Skip to content

Chapter 74

Chapter 74

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,286 words 0 views Progress saved
Download Book

wuron tayi qoqarin yi amma ta qiya,don tsakanin kwana ukun da sukayi cikin gidan indai ta kunna risho to abdallah zata dafawa wani abu,ta riga ta saba don rayuwar gidan sun data tashi cikinta marabarta kadan ce da wannan Mero ce tayi sallama ta shigo gidan,ta dubi maryam tace ''takwara ina kwana''ta waiwayo fuskarta dauke da 'yar fara'a ta amsa mata ''a'ah,mero,yanzu kuma sammako zuwa min aka koya kenan,kodon,kinga kin samu abokiyar hira ne?''inji inna wuro dake fitowa daga daki dariya tayi ''wallahi kuwa inna,na samu larabawa abokan hira''haka take kiransu maryam sabida farin da suke da shi,duk da itama din farar bafulatana ce saidai nata farin baikai nasun ba Ta shiga dakin inna wuro da suke zaune da mero,suna hira suna cin gyada marau marau,gefansu ta samu ta zauna kana tace da inna ''inna don Allah ina zan samu ganyan magarya?'' ''ganyan magarya me zakiyi da shi?'' ta danyi murmushi,a zaton innan ko maganin mu na mata takeson ta hada ''akwai cikin kayan malam,amma ina tsammanin busashshiya ce,idan danya kike so saidai ko a yago miki can qofar gidan malam haladu'' ''sai nasa yara su ciro miki,yaya abdullahi zakiyiwa magani?''inji mero wadda ta cafe zancan,kallonta maryam din tayi,ta lura da yadda take yawan kulawa da duk wani lamari da ya shafesu hakan yasa ta dan saki jikinta da ita ''eh''maryam tace mata,take ta miqe tana jawo hijabinta tana yafawa ''bari na kawo miki''ta fada tana ficewa,mero sunanta maryam,tsirar gidaje biyu ne kawai tsakaninsu da gidan inna wuro,irin marasa shi din nan ne na azo a gani,hakan ya sanya hatta aurenta iyayenta suka kasa,hakan ya sanya take shigowa take taya inna wuro aikace aikacen gida,taci kuma na rana da dare wani lokaci harda na safe agidan bayan wanda tsoho malam yasa ake zubawa akai gidan naau sabida iyayenta da qannenta zama tayi suka ci gaba da hira da inna wuron bayan ta mata tayin gyadar,cikin minti goma saiga mero da ganyan kore shar mai yawa kuwa,maryam ta miqe tana mata sannu ta saka hannu zata karba ''bari na kai miki dakin ma''kafin tace wani abu har ta fice ta nufi dakin nasu,binta tayi da kallo har ta dagaabulen dakin ta shiga,duk da ta koma ta zauna amma sai hankalinta ya kasu jiyi ganin ahiru meron bata fito ba,miqewa tayi taa cewa inna wuro ''bari na daura alwala naga an kusa azahar inna'' ''to...to,nima tashin zanyi''. sai data daura alwalar sannan ta nufi dakin,kan kujerar dakin ta tadda meron tana faman zuba surutu idonta kan abdalladake kwance,abdallah na daga kwancen yana kallonta qarasa shigowa tayi ''kin manta bai da lafiya ne,mara lafiya baison surutu''ta fada tana qarasawa kan katifar ''amma meramu har mirmushi ya yimin fa''sai taji wani dim,ta waiga ta kalli abdallah,idanunshi na alaumshe sabanin dazun da yake tar a bude. sauka tayi kawai ta janyo,abun salla ta shimfida sannan ta kalli mero ''ya kamata kije kiyi sallah ko,don lokaci yayi'' ''shi kuma abdullahin fa?'' ''zaiyi shima''ta bata amsa tana tada kanbbarar sallah,sai data kusa raka'a uku kafin meron ta tashi ta fita tana yiwa abdallah sallama roba ta saka ta masa alwala sanna ta juyar dashi bangaren gabas,kafin ya idar ta zuba abinci cikin plate ta ajjiye,bayan ya gama ta dora mishi kan,fillow a saman cinyanshi don hisham yace a dinga barinshi wani lokaci ya dinga ci da kanshi don hannun ya dinga motsawa ya dinga jin qwarinshi sosai,ta koma saman kujera ta ta samu roba daya ta zuba ganyan magaryan tana gyarashi tare da cire qayoyin jiki shirun da taji alamun bai fara ci ba ya sanyata dago kanta,hada idanu sukayi da sauri ta janye idonta,ta rasa dalilin da a kwanakin nan bata iya hada ido da shi na tsawon lokaci,jikinta yaci gaba da bata kallonta yake,a sace ta kuma daga kai zata saci kallonshi suka sake hada ido,ya lumshe idon nashi da sauri ya bude,sign ne da ta lura yana yawan yi mata amfani da shi idan suka hada ido,batasan me yake nufi ba saidai a duk lokacin da yayi hakan takan tsinci kanta cikin wani irin feelings,wani irin abu ne cikin qwayar idanun abdallan da bata taba ganinshi cikin idanun wani ba ta janye idonta tana fadin ''kaci abinci kada ya huce''kai ya girgiza mata alamun a'a,babu yadda bata masa ba amma yaqi,qarahe sai daya bar abinda take yi din ta dawo kan katifar ta karbi plate din,ta debo ta miqa mishi,babu musu ya bude bakinshi ya karba yana kallon fuskarta,ganin ya karba sai ta ajjiye cokalin tana fadin ''bismillah to''tana maida fuskarta gefe a tausashe taji an kamo habarta ana qoqarin juyo da fuskarta,qin kallonshi tayi kamar yadda shima sam ya hanata sakewa har sai da suka sake hada ido,ture plate din abincin yayi da hannunshi guda kana ya jawota ta fada jikinshi. tayi ta qoqarin tashi,saidai ya hanata,har mamakin yadda ya iya riqeta haka tayi,kamar zata yi kuka tace ''abdallah,bafa mu kadai bane cikin gidan nan ka sani''shiru taji,alamun bazai kulata ba,tilas ta haqura da yunqurin tashin tayi luf cikin jikinshi,ya lalubi hanninta ya saka nashi ciki ya jade yatsunsu guri guda tare da sauke ajiyar zuciya wadda ta haddasa mata sauyawar yanayin jikinta gaba daya,ta runtse ido tana jin fitar numfashinshi. *_kuyi haquri da wannan_* *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽 [1:55pm, 9/24/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 💖🌺💖🌺 💖🌺💖 🌺💖 💖 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺💖🌺💖🌺💖 🌺💖🌺💖 🌺💖🌺 💖🌺 💖 © *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *_home of expert and perfect writers_* 4⃣6⃣ *_Annabi Muhammad S A W yace:duk wanda yaje gurin boka ko dan duba haqiqa ya kafircewa abinda annabi muhammad tazo da shi,hakanan ba za'a karbi sallarsa ta kwana arba'in ba(ba yafe masa su akayi ba,kuma ko yayi Allah baya buqata baxai karba ba,babu wani abu da zaka/ki aikata ya zama kaffarar wannan zunubin da kikayi face ki tubarwar Allah tuba na haqiqa ba tuban muzuru ba,kuma kada ki yarda qafarki ta sake kusantar gurin bama zuwan ba,shin me kike tsammani idan Allah ya dauki ranki a gun ko a hanyar zuwa kota dawowa?,Allah ya kare mana imsninmu,ya,cire mana dukkan wani qulli dake zuciyoyinmu game da 'yan uwanmu musulmi)_* *_Manzan Allah S A W yana cewa''ka tuna Allah lokacin da kake cikin jin dadi da yalwa,shi kuma sai ya tuna da kai lokacin da ka shiga qunci da matsi da wahala(ba wai ka xauna kara zube ba don kana cikin jin dadi da wadatar rayuwa,ba zaka tashi addu'a ko tuna Allah da girma yake ba sai bala'i da masifu sun maka katutu,wannan kuskure ne babba,Allah yana fushi da bawan da baya roqarsa haka annsbi S A W yace mana,Allah kasa mu dace)_* Saukar numfashinsa ne ya alamta mata bacci ya daukeshi,ta zare jikinta cikin dabara ta maye gurin da fillow,fuskarshi tarwai,kyawunshin nan mai daukar hankali yana nan,ta zuba masa ido tana tuhumar kanta na wasu 'yan lokuta,ta janye idonta ta lumshesu hadi da sakin ajiyar zuciya,mero ta fado mata arai,sai ta ja siririn tsaki kana ta sauka daga katifar,hijabinta na kanta don haka abun sallah kawai ta gyara ta zauna akai bayan bayan ta samu roba daban ta saka ganyen magaryar qwalli bakwai aciki,a nutse tayi bismillah cikin madaidaiciyar murya ta soma karanta suratul baqara cikin robar da ta zuba ganyan magaryar da ruwa aciki,da ka take karatun cikin daddadan

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138