Skip to content

Chapter 38

Chapter 38

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,286 words 0 views Progress saved
Download Book

sauri hadizan ta kaiwa bakin kamilar dula kin zata mata tonon silili cikin jama'a ''don ubwnki sharri zakimin'' ''ba wani sharri wlh gaskiya ce da bakina sai a hanani fadan gaskiya ta...'' binta ce ta atse cece kucen ta fito dakin,inna hadizan hannunta dauke da wayar jamilan wadda ta tasamma dubu dari biyu da hamsin tana ta digar ruwa ''kinga aikin da kulu ta miki''ta fada tana miqa mata wayar hannu jamia ta dora aka ta kurma ihu tana fadin kulu ta kasheta,ita kadai ce ta rage mata kadara shine don baqar zuciya zata tsoma mata ita a ruwa wallahi to ba zata yarda ba kukan kura tayi ta banka dakin nasu da gugu inna hadizar tabi bayanta tana fadib kada ta nakasta mata yarinya amma ina kota kan uwar bata bi ba tsaki hindatu taja tana fadin ''jarababbu,ku kashe kanku dai'' naira talatin talatin suka biya zuwa caffe din dake qasansu,su taradda gun cike da dalibai masu duba jarabawarsu,hakan ne ya dan janyo musu jinkiri,sai da suka jira har kusan shida sannan suka samu sarari,babu jimawa aka gano result din hindatu,ba ita mai jarrabawar ba hatta maryam tayi farinciki ainun,don makin hindatun ya kai dari biyu da biyar,sai da ta rakata ta samu ota sanna itama ta tari tata ta wuce gidan 🍂🍃🍂🍃🍂🍃 kamar yadda layukan suke shiru gidan shima yake shiru lokacin da ta isa tana shirin shiga ita kuma na shirin fita kunnenta maqale da waya,cikin dinkin fitted gown take na material ruwan zuma,dan siririn dankwalin kawai ta nade wuyanta da shi,ganin ta nufota gadan gadan yasa tayi hanzarin matsawa gefe dob ta lura idab batayi hakan ba tsaf zata bangajeta ne ta wuce,saddiqa ce uwar girman kai da dagawa,duk da hakan bata tsira ba sai data yi mata kallon biyi babu taja tsaki bayan ta cire wayar a kunnenta sanna ta wuce su biyun kuma na kwance cikin kujerun falon wato abida da salma kowa na sabgar gabanshi,abida na charting salma na danne dannen laptop da bata san me tak yi ba,sai t v plasma din falon dake ta zuba aiki babu mai kallonta,babu wadda ta amsa sallamarta cikinsu,bata damu ba sam don ba yau ta soma ganin hakan ba,har zata wuce daki sai ta jiyo motsi cikin kitchen din haka ta sauya akalar tafiyar tata can,baba uwani ce ke wanke kwanuka,ta qaraso kitchen din dafe da bakinta ''ayyah,baaba uwani ayimin afuwa na barki da wahala jiya da yau''murmushi tayi tana taunar goro ''haba 'yar nan ai an zam daya babu komai,ke dai ya kika barosu?'' ''lafiya baaba suna gaidake''ta amsa mata tana karbe soson wanke wanken ''to madala muna amsawa,inace yanzu kika shigo gidan?'' ''eh baaba'' ''to amma shine zaki wani,karbi wanke wabke,bani in qarasa kije ki huta ga kiran sallar magariba can anayi'' ''a'ah baaba,haba gaskiya bazan baki ba,ki huta kema nasan tun jiya kike dawainiya'' ''hmmm,wallahi ke dai bari 'yar nan,inda ace abdullahi ne sai ni sai hajiya aikin da sauqi,tofa ina wadan can marasa kunyar yaran kawai sun isa su saka ka gaji,ga daya ta dadu,wancan tace ita kaza za'a dafa min waccan tace kaza'' wani takaici ya kama marya ''kuma kika dafa baaba?'' ''to ya za'ayi meramu sai haquri'' ta ajjiye kwanon hannunta ''bana jurar raina babba baaba,babu wadda zaki sake dafawa komai saidai idan maami ta saka ki,duk mai buqatar wani abu ta shigo ta dafa ai itama tana da hannu'' sai da suka qarasa komai sannan suka bar kitchen din tare bayan baaban ta gaya mata mami na asibiti da azahar ta fita zuwa bayan isha'i zata dawo,yadda ta barsu a falin haka ta dawo ta taradda su babu wadda ta motsa don tayi salla tara saura ta fito din ta debi abincinta,zaunen dai suke duka su uku wannan karon kowacce taci ado,abida cikin matsatstsun riga da wando,salma cikin fitted gown,saddiqa kuwawata gown ce wadda bata da hannu duka saman qirjin a waje,mamaki ya cikata tamkar irin matan gidan nan dake tsammin dawowar mai gidansu a lokacib,babu tababa zaman jiran dawowar abdallah suke,takaici ya isheta kamar ta rufesu da duka,duk su suke jawowa abdallan ke daukar kansa on top,yake rage qimar mata,koma meye sune sila tasa kanta gaba zata wucesu dauke da plate din abincinta ''ke malama a bawa mutane abinci ko su zasuyi serving kansu?'' a nutse ta waiwayo ''su waye mutanen?''ta tambayi salma cikin gatse,amma da yake sam ba ganewa take ba sai tace ''mtseeww,gani kuwa kina kallona'' ''ayyah,to ai na dauka a qoshe kuke ko'' ta shige dining area din ta zuba mata ta ajjiye mata ''ni da kika raina sai nayi magana zaki zuban?''inji abida maryam ta dubi plate din hannunta ''sai kayi magana zansan kana so ai,ga wannan kici na zuba wani''ta fadi bayan ta ajjiye mata shi a gabanta,ba bata lokaci tasa qafarta ta shure shi take yayi dai dai a gun,wanda ba don tayi saurin ja da baya ba har a jikinta zai samu masauki ''lallai ne ba qaramun raini ne tsakanina da baqauyar yarinyar nan ba''cikin qanqanin lokaci ta yar da wayar hannun ta ta miqe tayo kanta,qyam ta tsaya hannayenta harde da qirjinta tana kallon abidan,qarasowarta dab da ita ta daga hannunta saidai kafin ta aiwatar da komai muryar mami ta karade falob ''kai,meye haka abida?''dolenta ta sauke hannun nta cikin hayaniya take fadin ''wallahi mami sai na hora yarinyar nan'' ''me ya hadaku kuma yau maryamu?,ban sanki da fad ba fa''hankali kwance ta gaya mata abinda ya faru,girgiza kai kawai mamin tayocikin takaici tace wuce amaryamu'' cike da takaici ta isa dakinta,tayi imani a lokacin da abidan ta taba jikinta ko siyar wace ce ita ba zata daga mata qafa ba,bata ga amfanin alkunya ga mutumin da baisan darajar dan adam ba,cikin ikon Allah abdul ya kirata,shi ya ebe mata kewa har bacci yayi awo gaba da ita 🍃🍂🍃🍂🍃 cikin bacci ta dinga jin yunwa na rage mata dadin baccin wadda ta tilastata farkawa,wayarta da ke gefan pillow dinta ta dauka ta duba lokaci,shabiyu da arba'in da takwas na dare,cikin mutuwar jiki da kasala ta sauko daga adon ta shiga toiket ta dauraye bakinta ta daura alwala ta fito ta tayar a sallah,raka'a hudu ta samu tayi tayi addu'oo'inta ta shafa a hankali ta bude qofar dakin nata ta fito don samawa kanta abinci a dining,tayi mamakin ganin qwayayen falon duka akunne,ganin laptop da waya kusa da ita yasa ta bayar salma ce qarshen tashi tabar falo a haka jingine yake da bango falon hannayenshi harde a qirjinshi,idanu kawai ya zuba mata fuskarsa qunshe da qaramin murmushi,yayin ita kuma take gaf da ahi har tana iya sheqar hucin nashi numfashin,hannayenta dafe da bangon kusa da kafadarshi ''fyaden kema zakimin?''ya tambayi salma kanshi tsaye,cikin lumshe idanu ta kada kai ''ko kadan,kawai ina da buqatar inji dumin jikinka ne,dubi kwalliyarnan duk kai na yiwa amma tun dazun nake jiran dawowarka,na hana idanuna bacci don kada ta tashi a tutar babu'' murmushinsa ya qaru fiye da na dazu,yasan kalma daya zaiyi amfani da ita wadda zata sata taji haushi ''sai ance mutum kaska ne yace shi bashi bane'' a maimakon yaga taji haushi kamar kullum sai yaga ko a jikinta,murmushi ta kuma yi ''to meye idan ma kaskar ce,duk akan sonka ne,nidai ko hugging dina ayi kawai na wuce dumin da naji

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138