Skip to content

Chapter 37

Chapter 37

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,274 words 0 views Progress saved
Download Book

na ake ko ina,ance na kasa kula da yaya matan da Allah ya bani,dukkansu babu mai zaman aure ko wacce rabi aure rabi zaman gida,ga wasu kuma sun kasa auruwa'' zuciyar mafuam ta kada don tasan maganar qarshen tata ce ''to wallahi ya isheni haka,kun gama mai da ni mutumin banza ko,baku isa ba wanna karon na gaji ko masu auri suyo zaman auresu marasa aure suyi aure ko inci uban yarinya wallahi'' ba inna hadiza kawai ba hatta da su maama sunyi mamaki,yau baane ke ja in ja da inna hadizar?,lallai a dade anayi sai gaskiya,komai yayi farko qarahensa na zuwa babu shakka,a bangaren inna hadiza kuwa ta gama qullatar huwaila ne dadi bisa dari kan dukkan bala'in da taga ya afko,mata babu shakka ita ta qulla zuwanshi qasa mama tayi da kanta tana fadin ''Allah ya huci zuciuarka malam,a yi mana afuwa'' sai yaji zuciyarahi ta dan rage zqfihar ya juya ya dan dubi maman,sannan ya maida idonsa gasu hadiza wadanda sjka zuba masa iddo qir babu mai cewa komai,baba hadiza na huci tana jiran ya gaya mata cuta ta fada masa mutuwa ''ke jamila ki tsaida hankqlinki,mahaifinki ne wanna,ki fada masa ya aayi hakan ta kasane don,samun bakin zaren,so ake a gyara lamarin ki koma gidanki kuci gaba da zama,mutuwar aure gun diya mace ai faduwar daraja ne,saidai kuma idan na qaddara ne''cewar mama jin an sako maganar komawarta gidan jabir ya,sanyata cikin rawar jiki ta bude baki zata yi bayani a wautarta da jahilcinta za'a maidata din,don a yadda ta dandana zaman daula bata jin zata iya zaman gidan nasu kona wata daya ne bare na dindin din tuni inna hadiza ta katsi numfashin jamilar ''uban me zaki gaya musu,cin fuska yaso yi miki kawai,ya aureki da kansa sanna yace baisan ya aureki ba,kujimin da,ke kuma aminatu banason munafurci da gilma,ina ruwanki?,ina cewa dai jamila bake kika haifa min ita ba,ai na dade da sanin cewa abunda kike nema kenan saboda har yau baqincikin qin aurar diyarki da baiyi ba yana nan cikin zuciyarki,to ahir dinki ki fita sabgata data yara na'' tsawa baban ya daka mata ya kuma ce ta ta shi ta fice masa adaki,koda ta ficen da yake ta riga da ta rainashi sai tayi tsaye abakin window tana eqa dakin tare da kallon jamila tana mata gargadi *mrs muhammad ce*πŸ‘‘ πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ»βœπŸ»βœπŸ»βœπŸ» [9/17, 12:53 PM] 80k: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺🌺 πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸŒΊπŸ’– πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸŒΊπŸ’– 🌺 β–Ά3⃣0⃣ *_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* dauke kanta tayi tamkar bata ga gargadin nata ba,domin burinta kawai a maidata ga gidan jabir,don ba jabir dinne ma yafi damunta ba tunda bashi daman take aure ba dukiyarshi take aure,tana da abokanan holewarta a waje a take ta warware musu yadda tayi amfani da sihirtaccen kwalli da turare har sau biyu ta dauke hankalin jabir ya aureta cikin gushewar hayyaci gumi ne kawai ke ketsatstsafowa maryam,bata sake jin tsananin tausayin jabir ba sai a lokacin,shikam baban nasu shiru yayi ya kasa furta komai,kimanin mintina biyar sanna ya dubi su binta yace su fita adakin,sumi sumi suka fice ya dubi huwaila da tayi tsamo tsamo ''duk abinda kukayi huwaila don kanku,amma ku sani dole ne ku nemi yafiyar maryama don an zalunceta'' ya waiwaya ga inna hadiza dake labe yace ''kije Allah ya isa tsakani na dake,tarbiyyar yara da kika bata min,haqqin maryam kuma ke da ita,kya sake samowa jamilar wani mijin,ku taahi dukkanku ku bani guri'' dama a qagauce suke saboda kunya da nauyi tuni suka fice,saura maryam da mama,miqewa itama maryam din tayi ta ajjiye masa kudin hannunta ''ba wanna babu yawa amana addu'a,kuma kayi haquri Allah ya huci zuciyarka,insha Allahu zamu gyara dukkan abinda baka so'' ''na gode,Allah yayi miki albarka,baki gaji ba maryam baki dade da yi mana hidima ba,har yanzu abincinki ake ci a gidan nan'' ''ba komai baba,kunfi qarfin haka ai'' tana shirin ficewa mama tace ''dawo ki zauna ayo maganar yaron nan a qareta'' cikin rashin fahimta baban ya dubeta ''au ta samu wani mijin ne?'' ''eh,gata nan ta maka bayani''inji mama bayan ta miqe tana tattare kwanukan da ya karya kanta a duqe ta gaya mishi iya abinda ta sani game da abdur rahim din ''to,madalla,sai a sanar masa ya turo kawai,ai babu wani bincike da za'a tsananta tunda kina sonshi kuma ma kada muje ya subuce mana garin binike,kinsan wani baya son tone tone'' sai taji,maganar ta mata wani iri taya za'a dauketa adanqata ga mutumin da ba'a binciki wayeshi ba,sanna kuma uwa uba daga haduwarsu jiya sai tace ya turo magabatansa,tilas sai an nuna masa an gaji da zamanta dama sai ta lanqwashe murya tace ''baaba,ina ganin an dan badakamar wata guda ko fiye kafin ayi masa maganar turowar,sanna baba ka gafarceni ayi binciken inaga haka sai yafi kyau'' ''hmmm,karatun boko ya bude miki ido mero''ya fada yana murmushi bata ji dadin yadda ya fassarata ba,don ita tayi ne da zuciya daya,tayi ne don gujewa auren jeka nayika ''shikenan tunda kin zabi hakam,amma kada kiyo kuka dakowa idan shima ya kama gabansa kafi wata gudan,maganar bincike kuma tunda ya gaya miki unguwarsu na baki wuqa da nama kiyo kinga kin hutashaheni ma'' hawaye ni ya silalo mata,bata taba jin inda 'ya takewa kanta binciken ma'aurinta ba,amma yata iya jaka tata *qaddarar rayuwar* take,ta kuma godewa Allah da bai sata ta kauce hanya ba duk da yadda ta tsinci rayuwar tata cikin tsangwama ''na gode baba,Allah ya gara gima''ta fada aladabce ''ameen ameen,idan kin fita ki turo min iwar taki'' tare suka karya da lafiyayyen qosai da kunun tsamiya wanda yasha lemon tsami,sosai tayi namijin qoqarin fidda dukkan damuwa daga zuciyarta suka karya din cikin wawala sun tattauna da mama kan atamfofi da take so ta dinga sarowa maman idan tadauki albashinta na wannan watan ko falle bibbiyu ne ta fara saidawa agani idan zasu karbu,albarka maman kawai ta shi mata tare da mata kyakkyawan fata sai la'asar ta fara shiri tafiya,hindatu tace ''ki jirani adda maryam mu fita tare zanje duba jamb dina,tun jiya naji sanarwa ta fito'' ''to kiyi,maza ki shirya don so nake naje nayi abincin dare,jiya duka baaba uwani na dorawa aikin'' ''gaskiya kam,don ma muta nene masu karamci da mutunci'' inji mama dake ta hadawa mami su kuka daddawa kubewa man shanu da sauransu qarfe biyar sukayo sallama da mama ta fito don raka su,jamila ce tsaye a tsakar gidan sanye take dai da swiss lace dinta tun na shekran jiyan,mai tsada ne amma gaba daya ya yamutse yasha squeezing,fuskar nan ta hqutsine kamar dakalin kashi sqboda tsabar bqcin ran da take,ciki da baqinciki uwa uba kwana biyun nan bata saurari wanka ba,gabanta hadiza ce riqe da kwanon da yasha uwar lamba shinkafa da wake da manquli ce aciki da barbaden yaji ''haquri fa zakiyi kici tunda dai na ba gidanki bane,mu bamu da wani miyar nama da zamu zuba miki,kina kallo haka suma qanna naki suka ci'' ''idan naci wannam abun Allah ya tsinen hadiza,wai ma meye amfamin kudaden da na ringa satowa ina kawo miki duk ina kika kaisu?,kinje kin rabawa garadan soro sun cinye kuma gashi nan auren da ake ta tattali din ya tsinke....'' da

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138