abdallah ya fada bayan ya tallafe kumatunta ya sanya zazzafar qwayar idanunshi cikin tata,laqwas jikinta yayi,farinciki ya maye gurbin bacin ranta,tuni ta sanya hannu ta aoma kwasar tuwon sai gashi qarshe ta bige da santi ta cusa kanta cikin pillow ta sake rubtse idanunta akaro na barkatai,har yanzun dai bata daina jiyo tashin hayaniyar ba daga dakin abida muryar abida ce wani lokaci data abdallah,kuka take tun kusan rabin awa das,uka shuhe,sun hanat a bacci,ta kuma gaza fahimtar meke faruwa ''wallahi abdallah ko baka aureni ba indai ka kwanta da ni burina na duniya ya gama cika,don Allah abdallah ka amince wallahi zan iya rasa raina ayau idan ban samu cikar muradina ba,muna da dama abdallah muna da lokaci isashahe,mami bata nan daga ni sai kai kawi abdallah,pls ka taimaka min'' mamaki baqinciki da takaici suka sake cikashi,gumi ya kuma karyo masa,kimanin awanni biyu yana fama ta rabu da shi amma ta qiya,tun yana lalashinta yana qoqarin fahimtar da ita har ta soma bashi haushi,da ya miqe ta yago shi,har ta rabaahi davtshirt din jikinshi sai singlate kamar tsohuwar mayya,bayason gwada mata qarfi ne amma ya fuskanci sai ya biyo,mata ta hakan cikin zafin nama ya miqe ta sake yunqurin kamoshi,tuni ya watsar da ita ya fice kana ya maida maqulli ya rufe dakin,dai dai da fitowar maryam kenan wadda tayi niyyar barin dakin nata ta canza makwanci sakamakon hayaniyar da ta hanata sakat tasu a tsorace ta dubeshi idanunta cikin nashi,ganinshi a jargitse ga sautin kukan abida dake fitowa cikin dakin da ya kulleta,sai ta dan ja baya kadan zuciyarta ta soma harbawa,shi din ma ita yake kallo *mrs muhammad ce* [9/17, 12:52 PM] 80k: πππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊπΊ πΊππΊππΊ πΊππΊπ πΊππΊ πΊπ π πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πππππππ *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* ππΊππΊππΊ ππΊππΊπ ππΊππΊ πΊππΊ πΊπ πΊ βΆ2β£7β£ *_ubangiji madaukakin sarki yakanyi duba izuwa filin arfa,sai yace da mala'ika jibrilu,me bayin nan nawa suke nema haka(duk da cewa shine mafi sani),sun fito cikin tsananin zafin rana da qasqantar da kai?,sai mala'ika jibrilu yace''rahamarka da gafararka,sai ubangiji yace na gafarta musu''_* *_haka ubangiji s.w.a yake rabon irin wanna garabasar a filin idi,annabi muhammad s.a.w yana cewa''kada ku hana bayin Allah mata zuwa masallaci''_* *_sannan yayi umarni da a fita sallar idi maza da mata yara da tsofaffi_* *_yake 'yar uwa,kada ki bari wanann garabasa ta wuceki wadda baki da tabbas din ganin wata kamarta,Allah yasa mu dace,ya yafe mana kurakuranmu,yasa mu cikin bayinsa da za'a gafatarwa Allahumma ameen_* *_wannan shafin sadaukarwa ne ga dukkanin al'ummar musulmi,Allah ya karbi ibadunmu_* ci gaba yayi da lallonta kamar yadda take kallonshi,tuni oily eyes dinta suka qara sheqi da sakamakon tsoro da qwalla da ta tarar mata,zuciyarta na raya mata mummunan abu abdallah ya yiwa abida,cikin hanzadi ta juya da nufin komawa dakinta ta banke saidai taku daya biyu ana ukun ya cafkota ya maidota baya,take jikinta ya soma bari,bakinta na rawa ta soma fadin ''don.....d....don Allah kayi haquri,ka fufamin asiri'' galala yake binta da kallo,tuni ya gano manufarta,ganin taqi nutsuwa ya sanyashi daka mata tsawa ''me zayi dake da har kike tsammanin wani abu zan mikiοΌ,koyin ma zanyi kin min kadan 'yar tsakuwa,abinda nakeso dake kada ki kuskura wani yaji abinsa kika ganiοΌ,ina fatan kin fajimceniοΌ'' kai kawai take gyadawa babu qaqqautawa,burinta kawai ya saketa ta samu ta tsere,yana sakin nata kuwa ta shige dakin jiki na rawa ta murza key binta yayi da kallo cikin mamkin mummunar fassarar da tayi masa tashi guda,koda ya koma daki sai yaji abun ya tsaye masa a rai,ta tuhumeshi da laifin da bai taba sha'awar aikatawa ba,hasalima ya tsani mai aikata shi,gefe guda kuma tsanar abida ce fal cikin zuciyarshi,yaci alwashin koda zata rasa rayuwarta bazai iya aurenta ba,yana da tsananin kishi ya tabbatar koa ya aureta din bazaya samu kwanciyar hankali ba ππππππ kusan dukkaninsu kwanan zaune sukayi babu wanda ya runtsa,kowa da abunda ke yawo cikin rai da zuciyarshi,duk da hakan maryam bata kasa tashi yadda ta saba ba ta hada breakfast,saidai babu wanda yaci,bata san da hakan ba sai da mami ta dawo ta hau sama ta kintsa kana ta sake dawowa qasa don yin karin safe,abida qunar zuciya ta hanata fitowa,abdallah yayi sammakon zuwa ofgice saboda wani taron gaggawa da zasuyo wanda shi kansa bai san da shi ba sai da asubahin ranar his excellency mr presdent ya sanar mishi,saboda haka kiegin qarfe shida yabi zuwa abuja maryama kuwa tsoro da fargabar haduwa da abdallan ne ya hanata fitowa bayan ta samu ta kammala aikin ba tare da sun hadu ba ''shi kam abdallah ai ya jima yanzun a abuja,jeki kiramin abidar dai ta karya,ya zatayita zama bata ci komai ba'' kamar tace da mami ba zata iya zuwa ba don tana fargabar halin da zata je ta taradda abidar,bata da amsar tambayar da mami zata yi mata game da abunda zata ga ya samu abidan ba zata iya qin zuwan ba don haka ta miqe jiki a sanyaye ta nufi dakin,sai da tayi knocking sau biyar kafin a bada izinin shiga cikin qaqqarfa kuma kausa sashiyar muryar abidar ga mamakinta sai ta tadda abidar ta fito daga wanka ras da ita,babu wasu alamu dake nuna wani mummunan abu ya faru da ita ''meye kika tsaya kikatsaya kika zuba min idanun
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138