Skip to content

Chapter 47

Chapter 47

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,256 words 0 views Progress saved
Download Book

mai yawa kamar yadda a baya yayi nufinta da shi 🍂🍃🍂🍃🍂🍃 Washegari mai lalle tazo yi musu,babu yadda mami batayi da abida ba amma qememe taqiya,tabe baki tayi ''nifa mami ba za'a batan hannu ba hakakawai da wannan abun'' ''banda abinki ai shi jan lalle ga mace sunna ce baya ga haka ma ado ne''inji mami ta sake ya mutsa fuska ''um um,a muku dai,mukam a turkey bamu irin wannan abun''ba wanda ya kuma tanka mata cikinsu nanta kwanta tun tana kallin qunshin har bacci yayi awon gaba da ita kamar ko yaushe suna table don cin abincin buda baki u ukun maryam mami da abdallah,ta zubawa mami da abida ta soma zuba na abdallah,ya dago da sauri don yaga iya wanda zata zuba din don vaiso ta cika masa plate kamar na jiya,idanunshi suka sauka kan zara zaran fararen yatsunta da qunshin yayi kwanciyarshi kai ya sake fidda kyawun hannunta,farar fatarta ta sake shar Zanen ya burgeshi duk da ya saba gani lokaci lokaci gun maminshi,duk kuwa sanda tayi din tun yana yaro ya dinga cewa tayi kyau kenan,maryam ta janye hannunta bayan ta ajjiye nasa plate din ta koma mazauninta,sam babu wanda ta lura sai abida,kishi ya cikata har taji kamar ta guntike hannun maryam din,ya janye idanunshi daga kan lalken suka hada udanu da abidan ''ke ina naki kwalliyar?'' ''abida kam ai ta manta gargajiyar al'adarta,tace bataso bata mata hannu za'ayi,bayan shi kanshi ma ganine'' caraf abidan tace ''naga kamar ya burgeka ko,ba damuwa sai amun gobe'' tabe baki yayi ta daga kafadarshi hade da ware ya tsunshi ''no,idan ta nine kada ki sauya ra'ayinki ki bata hannunki''ya qarashe zancan yana jan plate dinshi ta soma cin abincin zahariyya ce tayi sallama hannunta duka biyun dauke da foodflask masu azabar kyau da tsada,fuskarta a washe da faea'ar data qiqirarwa kanta ta qaraso gun,ta fara da dora flask din duka saman teburin wadanda tunda aka shigo dasu maryam take jin matsananciyar faduwar gaba ta kuma kasa daina kallonsu,mami ta gaida kana abdallah,tsakanin ita da abida kuwa babu wanda ya kula wani kowa na ji da danbanzan girman kanshi rawanin tsiya ''favourite food na ya abdallah nene ra tashemu sai da mukayi masa wai yadda ta saba sanda alhj baaba(alh abdulkareem mai nasara kenan mahaifin abdallah)yana raye wai yanzun ma ba zata fasa ba'' murmushi mami tayi tana janyosu gabanta tare da fadin ''kai kice mata kam mun gode qwarai,kamar kuwa tasan yau bamuyi girki ba nace maryan ta bari sai sahur aikin yayi yawa''inji mami sanda take hude flask din,rake kuwa qamshi ya cika gurin ''ki mata godiya''inji mami sanda zahariyyan ke nufin fita ''zata ji kam''ta amsa mata lokacin da take qoqarin sanya qwayar idanunta cikin ta maryam a fakaice,cikin sa'a kuwa suka hada idon,wanu mummuna kallo mai cike da gargadi da jan kunne tayi mata kana ta fice Gaba daya ta saki cin abincin ta zurfafa cikin tunanin yadda zata salwantar da abincin ba tare da tabar kowa ya dandana ba,tayi imani komai zasu mata ba zata iya bari tana gani gaban idonta wannan ahli su salwanta ba,qarshen butulcin da zata musu kenan wanda ba zata iya yafewa kanta ba har abada,cikin haka taga mami na kiciniyar bude food flask din zata zuba,da sauri ta miqe tana fadin ''mami barshi in zuba miki mana ''tuni har ta isa gabanta ta karba don kada ta yanke mata hanzari tace ta barshi,ta jawo flask din miyar gaban table din sosai ya zama rabi kan tebur din yake zaune rabi kuma free ba matokari,sai ta jawo na abinci ta bude,da plate a gabanta amma sau tayi dabarar miqa hannunta tavdauko na can sashen da abida ke zaune Tana daukar plate din ta sakeshi kan flask din miyar take nautin tangaran din ya rinjayeshi sukayi qasan table din suka tarwatse kan tiles,tangaran din ya koma piece,taja baya da sauri tana salati tate da kallon gun da abincin suka kife ''subhanallahi ya haka maryam?'' ''for god sake mami yanzu wannan wane irin kidahumanci,ita din qaraman yarinyace da zata kifar da abinci flask biyu,kayi magana kuma yanzun mami ta ji haushinka ta saka a black list''ya qarashe maganar cikin bacin rai yana yayyarfa hannu da jujjuyawa hagu da dama kan kujerar da yake zaune harara ta balla masa sannan ta kalli maryam ''ina fata baki ji ciwo ba maryamu'' kai ta gyada zuciyanta na wani irin gudu gefe daya kuma tana hamdala ga madaukakin sarki da ya bata nasara a sauqaqe ta rabasu da abinda zaya hallakasu,ita ta tsaya ta gyara gurin duk da momi tace ta bari sai ta huta tukyn amma sam ta qiya,bazata iya ba don ko quda bata fata ya dandana abincin,balle ma ta tabbata ban da awa biyu ko uku indai da gubar abincin zai fara ratattakewa ta gyara gurin tsaf ta kwashe bayan ta rage kadan ta samu yar roba ta zuba hade da miyarshi ta shige da shi dakin gadonta ta tura ahi qasan gado,sai da ta gama komai kafin ta kwanta ta jawo robar don dubawa,cikin awa uku abincin ya fita kamanninsa kamar wancan,batasan lokacin da hawaye suka soma zuba daga idonta ba mutum abun tsoro Allah abun tsoro yanzu dan uwanka bil'adama kake da buri yaci wannan abun? waishin wanne rin laifi ne abdallqh ya yiwa mutanen nan ne haka da zafi da suke da burin rabashi da soron duniya? sai kace mudin an mana wahayin tabbata acikinta? kwana nawa ne kaima ka hada ya naka ya naka ka qara gaba? koda shekara miliyan zakayi wataran dai sai sun qare din ka tafi. itakam ko kadan batq ga abun morewa ba wajen cutar da wani bayan ka san cewa Allah bazai taba qyaleka ba sai yabi kadi,duk wanda yaci nanin nanin dole ta cishi cike da kasala da mutuwar jiki ta shige toilet dinta tayi plushing din duka abincin ta wanke robar ta wullar a dust bin 🍃🍂🍃🍂🍃🍂 Sallah bikin daya rana,cike da walwala farinciki bikin sallah ya soma gudana cikin duniyar musulmi baki dayanta,sai a lomacin mayama ta dinga ganin dangin su mami da na mahaifin Abdallah,don kusan kullum ne sai sunyi baqi,saboda haka bata samun zama aosai,damuwarta daya ma kada abdur rahim yace zaya zo ya samu bata da lokaci sai gashi bai ma nemi zuwanba iyakaci waya sai saqon,barka da sallah daya turo mata na credit din dubu goma yace kuma ta jirayi kayan salarta duk ranar da zaya zo Ta fuskanci ba kadan bane maso sun abdallah cikin danginsa daga na mamin har na abbaanshi,kishi ke hana abida zama ciin gidan tayi ficewarta yawo sai dare ''rashin sani yafi dare duhu''maryam kan fadi hakan cikin zuciyarta ko kuma tace ''bonono rufin qofa da barawo''a duk sanda taga abida na wannna haukar kishin nata don bata da masaniyar kai kudi abdallah daga ita har zubaidan bare salma da saddiqa da bama ganinsu ake ba,har ga Allah tausayinta takeji kan fadawa son botsatstsen mutum irin abdallah,wanda koda yana sonki zaki sha wuya da shi bare kuma baiyi da ke a ganinta hudu ga salla suka fara samun sararawar baqin duk da ana cikin dai hidimar sallah da shagulgulanta da la'asar ne babu dadewa da gama salla wayarta ta fara ringing,tana kan cinyarta din haka ba jinkiri ta daga,muryar jabir ta tsinta

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138