Chapter 22
Chapter 22
hannunshi ya saka ya riqe inda yake tsammani iya nan dafin ya tsaya zaune yake a falon tunda ya fito a kitchen din,da alsmu xafin harbin na damunshi sosai,duk da 'yan dabarun da yayi,duk sai ta shiga damuwa tana jin itace sila,ta rasa da me zata taimaka masa,duk sanda ta matso gun da yake sai ta kasa tabuka komai saboda kwarjinin da yake mata,qarshe sai tq koma kitchen din ta dauki wayarta ta kira mami ta sanar mata sosai mamin ta rude tace ta gaya mishi ya taho asibiti yanzun lallai kwance ta sameshi saman doguwar kujera a darare ta matsa kusa da shi kadan cikin sassanyar muryarta ''mami tace ka sameta a asibitinta'' sam bai ji isowarta gun ba sai saukar siririyar muryarta jin shiru ya sata sake maimaitawa kusan minti uku kafin yace ''leave me alone pls,bani son naci tunda ni ba kurma bane,sannan bani son gulma,har kin kirata saboda tsaban gulma,bace min a gun'' bata damu ba tunda ta isar da saqon mamin dai,kitchen din ta koma ta fara soya patatoes bolls din duk da rabin hankalinta na ga abdallah wanda bata ji motsin tafiyarshi ba,dalili kenan da yasa taa kammala suyar ta sauke man ta leqo falon,yana kwance abinshi yadda ta barshi,sai 'yar nutsuwar da ta samu tayi qaura,waishi wane irin mutum ne da ciwo ke cin jikinshi amma bai damu ba cikin dan qwarin gwiwar da ta tattara ta sake nufarshi da nufin tunassr da shi koda qila ya manta,saidai kafin ta qarasa wayarshi dake ruwan cikinshi ta dauki sassanyar ringing alamun shigowar kira da alamun kasala ya dauki wayar ya duba mai kiran nasa ya amsa bayan ya maidata handsfree ya dorata saman cikin nasa ''abdallah yaya me na jika shiru?,ko maryama bata sanar maka saqona ba?'' cikin murya mai kama da ta mai bacci yace ''ta gayamin mami,kawai....'' ''ya isa bana buqatar uziri,na baka minti talatin in ganka a office dina ok?'' ''yes mami''ya fada daga bisani wayar ta katse cikin sanda ta juya don komawa da baya tunda bai ganta ba ''dakata a nan''ya fada cikin kaurara murya,cak ta tsaya din yayin da shi kuma ya miqe a hankali ''sai ki fito amma zan sake maimata miki ni bani son shishshigi''daga haya ya juya yayi waje motoci hudu ne baqaqe masu azabar kyau a jere,tun kafin ta qaraso taga abdallah tsaye jikin daya,xubaida ce ke fuskantarta bisa alamu magana suke,isowarta ne ya sanyata jin maganar qarshe da abdallah ke fadi ''nacinki kullum sawa yake ina dada tsanarki,bana son shishshigi bana son naci kuma bana son takura,ki tambayi nene tun asali ke ba type dina bace,bazan taba auran macen da bata yimin ba,ba ko wacce irin mace nake so ba,for now ya kamata ki gane hakan'' ya sanya hannunsa ya janue hannunta data tokareshi da shi ya bude bayan motar da kanshi ''naji abdallah,amma atleast dai a yanzun ka barni na raka ka asibitin bai cancanci ka tafi kai daya ba'' ko kallo bata isheshi ba don tuni ya gama maganarshi da ita ya juya bayanshi yace da daya daga cikin security dinshi su rage biyu daga cikin motocin da biyu za'a tafi,ya rufe maganar da fadin ''ko kun manta muna bincike kan alhj haladu uba mai qusa,kuma banson yasan ina cikin garin nan,ku kiyaye'' ''yes,sir''ya fada cikin girmamawa kusan tare shi da zubaida idonsu yake kan maryama dake tsaye daura da su ''me kika tsaya kina wa mutane a gurin?'' cikin tattausan muryarta tace ''bansan wacce mota zan shiga ba ai'' ''saikiyita sanqamewa anan har a tashi qiyama''ya fada yana shirin shigewa motar ''amma abdallah wannan ita kuma fa?'' wani kallon biyu babu ya mata cike da quluwa da tarin tambayoyin da nabu macen da isa ta masa su idan ba maminshi ba,tsaki ya ja mata sannan ya ja motarshi ya bame sun gama reverse suna shirin ficewa maryama dake motar baya cikin gidan baya a takure saboda su uku ne maza biyu ita ta ukun taji an dakatar da su,abdallah ne ya fito ya qaraso har gaban motar,glass din duka motar yasa suka sauke ya qare musu kallo sannan yace da na gaban motar ''you are verry stupid lawal,oya getout ka koma baya,ke kuma ki fito ki dawo gaba saunar yarinya kin shige cikin maza kin wane qwame'' yana tsaye akayi hakan sannan ya bisu da tsaki ya kona tashi motar duka direbobin suka ja suka fice a gidan *ABDULLAHI SPECIALIST HOSPITAL* shine abinda ke rubuce jikin wani makeken allo dake maqale a goshin ginin benan asibitin,wanda ko daga ina ka taho zaka gani saboda girman allon da rubutun da kuma tsahon benan,gini ne na alfarma tamkar ba asibiti ba,komai neat bisa tsafta tsari da kuma qwarewa,tun daga parking space ma'aikatan dake cikin harabar asibiti leburori da masu gadi suka soma tururuwar zuwa gaida abdallah,ga mamakin maryam hannu yake basu suna mudabaha cikin fara'a da sakin fuska a haka suka ratsa cikin asibitin har zuwa sashen da office din mami na musamman yake ''wonderful,abdul dama kana nigeria?''suka ji an fada,wani matashi ne wanda ke nufosu yake fadar haka,sanye yake cikin qananun kaya wanda kallo daya zaka mishi kasan dan birni ne yasan gayu gayu ya sanshi,ba wani mugun kyau ne da shi ba amma iya adonshi ya bashi sunan kyakkyawa da fara'a sukayi musabaha da abdallah ''idan ban manta ba shekaru biyar rabona da kai abdallah,yanzu laifin kudrat sai ya shafi mansur?'' dan qaramin murmushi ya saki kana yace cikin basarwa ''manta kawai friend ya bayan rabuwa?''sai alkhairi abdul,hala wannan ce madam din tamu?'' wani haushi ya kama abdallah don yasan ba kowa yake nufi ba sai maryam,sai ya zuba mata ido yaga yadda zata karbi maganar,babu abinda ya fuskanta tattare da ita don kanta a sunkuye yake jinta take kamar ta,zura a guje,ta takura matuqa cikin tafiyar nan maida kallonshi yayi gun mansur ''kada ka sake fadi,cook dina ce,nazo ganin mami na ne ta shigo cikin sahun bodyguard'' murmushi mansur din yayi ''tofa wannan karon babu rabuwa abdul,bani adress dinka,zan sameka har gida,ina da magana da kai'' saboda yanayin aikinshi yasa bai bashi adress din gidan ba kai tsaye sai ya amshi phone num din mansur din yace zai nemeshi duk lokacin da zasu hadun,sukayi sallama kana suka nufi office din mami duka a waje suka tsaya abdalla ne ya shiga ciki,fitowar mamin kenan daga toilet ta daura alwala ''ina maryam din''ta tambayeshi tana shimfida abun sallah ''suna waje'' ''kana nufin har ita din'' ''eh mana mami,har da ita'' ''koma ka shigo min da ita'' cikin shagwaba yace ''yanzu mami a gabanta za'a min treatment din bayan da zafi kuma salon ta raina ni'' ita dai mami bata kulashi ba ta tayar da sallarta,tilas ya koma yace da lawal ya shigo da ita *mrs muhammad ce* [9/17, 12:52 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺🌺 💖💖💖💖💖💖💖 🌺💖🌺💖🌺 🌺💖🌺💖 🌺💖🌺 🌺💖 💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺 💖💖💖💖💖💖💖 *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺💖🌺💖🌺💖🌺 💖🌺💖🌺💖🌺 💖🌺💖🌺💖 💖🌺💖🌺 🌺💖🌺 🌺💖 🌺 ▶1⃣9⃣ teburin mamin yayi zamanshi yaja laptop dinta yana danne danne ya barta nan a tsaye,a haka mamin ta kammala sallarta ta shafa addu'o'inta ''sannu maryama ya akayi kunama ta sami abdallah?''mamin ta fada cikin kulawa tana linke sallayarta ''tsautsayi ne mami''taji abdallah ya amshe zancan yayin da tayi duru duru tana tsaka da neman
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138