Chapter 13
Chapter 13
ne suka wawashe ragowar shekarun suka boyesu sanye take da swiss lace ruwan toka da adon orange,sai labcoat da ta dora fara tas a sama,takalmin qafarta hill ne shima fari ne qaf kamar ranar ta fara sashi,ta nade wuyanta da mayafi orange,fuskarta qunshe da yalwataccen murmushi ''sannu hajiya,maimakon ku shigo sai kuma ku zauna anan,ku taso don Allah''ta fada tana nuna masu qofar,gaba tayi suka bita abaya abun mamaki sai gasu a wani gurin,guri ne mai kama da gurin shan iska,saidai dauke yake da tyles fari qal illa tsakiyar gurin da aka yiwa shafe din cycle aka cika shi da 'yan shuke shuke masu furanni dake fidda qamshi qofa ce ta glass wanda na waje baya iya ganin na ciki bayan sun shiga ciki ta fahimci hakan,falo ne shima mai dauke da kujeru set biyu,gini ne sama da qasa wato mai bene,wanda matattakalar na acikin falon,tsarinshi abun sha'awa ne matuqa duk iya iya tsarinka sai ya burge ka,komai na cikin falon fari ne da milk,babu alamun qura ko dauda a tattare da shi sai kace yanzu aka bare komai aledarsa aka sanya ''bismillah''hajiya bintu tace musu tana shirin zama ''hajiya ga maryam na kawo miki,kuma bani da haufi a kanta,ke kanki,nasan zaki ji dadin aiki da maryam insha Allahu''haj atika ta fada bayan sun gama gaisawa murmushi ta sake yi ''ina fatan haka,maryam sannu,ina fata hajiya ta gaya miki komai,girki ne kadai nake so ki dinga yiwa yaro na,kada kiji a ranki cewa wai aiki kika zo,kisa aranki taimako na kika zo yi,ki dauki kanki tamkar diyata,domin dama ina cike da kewar rashin yarinya mace,to ina ji a raina yau Allah ya bani,abu daya kawai nake buqata daga gareki,ki riqe amana don Allah,ki kula ki kuma yi taka tsantsan da abincin yarona,nasan kinsan komai game da abubuwan da ya faru a kanshi,ina son *abdallah* don Allah ki kula min da shi,na rasa babanshi bana son in rasa shi''ta qarashe maganar muryarta na bayyana raunin da zuciyarta tayi duk sai taji tausayin su ya kamata,sai take jin ina ma ita ta samu wanna gatan,ina ma ita ke da gata har kamar haka ''insha Allahu haj na miki alqawarin ba zaki samu wani abu mai kama da cin amana ba daga gareni'' hakan data fada dukansu yayi masu dadi har haj bintan na murmusawa ''idan kika min haka kuwa maryam kin gama min komaibani da abinda,zan saka miki da shi,gyara guda daya,indai kina son insinga jinki kamar diyar tawa da gaske to kada ki sake kira na hajiya,ki kirani da *mami* kamar yadda *Abdallah na* ke kirana'' sai a lokacin maryam tayi murmushi karo na farko,harga Allah taji dadin karramawar da tayi mata''to,mami'' ''yauwa,na gode,hajiya atika na gode qwarai da gaske,bazan iya manta wannan taimakon da kika yimin ba'' ''babu komai haj bintu,ai abdallah kamar da yake a gurina,ni zan wuce,maryam.....'' hajiyan ta fada tana miqewa har waiting parlour haj bintu ta taka mata sannan ta dawo,da murmuahin dai nata ta dubi maryam ''taso,maryam na nuna miki daki,don fita zanyi asibiti ina da C S har mutum uku,Allah ne ma yayi ba zamu samu sabani ba''ta gaya mata lokacin da tayo gaba ta bita abaya,wani labule mai kyawun tsari ta daga daga sashen hagu na falon,saiga gajeran corridor ya bayyana,dakuna uku ne a gun,ta tura daki na uku ya bude tace ''bismillah maryam,ga dakinki,ni,zan fita ki zauna ki huta kafin na dawo mu shirya yadda lamuran zasu kasance,yau dai babu aiki,don Abdallan ma baya gari,amma gobe zai dawo'' ''to,mami sai kin dawo''ta fada cikin girmamawa tabi dakin da kallo bayan mami ta fita,daki ne wadatacce shimfide da carfet mai taushi,sai gado cupboard ta jikin bando da madubi hadi da dressing chair,curtains,dukkaninsu pink da fari,cikin dakin akwai toilet,sai a c daura da window din jikin gado,gefan gadon ta ajjiye kayanta sannan ta shiga toilet din ta dauro alwala ta gabatar da sallar la'asar sannan ta soma jera kayanta cikin sif din sama sama take jiyo sallama a falon,ta miqe ta maida hijab dinta tayo hanyar falon,budurwar da suka gani ce dazu tsaye tana kalle kalle ''sannu''maryam tace da ita don jawo hankalinta ta fuskanci ta fito a dage ta kalleta ''ina mamiοΌ'' ''ta fita aiki'' bata tanka mata ba ta juya ta fice itama maryam ta juya ta koma dakinta *mrs muhammad ce*π πππβπ»βπ»βπ» [9/17, 12:51 PM] 80k: πππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊπΊ πππππππ πΊππΊππΊ πΊππΊπ πΊππΊ πΊπ π πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πππππππ *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πΊππΊππΊππΊ ππΊππΊππΊ ππΊππΊπ ππΊππΊ πΊππΊ πΊπ πΊ βΆ1β£2β£ Har gefin magariba tana gyaran kayanta cikin drower din,dakin tsaf yake don haka bashi buqatar wani sabon gyaran na daban,ta maida qofofin cupboard din ta rufe dai dai lokacin ta jiyo kiran sallah sama sama saboda haka ta shige toilet har isha'i tana kan abun sallarta,sai da ta bada faralin isha'in sannan ta nannade ta,zaman shirun ya mata yawa,sai kewar gida ta soma damunta,ta jawo wayarta ta lalubu number din hindatu ta kira,ba bata lokaci ta daga ''wayyo ya maryam dita,i missed you wlh wuni guda kawai'' ta gatsine fuska tamkar tana gabanta ''hmmmm,ba wani nan,kinyi missing din nawa kika gaza kira na sai da ni na nemeki'' ''ayyah anty na,kinsan dai halin student,wayan,ba credit,am sorry ya maryam'' ''shikenan,ya gidan ina mama ta'' ''gata kusa da ni bari in bata'' kusan minti goma suna hira har aka fara mata warning kudinta sun kusa qarewa sannan sukayi sallama toilet ta koma ta hada ruwan dumi tayi wanka ssnnan ta sauya doguwar rigarta mai kauri ta bacci ta dora hijab,tsna maida kayan da suka fadl daga cikin sif din ta jiyo sallaman mami kan kujerar falon ta taddata a zaune tana cire agogon hannunta ''sannu da dawowa mami''cikin fara'ar nan dai tata tace ''yauwa maryama,ya baqunta,na barki ke daya ko,gurin nawa ba yara ni daya ce,gun haj laura kuma basu sanki ba bare ki shiga,sannan na manta ban nuna miki kitchen ba,ina fata yunwa bata takura ki ba'' murmushin itama tayi ''banjin yunwa ma mami'' ''a'ah,ban yarda ba,bari na shirya na fito saiki dafa mana wani abun mai sauqi'' ''to mami'' miqewa tayi tana nuna mata jakar da ta shigo da ita ''taimaka ki shigo min da brief case din nan''inji mamin ta haura sama maryam din ta bita a baya tana mamakin sauqin kai irin na mamin,tamkar ita ba wata bace,tsabar sanin qima irin ta dan adam saman ma wata duniyar ce,komai nashi fari ne tun daga parlour har bedroom din mamin sai dan ratsin baqi kafan wanda bai taka kara ya karya ba ''hmmm,wani aikin sai likitoci''maryam ta fadi a zuciyarta a falon qasan suka sake zama bayan sun kammala cin abincin daren ''gaskiya maryama my son zai morewa girkinki,haka kija iya abinci''a kunya ce tayi mata murmushi cikin seriouse tone tace ''maryam kamar yadda na fadi miki dazu inason Abdallah so na haqiqa saboda shi kadai Allah ya mallakamin,cikin irin abinciccikan da Abdallah keso akwai irin namu na gargajiya,sannan yanason kayan snacks,aikinki zai kasance ne ranar weekend zaki dinga breakfast lunch da dinner,amma ragowan kwanakin breakfast ne kawai sai dinner,amma idan ke kina da buqatar ci zaki iya dafawa,saidai majority idan da wuri abdallah zai fita yana tafiya ne da breakfast dinshi sannan anan zaki dinga shirya masa saman dining dina anan yake karyawa,ina fata nima za'a dinga
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138