Skip to content

Chapter 136

Chapter 136

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,307 words 0 views Progress saved
Download Book

ba musamman abdul_ahad wanda dama danka na faro kusan shine tubalin sauran 'yan uwansa,irin tarbiyyar daka nashi to sauran ma idan ka haifesu zasu taahi ne kan aninda suka ga na gaba da su nayi wato babban yayansu,saboda ko yaushe suna tare,suna ganin irin abubuwan da yakeyi suma zasuyi qoqarin yin koyi da shi,hakann idan gurbatacciyar tarbiyya ya samu,da sun fara girma zasu bi sahunsa Ta shafa addu'o'inta kana ta miqe ta ninke abun sallar,mami ta dubeta ''ya kamata kam ki tafi haka ki kwanta maryamu,kullum ace sai kin tayamu hira zaki tafi daki ko kwanta,banda abunki ai bani,kadai ce a dakin ba balle kice kewa zata dameni,ga mai gida na ma baiyi bacci ba'' murmushi maryam din tayi cikin kunyarta din nan da har yau bata canza ba,har yau babu wani abu da ya ragu daga qaunar da mami ke mata sai ninkuwa ma da yayi ''kije ki,kwanta maryam kinji,Allah yayi miki albarka,haqiqa har *ABADAN* bazan daina alfahari da ke ba,kin cika uwa ta gari mai fidda kyakkyawar yabanya,fata na ubangiji ya cika rayuwarku da haske farinciki da kwanciyar hankali,kin haifa min jikoki maryam hudu ne amma inaji sunfi miliyan,sabida samun yara kamarsu wallahi ba don suna jikokina ba sai an tona,Allah ya miki albarka,Allah ya miki albarka''kanta na aqasa take amsawa da amin zuciyarta cike da farinciki da qaunar mami Wayar tata dake hannun abdul ahad ta dauki tsuwwa wanda tun tana cikin yin sallah ta ji tanayi,abdul ahad ya dubi umminsa ''ummi,abba ke kira tun dazun''yana saukowa daga gadon ya miqa mata wayar,ta riga da ta horesu,sam basa daga mata kira sai sun kawo mata ko sun sanar mata,ta daga kana ta kanga wayar a kunnenta ''please dear ki taho haka don Allah,i nedd you''murmushi ya subuce mata,kunyar mami tasa ta kana magana sai kawai ta katse kiran,minti biyu tsakani saiga tex dinshi ''gaskiya fa ina alkunya da yawa,na baki minti biyar matuqar baki taho ba da kaina zanzo har,gaban mami na sungumeki,kin sani zan iya ko?''murmushi ta sake saki taci gaba da duba agogo sai da ta minti biyar din sun cika daidai sanan ta miqe ta yiwa mami sallam,a bakin qofar dakinsu mamin taci karo da shi dauke da amatullah,dariya ta subuce mata ''gaskiya kun samu aikinyi,ta yadda kenan zata kwana cikin 'yan uwanta'' ''me ruwanki da mu?,kedai ki kuka da kanki,yau sai kin biya dukka bashin da kika ci''kai ta girgiza tana murmushi ta wucesu shi kuma ya shiga dakin Bandaki ta fada kai tsaye bata zauna ba,sai data yi wanka mai kyau kana tazo ta mulke jikinta da turaruka masu dadi wadanda ta siyosu dazu da rana da suka fita yawin miqe qafa,dukkansu na kamfanin alharamain ne masu dadi qamshi,daya daga cikin kayan baccin data siyo ta cira,doguwar riga ce har qasa mai hannun shimi mai azabar yauqi da santsi tana da dan duhun kala kadan ta sanyata,ta feshe kanta da turaren gashi kana ta rage hasken fitilar dakin ta haura gadon ta kwanta,jin shiru bai dawo,ba ya tabbatar mata yana can ana tataburza wata qila da amatullah,kiran da ya ahigo wayarta ne ya katse mata zancan zucin da take yi,lubabatu ce da hanzarinta ta daga don tana sa ran jin daddadan labari saboda sun baro nijeria hindatun nada tsohon cikin haihuwarta ta biyu ita da hisham dinta,ai kuwa abinda ta zata dinne ta sauka dazu qn samu baby girl da take ta sha'awar haifa,don haihuwar fari namiji ne ABDULKAREEM wanda yaci sunan mahaifin abdallah ''adda na haifawa abdul_ahad mata,din gaskiya tun yau na mata miji,ina son absul_ahad adda wallahi dama yaya abdallah zai barmin shi,amma na sani bazai iya ba don ya fimu qulafucinsa''dariya maryam ta saka tana cewa ''Allah ya tabbatar,zanso haka lubabatu,Allah ya raya mana baby'' ''adda sunanki taci fa,nayi alqawari dama ina fatan Allah yasa ta dauko halayenki,maryam sunanta saiki zaba mata nickname''ba qaramin farinciki maryam taji ba take tace ''mu dinga kiranta AMEERA ai yayi ko?'' ''yayi adda,Allah ya qara girma,kinga mama ce a gurina(maman maryam din)ga maijidda(kulu,da yake haka suka koma ce mata) ta takuramin sai na bata ta tuna kiki tsarabar da tace tana so,kuma wai abdus samad ya cika mata alqawarin da ya daukar mata''dariya ta saki kana tace ''kice mata sunfi kusa,don abdus samad yanzu,haka,ma ya jima da yin bacci amma gobe zan kira na hadasu'',ta karba suka gaisa kana ta hadata da mama ma suka gaisa sannan sukayi sallama Bata kai ga ajjiyewa ba kiran shamsiyya (qanwarta yar inna hadiza)ya shigo,suna gama hira zara ta kira sai bintu kamar hadin baki,dukkansu taya ta murna suke kan zuwa ta daya da abdul_ahad yayi,taji dadi sosai kan yadda kullum Allah ke dada hada kansu suka fuskanci gaskiya suka zamo tsintsiya madaurinki daya,tana cikin addu'ar bacci ne jin shirun na abdallah yayi yawa kiran hindatu ya shigo,tana kaiwa kunnenta abdallah ya shigo dakin yana sakin hannun rigar baccinsa da ada ya nannade,dariya ya bata cikin zuciyarta tana cewa hala dambe akasha kafin amatallah ta yarda ''ke kam baki duba agogo?mufa anan qarfe sha biyu na dare'' ''tun dazun nake kiranki naji busy wayar taki'' ''eh wallahi muna ta waya da su azara'' ''lubabatu ai ta haihu,shegiyar gari,dazu naje gidan na gama yi mata tsiya ai,can na samu su shamsiyyan ma....''maryam din na shirin tambayarta tsiyan me abdallah ya wafece wayar ya kara a kunnensa ''sai da safe,a barmin gimbiya ta ta huta hakanan''ya fada,dariya hindatun tayi tace ''ranka ya dade,girman kujerarka,ai kafi gaban haka ma,Allah ya bamu alkhairi'' ''ameen,ki gaida min boss(haka yake kirab jabir idan yaso tsokanarsa) da duka yaran''daga haka ya katse wayar yana jifan maryam din da wani shu'umin kallo Bayanta ya fada kana ya janyota ya rungumeta tsam a jikinsa dukkansu suna murmushi yace ''idan na barki da wannan hindatun yauma saidai na haqura'' murmushi ta saki a boye cikin son jan tsokana ''yanzun ma haqurin zakayi,tunda jibi zamu koma so nake nayi bacci sosai don gobe wuni nakeso nayi a harami ina da addu'o'i sosai''bai bi ta maganarta ba ya fara aike mata da saqonni sannan yace ''wacce buqata kike da shi haka,tunda kika sameni ai baki da sauran matsalar rat yuwa''murmushi ta saki kaina ta juyo suka koma fuskantar juna numfasinsu na,haduwa guri guda,fuskanta qunshe da kyakkyawan murmushin daya bayyana fararen haqoranta,kasa daurewa abdallah yayi har sai da ya shafi fuskartata yana fadin ''maryam diyana''wani murmushin ta kuma yi ta kwantar da kanta cikin qirjinsa,don duk lokacin da ya mata irin haka din tssan ta taba zuciyarshi sosai,sai data saki ajiyar zuciya sannan tace ''ba shakka bawan Allah ka gama tare min komai,na tabbatar da cewa na gama samun aljannar duniya tunda Allah ya mallakamin miji kamar kai,ya bani baiwar 'ya'ya nagartattu,ya bani suruka irin mami,ya bani mahaifiya irin mama,nikam Allah ya gama min komai babu abinda ya rage gareni face inta miqa godiya ta agareshi tare da neman lahira ta kuma''kai ya jinjina yana sake jin qaunarta a ranshi,duk da ni'ima da daular da take ciki hakan bai hanata tsayawa,bautar Allah ba ka'in da na'in,hatta da abdus samad dan shekara goma sha biyu ta koya masa azumin tadawwu'i,su amatul jabbar ne kadai basa yi suma jira take sukai shekara goma goma,mace ta gari kam ya riga da ya gama mallakarta sai godiya ga madaukakin sarki ''dazun bayan fitata kai

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138