Chapter 123
Chapter 123
mata rakiyar idanu wayon da ya mata yasa ta dan saki jikinta kadan taci naman da dan drinks,sai da ya tabbatar ta kwanta yaja mata bargo har zuwa kafadunta kana ya sunkuya ya sumbaci goshinta ''kiyi bacci baby,kina tare da ni''a hankali ta gyada kanta kana ta lumshe idanunta,shi ya tattara kayan da sukayi amfani da shi duka ya fidda zuwa kitchen A qalla mintina talatin yayi kafin dawowarsa dakin,ya shigo ya rufe qofar da bismillah sannan ya isa ga makunnin qwan dakin ya maida hasken zuwa kala mai duhuwa ta bacci,tun dazun idonta biyu tadai rufe idin ne kawai amma fargaba ce fal ranta,tana jinsa ya gama tofa addu'ar bacci ya shafe jikinsa da ita,ya karanta mata itama ya soma shafa mata zarcewan da ya soma yi shi ya sanyata bude idanunta ta riqe hannayensa duka,cikin rawar murya tace ''kayi alqawari fa....'' ''baby bazan iya cikawa ba kimin afuwa''ya bata amsa ''amma....''hade bakinsa yayi da nata wanda hakan ya hana mata damar qarasa abinda take ahirin fada din Ya kusa minti goma bakinsa kan kunnenta yana gaya mata wasu kalamai da suja kashe mata jiki gaba daya shi kuma ya samu daman aika mata da saqonni kala daban daban masu dauke duk wani tsoro da fargaba,cikin shu'umancinsa ya mantar da ita duk wani tsoro da wata fargaba,sai da ya mata jagoraxa duniya ta daban wadda ko cikin mafarki bata taba shiga makamanciyarta ba sannan ya fito mata da muradinsa muraran,sai a lokacin ta gane lallai wayo abdallah kawai ya mata,kuma a lokacin ta raina duk wani wayo nata,koma mata yayi tamkar mahaukacin zaki da yunwa ta koroshi ya fito farautar abinci,ba qaramin tsorata tayi ba,ya koma mata gaba daya kurma bebe kuma makaho,bai sauraran komai sai abinda yasa a gaba,cikin zafin nama yake fidda zazzafar soyayyarta data jima danqare cikin zuciya da gangar jikinsa Bai ankara da barnar da ya tafka ba sai bayan shudewar awanni kusan shida,kuka take sosai idanun nata sun gama zama gauta saboda ja,sosai suka kumbura kamar an hura su,duk yadda yaso ta tsaya tsaiwar ta gagareta,dole ya maidata ya kwantar,tausayinta ya ratsashi,ta ya akayi ya yiwa maryamunsa irin wannan barnar?,shi kansa bai sani ba baisan lokacin da ya aikata ba,kawai sai ya koma saman gadon ya fara qoqarin janta jikinsa,a tsorace take da shi sosai saboda haka runtse idonta tayi sosai ta qanqame jikinta guri guda duk da ciwon da jikinta yake mata,bata so ya ko taba ta,gani take tsabar mugunta ce yana sane ya mata hakan bayan ya mata alqawarin babu abinda zai mata,wanne irin roqo da magiya ne bata masa ba amma yayi banza da ita,shi kurma ne ko makaho ne? sarai ua fuskanci batason ya taba ta ne shi kuma kukan nata ne bayaso,cikin matuqar sanyin jiki da na murya tamkar ba abdallahn mami ba yace ''ba wani abu zan kuma miki ba maryam,kiyi haquri ki kwanta jikina,baki ganin yadda jikinki ke rawa kina buqatar taimako na'' cikin muryar kuka tace ''ko mutuwa ma nayi ba kai ka jawo min ba,ina zaman zama ne ashe baka da imani,so kake na mutu''duk da hankalinsa,a tashe yake sai da taso bashi dariya,ta yaya wannan abun zai kasheta,idan da yana kisa ai da mata da yawa sun mutu kenan,ganin ta kafe kai da fata bazai taimaka mata ba ya sanyashi shareta,ya sanyata cikin jikinsa ta dolenta,babau qarfin qwatar kai hakan ya sanyata taci gabq dq kukanta tana cewa baya sonta dama,bashi da bakin magana illa ''am sorry,am verry sorry,kiyi bacci idan yaso gobe saikimin duk hukuncin da ya dace da ni abdallah zai karba saboda laifi yayi miki,shi kansa yasan ya cancanci hukunci'' tun yana jin surutanta har yaji dif,ya keqa fuskarta data hada ja yaga bacci ne yayi awan gaba da ita,ajiyar zuciya ya kuma sake ya sake maidata jikinsa,sam bacci qauracewa idonsa yayi,tausayi qauna da soyyarta ke addabarsa,a hankali yaji jikinta ya fara daukar zafi da alamun zazzabi ne yake kamata,addu'a ya dinga yi,cikin zuciyarsa Allah ya kawar da zazzabin nan kada abun ya yiwa diya nan yawa,kafin asuba kuwa jikinta yayi rigif da zafi,har wani huci yake fitarwa Cikin baccinta ta jita aruwan zafi yana ratsata,da azama ta bude kumburarrun idanunta ta saki qara data bashi tausayi,duk yadda yaso sata ciki ruwan dumin taqi shima kuma ya kasa saboda baison kukan da take,ahi ya gama shiryata tsaf kana ya bata guri don ta tubure masa sai wani dakin ya canza ya bar mata wannan Qarfe bakwai ya sake leqota sai ua sameta kwance kan abun sallah bacci ya dauketa,a hankali ya lallaba ya dauketa ya maidata kan gadon ya fara qoqarin rabata da hijabin jikinta saboda zafin zazzabin dake tashi a jikinta,garin haka ta bude idonta sai ta tabe fuska zata saki wani kukan,da sauri ya kwantar da ita yana daga hannayenshi sama ''ni fa babu abinda zan miki,hijabin da kika bari a jikinki qara miki zafin zazzabin yake'' kanta ta cusa cikin filo tana fadin ''nidai ka fita wallahi'' tsam ya miqe ya fice daga dakin yana waiwayenta,ta sa gefan hijabinta tana share hawayen da yaqi tsaiwa,itakam da tasan haka ake shan wuya da ta gudu wlh,ashe duk wayo abdallahn yake mata don yaga ya girmeta Har qarfe goma na safe yana fama da ita,taqi yarda ko dakin ya shigo bare ta sha tea din da ya dafa mata,don ba girki ya iya ba,da zarar ya shigo dakin zata fashe masa da kuka,duk yabi ya susuce,ga ciwo da alama tana jinsa sossi,ya kira raaliya bai sameta ba tilas ya kira baaba uwani,a falo ta taddashi kwance kan doguwar kujera rigingine,da sauri ya miqe yana tambayar baaba uwanin ''gaskiya ranka ya dade kuje asibiti,ta gayamin tana jin ciwo,sosai hakanan ba zata iya shiga ruwan zafin ba''shiru yayi donshi ba wani asibiti da ya sani idan ba mallakin maminshi ba,don tun yana yaro acan ake bashi duk wata kulawa saidai idan abbanshi ne yace a fiddashi waje,yana kunya kuma yajewa mami da maryam a hakan,dabara ta fado masa don haka da sauri ya yiwa baaba uwani godiya yasa driver din gidansu ya maidata Sai da ya hada girar sama da ta qasa sannan ya shiga dakin,tana kwance don bata isa ta zauna ba,ganin fuskarsa a haka yasa bata yi masa boren ba,don ta manta rabin da ta ga fuskarsa a hakan,gaban ma'ajiyar kayanta ya isa ya ciro mata atamfa da hijabi,ganin yana niyyae sa mata su ns yasa ta saki shagwababben kukan nata sai ya kauda kai yana jin ciwon kukan har cikin ranshi ya zube hannayensa cikin aljihun wandonsa ''ya isa,idan zaki iya ki sauya da kanki yanzu na baku minti goma''ya fada yana ficewa a dakin Cikar mintina goma ya dawo dakin har ta sauya din kuwa saidai zanin da bai dauru ba,ya dagata ya gayara mata daurin zanin kana ya dauketa cak ya fice da ita,Allah yasa babu kowa a gidan don har security dinshi ya basu hutun sati guda,a motar ya sakata ya dan kwantar mata da kujerar sanann ya dawo ya rufe ko ina Sunan asibitin kawai data gani yasa ta tuna cewa asibitinsu ne,idonta cike da qwalla ta dubeshi yana gyara parking na motarsa a inda taga manyan likitoci ke parking kawai a gun ''amma ya za'ayi ka kawoni gun mami abdallah baka jin kunyarta ne?''sai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138