Chapter 6
Chapter 6
ka,wanda dashi gwara babu''tofa baki yasan abinda zai fada baisan me za'a mayar masa ba kamar ta zubawa maraqisiyya ruwan zafi ta,lsilayo wani uban ashar din''wlh zaki san kinyi da huwaila 'yar hadiza,auren da kike taqama ayishi mu gani'' ''Allah ya fiki ya fi wanda ya fiki ma''hindatu ta fada wadda maryam ta tura daki tana mata gargadin kada ta sake cewa komai,sai kuma abu ya dawo kanta bata kula kowa ba ta fice inda ta nufa cikin zuciyarta cike fal da tsanar halayensu ππππππ Saura kwana goma biki aka kawo lefe,lefe ne na gani na fada wanda ita kanta maryamu ta yaba qwarai da gaske,qarara rudewar su huwailan ta fito,sumbatu suka dinga yi don duka cikinsu babu wadda ta aurar da 'yar da ta samu lefe kwatankwacin haka,komai sai da suka masa dilla filla suka qare masa kallo abinda ya bata mamaki ganin dukkan 'yan gida sun shiga shirye shiryen bikin gadan gadan,kada ma inna hadiza taji labari,duk da ba shiga sabgar su maryamun take ba,harda cin bashi da sauya furnitures din daki maryam na zaune gefan mamanta tana lissafa mata sunayen mutanen da zata tura hindatu takaiwa cingam tana rubuta mata a takarda hindatun ta shigo,hannunta ledar dinkunanta ne da ta door mat da maryam ta bada ta siyo,ta zauna kan kujera tana fadin ''sannu harkin dawoοΌ'' ''eh wlh amma fa na sha wuya''ta fada tana shiga kitchen ta dauko ruwa cikin gorar faro da suke durawa susa a fridhe dinsu,sai da tq shanye sannan tace ''mama'' ''na'am'' ''nifa abun nan na bani mamaki'' ''mefaοΌ''ta tambayeta tan duba rubutun,da maryam keyi ''su hauwa mana da su jamila,gaba daya sai hidimar biki ake yi,kada ma jamila taji labari ita da mamanta,mutanen da aduniya babu wadanda suka tsana kamar muοΌ'' sai a lokacin maman ta kalleta duka harda maryam din ''to,banda abinki hindatu sai ku godewa Allah,me yiwuwa Allah ne ya ganar da su gaskiya,tunda babu wanda za'ace *ABADAN* zai dawwama a halin da yake,dole watarana akwai sauyi,qila Allah ya ganar da su ne'' ''nima dai mama haka nayi tunani,kuma wallahi bakiji dadin da naji ba,Allah yasa silar gyaruwar tsakanin mu kenan'' ''ameen''cewar mama,ita dai hindatu tabe baki tayi tace ''to Allah yasa,amma ba girin girin ba tayi mai'' sallamar jamila ce ta katse hirar tasu,dukkaninsu suka bita da kallo,don basu iya tuna yaushe ta shigo dakin na qarshe,koda sun tuna ma ba alkhairi ne ya kawo ta ba ''sannu mama'' ''yauwa sannu'' ''gurin maryamu nazo'' ''to gani''injita ''cewa nayi yaishe zqki lalle,ina son na biki ne muje tare,kinsan qannan amarya dole su fito kamar amaryar'' sosqi maryamun taji dadi har ta saki tattausan murmushin ta ''ai ba damuwa,jibi ne sai mu tafi tare ai'' ''to shikenan''ta juya ta fice hindatu ta kalleta ''haba ya maryam,nidai gaskiya bazan hada tafiya tare da su ba'' ''sai ki fasa zuwan ai''inji mama ''don kuwa ni zan biya mata ma kudin lallen,haba hindatu dan uwanka dan uwanka ne fa,kuma ka dinga kyautatawa dan uwanka musulmi zato,ki zama mai tsarkakkiyar zuciya kinji qanwata''dole hindatun taja bakinta ta tsuke Tare suka je lallen maryam hindatu da jamila,ita biya kudin dukkaninsu πππππππ cike gidan yake da mutane kasancewar yaune ranar daurin aure,ga gauyar yan uwa daga bangaren mama da inna hadiza,kusan yawancin danginta na cike a gidan danqam,har ita kanta maman tayi mamakin hakan,amma sai ta share,batun sanin cewa babu yadda Allah baya iya sauya lamarinsa maryam na maqotansu ita da qawayenta ciki harda raliya,tayi shar cikin atamfa super riga da zani plain,ba qaramin kyau tayi ba,fuskarta cike da walwala da farinciki guda suka dinga ji tana tashi sosai tamkar a cikin gidan akeyi kasancewar maqota ne gida jikin gidan,raliya ta saki tata gudar tana fadin ''shikenan alhmdlh an daura,tazama tazama,yau diyana ta shigo sahu,Allah yasa wata tara iwar haka mu hadu suna''dariya duka aka saki wasu na cewa amin wadda shigowar hindatu cikin gunkin kuka ya katse musu ita maryam ce ta soma miqewa tanajin qirjinta na bugawa tun kafin taji me ya samu hindatun zuciyarta ke mata saqe saqen munanan abubuwa zubewa tayi gaban maryam tana fadin ''ya maryam don Allah me kika yiwa ya jabirοΌ,me kika yi masa da zai miki wannan sakayyarοΌ,me kika yi masa da har ya guje miki ya maida aurenshi kan *JAMILA*οΌ'' dum taji kunnuwanta sunyi,qwaqwalwarta lokaci guda ta gaza yin aikinta,sai ta daina gane komai,meke shirin faruwa d itaοΌtambayar da taji qwaqwalwarta na mata kenan,kafin bijirowar amsar sai taji tamkar an zare dukkan wata garkuwa da ta sata ta iya tsaiwa da qafafunta,yaraf taji ta zube,daganan komai ya dauke mata dif kamar an dauke wutar nepa adaki mai tsananin duhu........ *mrs muhammad ce*π πππβπ»βπ»βπ»βπ» [9/17, 12:50 PM] 80k: πππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊπΊ πππππππ πΊππΊππΊ πΊππΊπ πΊππΊ πΊπ π πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πππππππ *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πΊππΊππΊππΊ ππΊππΊππΊ ππΊππΊπ ππΊππΊ πΊππΊ πΊπ πΊ βΆ6β£ ''ya maryam,me kika masa da har ya guje miki ya maida aurensa kan jamilaοΌ'' maganar da keta amsa kuwwa cikin kunnenta kenan bayan ta farka,sai hawaye ya fara turereniyar fitowa daga runtsatsun idanunta da ta kasa budesu suna bi ta gefan fuskarta su sauka har cikin kunnenta,wani irin yanayi take ji daban cikin zuciya da gangar jikinta me ta aikatawa jabir da zafi haka wanda har ta cancanci wannan hukuncinοΌ a iya saninta ba zata iya tuna abu guda ba mara dadi da ya taba hadasu a tarihin rayuwar soyayyarsu ba hindatu ce ta fara ankara da farkawar tata ta sanadiyyar hawayen fuskar tata dake bi ta gefen kuncinta,da sauri ta taso ''sannu ya maryam,me yake miki ciwo yanzu'' kai kawai ta gyada mata alamar babu komai mirya can qasa tace ''dagoni hindatu'' a hankali ta taonaka mata ta tashin ta jingina da filo sannan tace bari na kira ''mama'' maman ce ta takurata kan ta tashi hindatu ta rakata asibiti,bata biqatar fita koda falon nasu ne don bata san da wanne iso zata kalli jama'a,hakanan suma batsan da wanne ido zasu dubeta ba,ta tabbatar maganar ta gama zaga unguwar ma gaba daya ba gidan ba,amma ba zata iya misa mata ba don ita don ma so take tadan gusa daga gidan saboda haka ta zura hijabinta hindatun tace bari ta nemo dan adaidaita sahu sai tayi mata magana bayan fitar hindatun shiru dakin yayi,baka jiyo komai sai hargowa da hayaniyar jama'arsu huwaila da inna hadiza cike da farinciki,mintuna biyar sai ga hindatun ta dawo ita ta riqe maryamun suka fito yayin da 'yan uwan maman nata dake zaune jugum a rumfar tasu suke mata sannu da jaje,don tuni wasu ma soma hada kayansu don komawa inda suka fito Sun samu ganin likita cikin qanqanin lokaci don private clinic suka je,likitan yace zai riqe ta zuwa magariba ta huta sosai tasha magungunanta,bata musa din ba suka bata gado hindatu na tare da ita basu bar asibitin ba sai magariba,suna hanya ne hindatu tace''anty raliya ta kira ki har sau biyu kina bacci,tace zaga sake kira,ya nasir ne yayi kiranta tunda kuma ta fita bata dawo ba'' kai ta iya gyada mata kawai don bata jin zata iya bude bakinta suna shigowa layin gabanta ya dinga dukan uku uku,ji take tamkar ta,canza wani gidan ba nasu ba,ji take kamar ta yanka a guje ta bace a nemeta a rasa,motocine a jere har zuwa qofar gidan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138