Skip to content

Chapter 105

Chapter 105

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,279 words 0 views Progress saved
Download Book

kallo,wani kyau baccin yayi masa sosai kamar ba mai bacci ba. Ta riga ta yarda kyau kam Allah ya bawa abdallah shi,irin kyawun da ba kowa Allah ke azurtawa da shi ba kusan awanni daya da rabi ya samu yana baccinshi tana zaune tamkar mai gadinsa duk motsinsa na kan idanunta,a haka taji an soma knockong qofar,ta fara qoqarin tureshi daga jikinta jin muryar mami ne amma qememe yaqi,tamkar ma yana sane sai ya sake kanannadeta abinsa yaci gaba da baccinsa,a hankali mamin ta murda qofar jinta abude yasa ta dan turo kadan tana sallama,amsa mata maryan tayi sai ta leqo da kanta,karo na biyu ta soma yunqurin maida shi gefe ta kasa cikin jin kunya,murmushi mamin ta mata kana ta mata alamar tayi shiru ta zauna kada ta tasheshi ta ja qofar ga rufe musu,ta sake kallon fuskarsa gumi taga yanayi duk da sanyin rabar dake dakin,tattausan tafin hannunta ta saka tana share masa tare da hura masa iskar bakinta,caraf taji an kama hannun naga an riqe,tsoro da kunya suka kamata sai tayi wuri wuri da ido,ya bude idonsa a hankali ya sumbaci hannun kana ya tashi zaune yana ambaton ''la'ilaha illal lah muhammadurrasululluh sallallahu alaihi wa sallam'' yana miqa ya dubeta tana qoqarin miqewa yace mata ''sannu baby am sorry na danne miki cinya ko''bata ce komai ba tana qoqarin fita cikin zafin nama ya rigata isa bakin qofar ya saka key ya qulle,ta kalleshi cikin alamu na tambaya kafin ta furta tambayar ma ya bata amsar ''babu inda zaki je,idan kinga kin bar dakin nan nazo tafiya ne''sai ta bata fuska kana tace ''to waishin ma ni matarka ce?,bayan kace temporary ne'' girarsa ya dage kana yace''yes har yau matata ce ke,dole kici gaba da yimin abinda nakeso kafin lokacin da maryara zata iso''kasa magana tayi shi kuma ya zare key din ya jefa aljihun three quater dinsa ''daga tashina a bacci kinsani magana my mero'',jin ya ambaci sunan meron ua sake hasalata ''ai ba meron bace,sabida haka kada ka sake kira mana sunanta,kayi qoqari mu rabu lpy''shikam da yar qaramar dariyarsa ciki ciki ya zari towel dake saqale kan murfin cupboard ya shige toilet A darare take zaune gefan gado tana bin dakin da kallo a haka ya fito ya sameta,da sauri ta dauke kanta don yaune karo na farko data taba ganinsa haka,rigar wankan jikinsa ya kunce zaren dake riqe da ita ta fadi a gun ya zama daga shi sai gajeran wando,cikin qunquni tace ''nikam naqi jinin rashin kunya'' a hankali ya tako gabanta ya durquso inda take a zaune har tana jin qamshin sabulun wankanshi da ragowar dumin dumin ruwan da yayi amfani da shi ''me kike fada?''ya tambayeta da wata iriyar murya ta daban,baya ta dan ja tana sake tsuke fuska don kusancin nasu yayi yawa ''nikam babu abinda nace''dagowa yayi yana dariya ''da kin sake kin maimaita yarinya yau da kinga yadda ake ruwan rashin kunya,yau da saidai mami tayi jinyarki ni kuwa na gudu abuja kinga ko fada ba zata samu damar yi min ba''sarai ta fuskanci me yake nufi,wai gabuntar dan fari ke damun Abdallah ko tabarar auta?,ta rasa wanne ne daga ciki,sai kuma ta tuna cewa itama 'yar farin ce take ta bawa kanta amsar saidai tabara ce kawai irin ta auta. Babu wanda ya sake cewa dan uwansa komai har ya kammala shiryawa,itakam sai dauke kanta kawai tayi wani sashen don harkarsa yake kamar shi daya ne cikin dakin,wannan karon ma t.shirt din ya sanya saidai baqa ce long sleeve haka ma three quater dinashi baqine,wani kyau suka yiwa farar fatarsa,ya fesa turarrurrukansa,ga tunaninta ta dauka zai bude musu qofa ne su fice sai taga ya soma sauko da wasu tsadaddun akwatuna baqaqe masu kyau qana nan set ne guda uku ya ciro biyu babban da qaraminsu ya ajjiyesu ''bismillah madam,a hadamin kayan tafiya''ya fada yana dauki pillow daga saman gado ya jefar a saman rugs din dakin ya kwanta rub da ciki yana kallonta ''ammafa mami tazo nemanmu dazun kana bacci'',girarsa ya dage ''ba matsala nasqn ba wata damuwa bace indai mami ce,bamu da damuwa da ita'' qi tayi duk don ua qyaketa ta fita hakan yasa ya janyo wayarsa ya kira mamin ya tambayeta ''a'ah,ba wani abu ne,dama baqi ne suka zo matan baffa salisu ne kuma sun tadda kana bacci,har mun gaisa ma sun wuce sauri suke suna zasu'' ''ok mami''ya fada ya katse wayar yana duban qwayar idonta ''sarkin kuka,komai kuka komai kuka,bayan qiri qiri baki da gaskiya''ya fada cikin zuciyarsa yana murmushi,bai ce mata komai ba har ta gaji da kallon da yake mata ta miqe ta isa ma'ajiyar kayanshin don yanzu kuma bata da wata dabarar ta kubce masa. Tsaye tayi a gun,ta rasa ma wanne zata dauka masa,kaya ne bila'adadin iya ganinta,a sanyaye tace ''wanne da wanne zan dauka maka'' ''na baki zabi,nikam,bani da ta cewa''ya fada yanajin dadin yanayin da suke,ji yake kamar ya riqe lokaci suyita zama a haka,a hankali ta dinga zaban kayan tana shiryawa cikin akwatin,tsit dakin yayi lokacin da take aikin,duk wani kotsinta yana binta da ido don,ba qaramin burgeshi take ba,komanta cikin nutsuwa,ta gama da suite suite ta saka masa yadi biyu shadda biyu tunda tasan tafiyar tasa majority sai yafi amfani da suite din,sannan ta saka masa na shan iska,ta kammala ta rufe qaramin kuma ta saka masa sauran tarkace na buqatar yau da gobe,shi kansa yanayin yadda ta tsara masa kayan ya burgeshi qwarai,komai a tsari,ta gama shima ta zuge tana fadin ''an gama'',sai da ya lumshe idonsa ya bude kana yace ''thank you verry much,shukran jazilan'' ya tashi ya zauna soasai yana fadin ''bari na qarasa daya nau'in godiyar ko''kafin tace komai ya jawota jikinsa,irin saqonnin dazu ya fara aika mata har suka so sufi na dazun zafi,nauyin da saqon nasa ya mata ya sata sakin kuka amma bai fasa ba don yana jin shine hanya daya data rage masa na samun sauqin abinda yake ji cikin zuciya da gangar jikinsa. Kukan wayarsa ne ya ceceta,da qyar ya iya miqa hannu ya dauka,sunan mami ya gani na yawo ya daga kana yayi shiru ''abdallah,maryam tayi baquwa fa''bazai iya magana ba don yasan da yayi din tana iya harbo jirginsa don haka yace ''uhmmmmm''tuni ma ita ta kashe bata jirayi amsar sa ba,ya dubi maryam da ta dunqulr guri guda,duk da abinda yake ji sai da ta bashi dariya,sai kace wanda yake shirin yin mai gaba dayan duka ta wani tsure ''raguwa kawai,abinda baikai ya kawo ba kin gaza daukeshi''ya fada yana miqewa itakam ko daga kai ta kalleshi bata iyawa saboda azabar kunya haushi da tsoro ya fito yana tsane jikinsa har yau tana nan inda ya barta,wayarta itama ta dauki tsuwwa da sauri ta daga hindatu ce ke kiranta ''adda maryam,jiran kusan minti arba'in'' tayi qoqarin daidaita muryarta saidai duk da haka a sanyaye take ''gani nan hindatu''ta kashe wayar ta miqe tana daidaita kanta Sai data juya baya kana tace cikin cool voice ''bani key din zan fita ana jirana'' ''dubeki,a hakan zaki fita,shiga toilet kiyi wanka'' ido ta zazzaro duk da bata kallonshi,kamar yasan zaro idon tayi kuwa yace ''eh,ko ba zakiyi ba kije ki daura alwala muyi salla azahar tayi mu samu ladan jam'i nasan yanzu masallaci

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138