Skip to content

Chapter 53

Chapter 53

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,280 words 0 views Progress saved
Download Book

dan koma ta runtsa,maryam kuwa bata bawa kanta wannan hutun ba,tun mami na mata mita kan ta huta harta gaji ta barta,cikin kwana biyar din nan sai da tayi saukar alqur'ani biyu,dukkan alkhairi babu wanda bata roqawa mami mamanta raliya hindatu da ita kanta ba kwana uku sukayi a madina ziyara,daga nan suka hada ya nasu ya nasu,mami tace itafa sai ta sauka a sudan tukun,cikin alamun tuburewa yace ''me zamuyi kuma a sudan mami,dear fa ta matsanta tana da buqatar gani na,i have alort to do mami a gida,inaga tafiya zanyi nikam sai kin taho'' ''wa salaam wa kitabi,nima na huta da qorafi kama gabanka Allah ya miyaye hanya sai mun taho''anan suka raba jaha da shi,maryam batasan me zasuyi a sudan ba sai da suka je,unguwar tamkar tana cikin qasarta haka ta gani,sai dai 'yan bambance banbance da ba'a rasa ba na suturu abinci da al'adu. kallo daya zaka yiwa matar ka tabbatar da 'yar sudance gabanta da bayanta,saidai mamakin da maryam tayi yadda hausa radam ta kama bakinta yanayin karyewar hatshen bw kawai zai nuba maka ba yarenta bane ara tayi ta yafa,ba abun mamaki bane jin yaren gausa bisa harsukan wasu al'umma ko qabilun da ba ahalin hausa ba,saboda yaren hausa yare ne sha kundum da ya fantsama lungu da saqo na fadin duniya,kusan a yanzu shine yare na biyu ko na uku da akafi amfani da shi,babu inda zaka tsoma qafarka a duniya ka rasa wanda ya iya ko yakejin yaren gida ne babba mai bangare biyu bangare daya na matar ne daya bangaren kuwa harkar sana'arta kawai take gudanarwa,gyaran jiki gyaran gashi lalle ne kayan gyaran jikin na mata turaruka na ruwa dana ice da humra na tsuguno harda na wanka,kai hatta da kitso idan kana da buqata akwai mai yi maka,yadda maryam taji suna hira da matar tana tambayar mamin bayan saduwa ya fahimtar da ita lallai sun san juna dama can da mami,tunda har taji tana tambayar matar wata najwa tace taje daarfur sai gobe zata dawo,hajiya laila ita kewa mami irin wadan nan gyararrki zamanin alh abdulkareem mai nasara nada rai,gayu kam da gyaran kai mami ta yishi lokacin da mijin nata ke raye shi yasa ta zama ta gaban goshinsa,duk da a yanzun ma bata saki gayunta ba saidai ta daina wasu abubuwan tunda babu mijin cikin kwana uku matar ta fara tsuma maryam,gyara take mata bana wasa ba tunda ta san haj bintu akwai sakin hannu idan harka ta hadaku,wani irin daddadan qamshi ta zaunar a jikinta wanda ko zama tayi a gu sai qamshin ya nasheka,farar fatarta ta canza yanayi farin nata ya saje armashi kyau gami da daukan hankali,sati guda ana mata gyararrkun taki wanne b'angare kafin suyo gida nijeria bayan haj laila ta hada muta wasu hade haden da zata ci gaba da amfani da su koda bayan bikin ne bayan sun koma boyonta mami ta dinga yi,tuni ta daina komai a cewarta bataso nan da kwanakin da suka rage biki wani abu na gyaran da akayi mata ya samu naqasu,baaba uwani ita ta goyi bayan mami tayi uwa tayi makarbiya take komai sunyi waya da mama da hindatu,mama cewa tayi sai tazo godiya don sam bai canci ta yiwa mami godiya iya ta waya kadai ba,amma da maryam ta sanar da mamin sai tace sam wallahi kada tazo,idan kuwa tazo din to ta nuna ba ita ta haifi,maryam ba,karamci da mutuncin mamin sunyi yawa har suka sa mama ta rasa ma me zata ce ko ta saka mata da shi?,hindatu amarya kam babu zama,ita da qawayenta ke gudanar da komai,don hatta da rabon kati su suka dinga yi,saboda mami ta riqe maryam tace babu yawon rabon iv da zata ta bata jikinta,ganin komai take tamkar a mafarki,wai tau ita maryam ce ake kira da sunan *amarya*,lallai babu wani abu da yake tabbatace sai mulkin ubangiji bata fidda ran ganin irin wanan lokacin ba saidai koda wasa bata taba kawoshi nan kusa ba haka,dukka kayan da zata saka raliya ta fidda takai dinki,duk wata sabga da ya zamto ita zatayi raliya ta tsaya kan komai ita keyi kan jiki kan qarfi kamar a itace maryam din,kyakkyawan amincin da aka gina shi bisa turbar gaskiya da amana kenan,yakan iya kai ku zama qasan inuwar al'arshin ubangiji ranar da babu wata inuwa sai taahi Biki ya rage saura kwana uku da daddare tana gurin baba uwani ta kai mata wasu kaya da take son bata ita da yan jikokinta kiran hindatu ya shigo wayarta ''kinyi tsada adda maryam,mami ta tsaya miki''inji hindatu cikin salon tsokana ''kema mama ta tsaya miki ai ya akayi ya gidan'' ajiyar zuciya tayi ''lpy lau,gida alhmdlh don har wasu daga 'yan gaya sun fara sauka,saidai ta wani bangaren ba lafiya lu ake ba''sai da gaban maryam din ua tsinke ya fadi,cikin sakonni zuciyarta ta fara raya mata faruwar abubuwa marasa dadi masu yawan gaske kuma duka akanta,muryarta na rawa t tambayeta mai ya faru dariya hindatun ta qyalqyale da ita ''kwantar da hankalinki adda mana,na gaya miki mu lpy muke alhmdlh,bangaren da babu lafiyar su inna huwaila ne da baaba hadiza,kinsan watan baqincikinsu ya kama,yanzu haka jamila na daki ita da sauran yan uwanta anata mata ruqiyyar banza da wofi ta tada aljanun qarya,wai wlh indai na auri jabir sai ta kashe kanta,ni kuwa nace shashasha ki kashe kan naki mana kanki da uwarki kika yiwa asara,ita kuwa inna huwaila sai zirga zirga take ta fita aje ta dawo ta kasa zaune ta kasa tsaye,zuwa dare saiga aminiyarta uwani sai ji mukayi tsakiyar tsakar gida tana cewa,ke kika kawo kanki kikace na kaiki gun bokan nan bani na jawoki ba,don aiki bai ci ba kuma zak nemi tijara ni gaban kishiya?,to ai ramuwar gayya tafi ta gayya zafi shi yasa na biyoki ayita mai kankat kema kowa yaji,mugun qullin da kika so qullawa,ta fayyace duk abinda suka qulla din sannan ta dora da fadin,bola kuma na bogi ne kudi kuma muni babu yadda kika iya,aminad da kuke baqinciki da ita daga ke har hadizan ai ta fiku,yanzu gashi data miqawa Allah kukanta ta jadiye baqicikinta na shekara da shekaru Allah ya yaye mata damuwarta ba tare da tayi hasarar sisin kwabonta ba,ku kuwa haihuwar asara babu kudi babu biyan buqata ga asarar imani,sallolin kwana arba'in a ajejere kun rasa ta kusan kwana dari bakwai,amina Allah ya sanya alkhairi ya tsone idon maqiya,kuma wallahi ni da ku dukanku ke da hadizar shege ka fasa,naci uwar mace a iya tijara da ramuwar gayya,duk kuma wadda take jin ta haifu da jini uwarta ta haifeta ta fito ta tanka wai in gaya miki adda saiga inna huwaila ta fito da borin kunyarta waisai sun daky wallahi bugu daya uwale rayi mata sai gata tayi plate a qasa''hindatu ta fada tana sheqa dariya ''wai kuma ta sumewa mutane jadiza tayo kanta wai huwaila kinci amanata ta hau dukanta,lubabat u kuwa itama tayo kan,hadizar ke in taqaice miki labari kowa sai ya ahigarwa uwarsa gida ya zama na wrestling,ina ta laluben wayata in miki vedieo don,kada ayi babu ke saiga babamu nan ya shigo shi ya raba cakwakiyar,kowacce da dogon bakinta ta taho zungi zungi zata yi masa bayani don ya bata gaskiya yadda suka saba yace babu

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138