Skip to content

Chapter 36

Chapter 36

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,288 words 0 views Progress saved
Download Book

tana ci gaba da dame gadon aikin da maryam din ta saki ''a'ah,maryamu kin gaji ne,idan ba dama sai na aika hindatu ta kiramin laure ta tayamu'' girgiza kanta tayi alamun a'a ''mama haka abu ya faru da jamila kuma dai?'' ''uwar asugwi din ta fesa miki din kenan ko''maman ta fada tana qarasowa cikin dakin,ta kama kunnen hindatu ta dan murde har sai da ta saki aiririyar qara tana dafe hannun maman ''don Allah mama kunne na,zaki tsinke kunnen autar taki fa ki rage mata kudin sadaki'' ''ai gwara in tsinke kunnen tunda ya iya jiyo gulma ya fadawa addarshi'' da qyar hindatu ta zame a hannun maman jikinta babu qwari haka suka dinga aikin,har ga Allah bata ji dadin mutuwar auren ba,tunda yau babu wanda,zaiso ace nashi ne kullum a bazawara,sai magariba uka kammala aikin komai yayi neat da shi,ta cire kaya jikinta ta daura zani da hijabi tq fito bandakin tsakar gidansu tayi wanka,tsakar gidan shuru da shi qwal kowa yana daka da mugun abinshi a zuciya,girgiza kai kawai tayi cikin zuciyarta tana fadin Allah ya gyara,sam rayuwar gidan nasu a karkace take kowa da inda ya dasa tasa alqiblar tana cikin sallar isha'i kiran abdur rahim ya dinga shigowa wayarta,hindatu ce zqune kan kujerar dq wayar ke kai don haka ta daga,bata ankare ba taji sun shiga hira da hindatu,dama gata gwanar surutu,sai da ta idar sannan ta miqa mata wayar,kasa dagawa tqyi saboda kunyar ama dake gurin,itama maman na ankare da ita amma tayi kamar batq gani ba,dn tasan maryq din ba boye mata zata yi ba,cikin zuciyarta take addu'ar Allah yasa mijin aure ne diyartata ta samu su ukun cikin kwano daya kamar ko yaushe suka ci tuwonsu na masara miyar busashshiyar kubewa,santi kawai maryam ke ti wa mama don tayi missing girkin maman sosai,mama gwana ce ba baya bace gun tsara girki musamman namu na gargajiya zumudi yasa hindatu ta kasa shiru jin addar tata taqi tada zancan mutumin da ya kira din dazun ''wai adda maryam abdur rahim din dazun fa yace saurqyinki ne,kuma naji shiru baki ce komai ba'' hara rarta tayi ''wannan baki naki hindatu kamar ba'a gasa miki shi ba?'' dariya suka sa su dukka ukun,tilas yanzun ta yiwa mama maganarshin tunda tun ajiyan yake jadda da mata aure yake son yayi bada wasa ya zo ba,a kunyace ta yiwa maman bayani,farinciki fal zuciyar maman ''Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa,ya kade dukkan sharri da fitintinu,addu'a ce yanzu kawai abunyi gareki maryam'' ''insha Allahu mama,sai a tayamu muma da ddu'ar''ta fada cikin karyewar murya wanda ke nuna raunin zuciyarta,tausayinta ya kama maman ''addu'a ta zama dole akan musulmi,ballantana uwa ga 'ya'yanta,wacce garkuwa kike da ita da zaki basu wadda ta zarce addu'ar,uwar ma irina mai yara mata da take musu fatan samu mazaje na gari nagartattu,babu sallar da zan idar da ita maryama ban muku addu'a ba,ku kadai nake da su fa'' wata iriyar qauna hade da tausayin mahaifiyar tasu suka lullubeta,haqiqa uwa ba wasa bace,wata ni'ima ce daga ubangiji,cikin zuciyarta take fata insha Allahu wannan karon zuciyar mqhqifiyar tasu zata wanke daga dukan wani quncin rashin auren nata,hawayen da suka tqru suka fara sauka a idanunt cikin dabara take sharewa don kada maman ta gqni hankalinta ya tashi kiran abdur rahim ne ya sake shigowa,wannan karon ba tare da jinkiri ba ta daga don so take ta kaucewa idon amman kada tqyo tozali da hawayen da takeyi ''ranki ya dade lafiya kike kuwa?''ya tambaya a sanyaye ''lafiya nake me kaji?'' ''muryarki ce naji tamin kama da ta masu kuka'' duk da yanayi da take ciki sai da murmuahi ya subuce mata ''idan banda abun abdul har yaushe kasan muryata da zaka tantance kuka nake yi?'' murmushi ya saki har tana iya jiyo sautinshi ''na dade da sanin muyarki maryam,ke dince baki sani ba,kina gidanku ko?''ya qarashe maganar da tambaya,cikin mamaki da sigar tambaya itama ta maida masa amsa ''wa ya gaya maka?''maryam,kina shakka cikin son da nake miki ko.....any way....naje gidanku ance min baki nan kina gun mamanki'' a wani mamakin ya kuma sakata,son iya saninta babu mai shigowa gidan su mamin ta sauqi ''ya akayi kasan gidan da nake zama taya kuma ka iya shiga da sauqi irin haka?'' ''maryam,duka abdul ba mai daukar abunda yake so da sauqi bane,yana bashi muhimmanci ne afili da boye,ina fata kin fahimceni?'' ''jinjina ga irin wanna son da abdul yake min'' ''jinjina ga zuciyar data sadaukar min da kanta''sai duka suka yi murmushi ''ina fata zuwa yanzu mutanen gida sun san da zama na?'' ''tun yanzu abdul,duka duka jiya fa muka hadu'' ''ke kika hadu da ni jiya,nikam ba tun jiya ba kika zama wani bangare daga jikin zuciya ta,so inason asan da ni maryam,aure nake so nayi da,wuri idan da ina da iko ma cikin watan nan banqi ki zama tawa ba'' tilas abdur rahim ya bawa maryam dariya ''gaskiya na baka sarkin zumudi na duk duniya'' ''na amsa tunda sonki ne ya ja min'' cikin qanqanin lokaci ya cika zuciyarya da farinciki ta mance duka abinda take ciki,ba dadewa da gama wayar tasu bacci yayi awon gaba da ita don tuni mami ta yarje mata tayi kwananta a gida washegari taa dawo 🎄🌲🎄🌲🎄 qarfe tara na safe ta gama shirinta tas,a falo ta taradda hindatu na shirya musu abun kari kan center table daya daga cikin abunda jiya ya zama mallakinsu cikin girmamawa hindatun ta gaidata ta amsa mata tana tambayarta mama ''mama na gurin baaba'' ''ya dawo ne?'' ''eh ya dawo dazu da sassafe,kin sanshi da tafiyar asubanci,yauwa tace idan kin tashi ki shiga ku gaisa'' ''yanzu kuwa''ta fada tana ciro wayarta dake tsuwwar shigowar saqo tana dubawa saqon barka da asuba ne aga abdur rahim,zaqaqan kalmomi da suka sanyata mirmushi ita daya tamkar wata zautacciya,tana mamakin yadda zuciyarta ta nutsu wa abdur rahim lokaci guda,sai da ta kammala karantawa ta masa reply sannan ta koma bedroom ta ciro dubu goma cikin kudin da mami ta bita kyautasu jiya dubu goma sha biyar mamanta inna haule baaba hadiza sai lubabatu jamila da shamsiyya su ta tarar cikin dakin,kallo banza uka suka bita da shi,gefan binta ta matsa zata zauna,cikin rashin mutunci bintan ta janye jikinta tana wani harare harare da kumbure kumbure gaida su ,bata da isar da zasu amsa mata har gara inna haule ta ama din sama sama,cikin girmamawa ta gaida baaban nata,ba laifi a sake ya amsa mata har yana tambayarta gun aikin nata,shiru ne ya biyo baya na wasu mintina sanan baaban ya dubi jamila ''inatambayarki tun dazu kun min shiru,yaro yace shi baisan lokacin da ya aureki ba,to inason in san ta yaya akayi ya aurekin,tunda shi ya rantse ya mayq bai san ke matarsa bace kuma bazai dawo dake ba'' cikin fitsara da rashin tarbiyya ta zumburo baki ''toni baba....ka tamvayi hadiza mana'' ya juya ga inna hadizan ''to kimin bayani tunda tace a tambayeki'' cikin borin kunya da haqiqancewa tace ''haba malam,wannan wane irin abu ne,ya zaka zo kasuwa ka dinga kwance min zani,sai da ka tara min idon duniya ni da diyata zaka hau bin qwaqwafinmu'' ''ke hadiza dubanni nan da kyau,na gaji da iskanci da rashin mutuncin yaran nan,jiya tunda naje qauye fita ta daya na gaza fita,zance

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138