Chapter 38
Chapter 38
sauri hadizan ta kaiwa bakin kamilar dula kin zata mata tonon silili cikin jama'a ''don ubwnki sharri zakimin'' ''ba wani sharri wlh gaskiya ce da bakina sai a hanani fadan gaskiya ta...'' binta ce ta atse cece kucen ta fito dakin,inna hadizan hannunta dauke da wayar jamilan wadda ta tasamma dubu dari biyu da hamsin tana ta digar ruwa ''kinga aikin da kulu ta miki''ta fada tana miqa mata wayar hannu jamia ta dora aka ta kurma ihu tana fadin kulu ta kasheta,ita kadai ce ta rage mata kadara shine don baqar zuciya zata tsoma mata ita a ruwa wallahi to ba zata yarda ba kukan kura tayi ta banka dakin nasu da gugu inna hadizar tabi bayanta tana fadib kada ta nakasta mata yarinya amma ina kota kan uwar bata bi ba tsaki hindatu taja tana fadin ''jarababbu,ku kashe kanku dai'' naira talatin talatin suka biya zuwa caffe din dake qasansu,su taradda gun cike da dalibai masu duba jarabawarsu,hakan ne ya dan janyo musu jinkiri,sai da suka jira har kusan shida sannan suka samu sarari,babu jimawa aka gano result din hindatu,ba ita mai jarrabawar ba hatta maryam tayi farinciki ainun,don makin hindatun ya kai dari biyu da biyar,sai da ta rakata ta samu ota sanna itama ta tari tata ta wuce gidan 🍂🍃🍂🍃🍂🍃 kamar yadda layukan suke shiru gidan shima yake shiru lokacin da ta isa tana shirin shiga ita kuma na shirin fita kunnenta maqale da waya,cikin dinkin fitted gown take na material ruwan zuma,dan siririn dankwalin kawai ta nade wuyanta da shi,ganin ta nufota gadan gadan yasa tayi hanzarin matsawa gefe dob ta lura idab batayi hakan ba tsaf zata bangajeta ne ta wuce,saddiqa ce uwar girman kai da dagawa,duk da hakan bata tsira ba sai data yi mata kallon biyi babu taja tsaki bayan ta cire wayar a kunnenta sanna ta wuce su biyun kuma na kwance cikin kujerun falon wato abida da salma kowa na sabgar gabanshi,abida na charting salma na danne dannen laptop da bata san me tak yi ba,sai t v plasma din falon dake ta zuba aiki babu mai kallonta,babu wadda ta amsa sallamarta cikinsu,bata damu ba sam don ba yau ta soma ganin hakan ba,har zata wuce daki sai ta jiyo motsi cikin kitchen din haka ta sauya akalar tafiyar tata can,baba uwani ce ke wanke kwanuka,ta qaraso kitchen din dafe da bakinta ''ayyah,baaba uwani ayimin afuwa na barki da wahala jiya da yau''murmushi tayi tana taunar goro ''haba 'yar nan ai an zam daya babu komai,ke dai ya kika barosu?'' ''lafiya baaba suna gaidake''ta amsa mata tana karbe soson wanke wanken ''to madala muna amsawa,inace yanzu kika shigo gidan?'' ''eh baaba'' ''to amma shine zaki wani,karbi wanke wabke,bani in qarasa kije ki huta ga kiran sallar magariba can anayi'' ''a'ah baaba,haba gaskiya bazan baki ba,ki huta kema nasan tun jiya kike dawainiya'' ''hmmm,wallahi ke dai bari 'yar nan,inda ace abdullahi ne sai ni sai hajiya aikin da sauqi,tofa ina wadan can marasa kunyar yaran kawai sun isa su saka ka gaji,ga daya ta dadu,wancan tace ita kaza za'a dafa min waccan tace kaza'' wani takaici ya kama marya ''kuma kika dafa baaba?'' ''to ya za'ayi meramu sai haquri'' ta ajjiye kwanon hannunta ''bana jurar raina babba baaba,babu wadda zaki sake dafawa komai saidai idan maami ta saka ki,duk mai buqatar wani abu ta shigo ta dafa ai itama tana da hannu'' sai da suka qarasa komai sannan suka bar kitchen din tare bayan baaban ta gaya mata mami na asibiti da azahar ta fita zuwa bayan isha'i zata dawo,yadda ta barsu a falin haka ta dawo ta taradda su babu wadda ta motsa don tayi salla tara saura ta fito din ta debi abincinta,zaunen dai suke duka su uku wannan karon kowacce taci ado,abida cikin matsatstsun riga da wando,salma cikin fitted gown,saddiqa kuwawata gown ce wadda bata da hannu duka saman qirjin a waje,mamaki ya cikata tamkar irin matan gidan nan dake tsammin dawowar mai gidansu a lokacib,babu tababa zaman jiran dawowar abdallah suke,takaici ya isheta kamar ta rufesu da duka,duk su suke jawowa abdallan ke daukar kansa on top,yake rage qimar mata,koma meye sune sila tasa kanta gaba zata wucesu dauke da plate din abincinta ''ke malama a bawa mutane abinci ko su zasuyi serving kansu?'' a nutse ta waiwayo ''su waye mutanen?''ta tambayi salma cikin gatse,amma da yake sam ba ganewa take ba sai tace ''mtseeww,gani kuwa kina kallona'' ''ayyah,to ai na dauka a qoshe kuke ko'' ta shige dining area din ta zuba mata ta ajjiye mata ''ni da kika raina sai nayi magana zaki zuban?''inji abida maryam ta dubi plate din hannunta ''sai kayi magana zansan kana so ai,ga wannan kici na zuba wani''ta fadi bayan ta ajjiye mata shi a gabanta,ba bata lokaci tasa qafarta ta shure shi take yayi dai dai a gun,wanda ba don tayi saurin ja da baya ba har a jikinta zai samu masauki ''lallai ne ba qaramun raini ne tsakanina da baqauyar yarinyar nan ba''cikin qanqanin lokaci ta yar da wayar hannun ta ta miqe tayo kanta,qyam ta tsaya hannayenta harde da qirjinta tana kallon abidan,qarasowarta dab da ita ta daga hannunta saidai kafin ta aiwatar da komai muryar mami ta karade falob ''kai,meye haka abida?''dolenta ta sauke hannun nta cikin hayaniya take fadin ''wallahi mami sai na hora yarinyar nan'' ''me ya hadaku kuma yau maryamu?,ban sanki da fad ba fa''hankali kwance ta gaya mata abinda ya faru,girgiza kai kawai mamin tayocikin takaici tace wuce amaryamu'' cike da takaici ta isa dakinta,tayi imani a lokacin da abidan ta taba jikinta ko siyar wace ce ita ba zata daga mata qafa ba,bata ga amfanin alkunya ga mutumin da baisan darajar dan adam ba,cikin ikon Allah abdul ya kirata,shi ya ebe mata kewa har bacci yayi awo gaba da ita 🍃🍂🍃🍂🍃 cikin bacci ta dinga jin yunwa na rage mata dadin baccin wadda ta tilastata farkawa,wayarta da ke gefan pillow dinta ta dauka ta duba lokaci,shabiyu da arba'in da takwas na dare,cikin mutuwar jiki da kasala ta sauko daga adon ta shiga toiket ta dauraye bakinta ta daura alwala ta fito ta tayar a sallah,raka'a hudu ta samu tayi tayi addu'oo'inta ta shafa a hankali ta bude qofar dakin nata ta fito don samawa kanta abinci a dining,tayi mamakin ganin qwayayen falon duka akunne,ganin laptop da waya kusa da ita yasa ta bayar salma ce qarshen tashi tabar falo a haka jingine yake da bango falon hannayenshi harde a qirjinshi,idanu kawai ya zuba mata fuskarsa qunshe da qaramin murmushi,yayin ita kuma take gaf da ahi har tana iya sheqar hucin nashi numfashin,hannayenta dafe da bangon kusa da kafadarshi ''fyaden kema zakimin?''ya tambayi salma kanshi tsaye,cikin lumshe idanu ta kada kai ''ko kadan,kawai ina da buqatar inji dumin jikinka ne,dubi kwalliyarnan duk kai na yiwa amma tun dazun nake jiran dawowarka,na hana idanuna bacci don kada ta tashi a tutar babu'' murmushinsa ya qaru fiye da na dazu,yasan kalma daya zaiyi amfani da ita wadda zata sata taji haushi ''sai ance mutum kaska ne yace shi bashi bane'' a maimakon yaga taji haushi kamar kullum sai yaga ko a jikinta,murmushi ta kuma yi ''to meye idan ma kaskar ce,duk akan sonka ne,nidai ko hugging dina ayi kawai na wuce dumin da naji
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138