Skip to content

Chapter 46

Chapter 46

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,276 words 0 views Progress saved
Download Book

da ta bi gidan da kallo,duk kyau na gidansu mamin wanna ya dokeshi,bude motar yayi yay ficewarsa ba tare da da yace mata komai ba zaman kusan awa guda da rabi tayi kafin ta sake ganin fitowarsa,a dan bakin qofar ya tsaya kafin ya qaraso tana iya hango jikin wanda suke magana tare,da alama macece don ga gefan mayafi nan,ba qaramar qufula tayi,ba cikin zuciyarta ''zance yazo kenan ya barni a mota ko yaya?''ranta sai ta kuma ji ya baci,ya bude motar ya shigo ''zance da ranar Allah cikin watan azimi,wanne wane irin tsari ne''ta ja tsaki,saidai cikin subutar baki tsakin ya fito juyowa yayi kalleta ''wa kike ma tsaki?''sai ta juyo tana kallonshi itama ''idan kika sakemin tsaki sai kin fita min a mota tunda bada kudinki aka siya ba''sai idanunta suka wal ''daina kallona''ya fada bayan ya dauke kanshi da sauri daga cikin idanunta ''kada ki cuceni''ya fadi can qasa yana lumshe idanu tarw da yiwa motar key,bata kawo komai cikin ran ta ba ta dauke idonta cike da jin haushinsa πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ² Ashirin ga azumi mami ta bata kayan sallarta,a dinke suke dinki ne na gayu wadanda suka mata cif a jiki,atamfofi uku lace daya material daya,sai codelace shima daya,duka atamfofin dogayeb riguna aka mata don mamin ta fuskanci tana sonsu,jaka biyu takalmi biyu sai mayafi biyu hijabi daya,sannan tace ashirin da biyar ga azumi zasu fita sai ta zabi fashion da zatayi amfani da su,bata fasa yiwa mami gidiya ba duk da ta gaya mata diyarta ta yiwa no need tace sai ta gode mata,godiya kuwa ai tamkat wajibi ne tayi mata don ko daga gurin mahaifinta bata taba samun makamancin irin wannan gatan ba abida kam akwati guda medium abdallan ya hada mata bayan takurawar da mami tayi masa kan ya hada matan,don shi totally baiyi niyyar mata komai ba cikin irin kyautar da mamin ke yawan yi mata ta fidda atamfa biyu ta baiwa tela ya dinkawa mamanta,ta siya mata mayafi takalmi da jaka,albashinta na watan ciki ta cira ta baiwa hibdatu tayi siyayyar salkarta babanra ma shadda ta siya masa kala biyu ta hada mishi da kudin dinki da takalmi da hula daidai,kai kada ksso kaga baqinciki,ina wuta a saka maman da iyalsnta,godiya kam gun baban ba'a magana ''sai yanzu nasan na haifa,yanzu ne na fara cin albarkar haihuwa''baban ya fada lokacin da yake gwada hular da ta kawo masan ''oho dai,wlh malsm ka guji ranar da zaka karbi shegen jika cikin gidan nan,ka gama cin dadin dai wuyar na tafe,shi yasa gata nan har yau babu mashinshini yo kowa yasan aikin tsiyar da take aikatawa'' inji baba hadizar don daga ita har huwailsn babu wanda yasan da zancan kawo kudinta,ranar kamar Allah ya kadasu duk suka fice unguwa suda qananun 'ya'yansu,huwaila tayi gurin boksn boginta ita da uwale hadiza ma ta bazama ga nata bokan,sunacan yawon asara har yan kawowar suka tafi,'yammatan da zawarawan kuma na nade a gado suna bacci don wadan nan sukan kai sha biyu da rabi zuwa daya basu tashi ba huwaila kuwa cewa tayi''mu namu ai shegensu mukayi muka shigo dasu gidan ko,ko ince tsinannu ne''shidai babu wadda ya kula cikinsu ya kwashe kayanshi ya shige dakinsa πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚ Qarfe goma suka dawo daga siyan kayan kwalliya da suka fita harda mami da abida,tayi sallama da mamin ta shige dakinta don da wuri take son yin bacci ta tashi akan lokaci sallar dare saboda yau an kai azimi ashirin da shida zuwa anjima daren ashirin da bakwai zai shi daren da akesa ran dacewa acikinsa zuwa sha daya na dare takammala komai ta haye gado bayan ta gama addu'o'in kwanciya ta karanta saqon abdur rahim fuskarta fal da murmushi,kusan cikin watn gaba daya wayarsu bata fi aqirga ba sai tex akai akai,yace shikam bazai iya jurar jin muryarta ba,tana shirin kashe wayar kira ya shigo,ta zubawa lambobin ido tana kallonsu,tana tunanin inda ta taba saninsu tabbas ta taba sanin numbers din,har wayar ta tsinke ta kasa dagawa,second biyar tsakani wani kiran ya kuma shigowa,jiki babu qwari ta sanya hannunta ta daga ta kara akunnenta ''assalamu alaikum wa rahmatullah''itace abinda yavdaki sodon kunnenta,mummunar faduwa gabanta yayi,babu inda zata ji muryar ta kasa ganeta,amma tan tama take kiran nata ne ko batan kaine,ta sake cire wayar akunnen ta tayi ta kuma duba screen din wayar mai kiran dai na bisa layi kuma ita din aka kirar *mrs muhammad ce*πŸ‘‘ πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½ [9/17, 12:54 PM] 80k: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’– πŸ’– *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊ πŸ’– Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* β–Ά3⃣4⃣ *_daga abu hurairah Allah ya qara yarda da shi yace:an tambayi manzan Allah s a w wanne musulmi ne yafi falala?,sai yace:wanda musulmi suka kubuta daga sharrin harshensa da sharrin hannunshi(ma'ana bai cutar da kowa da harshensa ta hanyar magana,ko kuma da hannunshi ta hanyar ayyukansa,daure ka/ki zama daga cikin musulmin da suka fi falala,abun ba wuya πŸ‘ŒπŸ½matuqar ka jajirce kafi qarfin zuciyarka,Allah ta bamu iko ameen)_* ''wa alaikumus salam''ta fada asanyaye shiru ya dan ratsa tsakani kadan ''da alamu baki ji dadin jina da kika yi ba ko maryamu?,hala ma kin manta da ni?'' ''ko daya,ban kuma mance da kai ba'' ''da fari kafin nace momai maryam,nasan bani da kalmomin da zasu gamsar da ke gurin ban haquri,amma duk da haka ina roqarki don Allah don annabi ki yafemin,ba da gangan abinda ya faru tsakaninmu ya faru ba,bada sani na bane maryam,ki yafewa jabir masoyinki'' tausayinshi ya kamata ta dan kumshe idonta kadan ta bude ''kada ka bata bakinka gurin bani haquri jabir,tuntuni gaskiya ta dade da yin halinta,anyi walqiya komai ya bayyana'' yaja dogin numfashi kana ya sauke ajiyar zuciya ''alhamdulillahi rabbil aalamin,dukkan godiya ta tabbata ga Allah,babu shakka ke din jaruma kuma nagartacciyar masoyiya ce,bana tantama zaki zama mace ta gari uwa ta gari gurin 'ya'yanta,bazanyi nauyin baki ba ba kuma zanyi qauro ba maryam inason ki bani damar fitowa neman aurenki karo na biyu,tare da cikakken fatsn babu wani da ya sha gabana'' sai da gabanta ya fadi,tayi shiru tana son daidaita bugun zuciyarta sannan daga bisani tace ''qaddara ta riga fata jabir,Allah ya qaddara run da dama ni ba matarka bace,hakaza matar mutum kabarinsa,bai wuce sati biyu da kawo kudin aure na da wani ba'' ''la haula wala quwwata illah billah''ita ya dinga maimaitawa tsawon mintina biyar ''yanzu kina nufi maryam na rasa ki kenan,zaki auri wani na?,ki bani dama maryam mai rabo shi zaya samu tunda har yanzu ba'a daura aurenku ba balle kice kin haramta a waje na'' ''kai mai sani ne jabir bakin gwargwado,ka sani cewa nema akan nema haramunne,baya ga haka ma daga ni har kai babu wanda aka bawa qudirar rubuta kundin qaddararsa da kansa,kuma buwayin sarkin dake rubuta msna din mai dumbin adalci ne,babu yadda za'ayi ya rubuta mana abinda zai zama zalunci ne a garemu'' ''haka ne maryam,alhndlh Ala kulli hal,na gode maryam,na gode matuqa da gaske,bazan taba iya mantawa dake cikin kundin rayuwata ba,na barki lafiya'' tafi minti biyar riqe da wayar ra kasa ajjiyeta,tausayin jabir dinne kadai ke dawainiya da ita,babu shakka bazata iya manta dumbin alkhairansa gareta ba,koda ta tashi sallar dare bata mantashi cikin addu'o'inta ba,ta roqa masa alkhairi

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138