Chapter 57
Chapter 57
ba,wuce hakan na nufin bacin komai''din din din wayar ta katse,hankalinta ta msida sosai kan hanyar ficewarta,wuf ta faki idanu ta fice ta nufi bangaren nasu cike da farincikin nasarar aikinsu ๐๐๐๐๐๐ Qarfe goma da rabi ne na dare,gefan lallausan gadon dakin nata take a cure guri guda,tafiyar yan kawota da mintina ashirin yayyafi ya fara sauka wanda ya haddasa sanyi da garin yayi hade da qamshin qasa,bai kankama ba ruwan hakanan yayyafin bai tsaya ba,kusan tunda suka tafi suka barta anan take zaune bata ko motsa ba hayaniyan data soma ji cikin paflour na muryoyin maza daban daban suka qara mata fatgaba,ta runtse idonta tana jin yadda zuciyarta ke dukan uku uku kamar zata yi tsalle ta fito ''ko baka fadi ba ba shiga muma za muyi ba don an dade da daina wannan''ta jiyo muyar wani daga cikinsu,tun tana jin hayaniyar tasu sama sama har taji dif alamun basu cikin sun fice kenan da gudu gudu sauri sauri ya qaraso cikin parlojt din saboda ruwan da ya sake danyin qarfi,duk da haka ya jiqa masa fararen kayanshi,ya tsaya ya kulle ko ina ya rage yawan qwayayen dake kunne kana ya doshi dakin kai tsaye a hankali ya tura qofar dakin kana ajjiye tarin ledojin dake hannunshi,qamshin dake dakin kawai ya isa ya tabbatar maka rana ce ta musamman,tsaye gayi hannunshi harde a bayanshi,sai ya lumshe idonshi yana zuqar qamshin qasa hade da turaren jikinsa da na dakin baki daya yadda suka hadu suka fidda wani qamshi na musamman kuma na daban,gwagwarmayar da ya fada kacin samunta ta zama mallakinsa ya dinga dan tunawa,a hankali ya bude idanun nashi ya tsaya yana qarewa shigar tata kallo gaba daya jikinsa ya saki lokacin da wani tunani ya darsu a ransa wanda ya qada maaa qwarin gwiwa da azamar isa gareta,tamkar mai tausayin gadon haka ya hau ya dinga rarrafawa har ya isa gareta kana yayi zaman dirshan a gabanta sannu a hankali ya dinga yaye mayafin dake kanta har ya cimma nasarar cireshi duka fuskarta ta bayyana,saidai ya cimma idanunta aruntse ne,ya karyar da kai yana ci gaba da kallon fukartata irin kallon da bai taba samun dama ya tsaya yayi mata shi ba,kyawunta yaci gaba da fito masa muraran,sosai ya shagala har baison abinda zai shiga tsakaninsa da yanayin Qememe zuciuarta taqi amincewa da daina mugun tseran gudun da take,gashi ya sata agaba,nauyi da kunyarshi sun hanata bude ido,jin shirun yayi yawa ya sanyata yanke shawarar bude idanun nata ko yama fita adakinne ma bata sani ba da kadan da kadan ta dinga budesu har sai da suka kammala buduwa tar,da qafafunshi ta soma tozali a hankali ta dinga daga kan nata har ya sauka bisa fuskarshi da ruwan sama ya jiqa har ruwan da ya soma taba kanshi ke diga kadan kadan,batasan lokacin data ta wuntsila gefe ba cike da *TSORO RAZANI DA FIRGITA BA* sakamakon wanda ta gani *ABDALLAH* ne cikin daren nan cikin gidanta kan gadon aurenta๏ผ,idanunta ke mata gizo koko meye๏ผ,me yake faruwa ne๏ผ,hauka ce ta samu qwaqwalwar abdallah ko bashi bane bama gaba daya aljanu kesan mata wasa da qwaqwalwarta da tunaninta,ina abdur rahim da ya bar abdallah ya keto dakinsu na sunnah๏ผ dimbin tambayoyin da suka nemi jirkita mata qwaqwalwa kenan tashi guda ba tare da tasan duka amsoshinsu ba *mrs muhammad ce*๐ ๐๐๐โ๐ฝโ๐ฝโ๐ฝ ๐๐๐๐๐๐ ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ ๐บ *ABADAN*๐บ ๐๐๐๐๐๐ ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ๐บ ๐๐บ๐๐บ ๐๐บ๐ ๐บ๐ ๐ *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* ๐บ๐๐บ๐๐บ๐ ๐บ๐๐บ๐ ๐บ๐๐บ ๐๐บ ๐ ยฉ *HASKE WRITERS ASSOCIATION*๐ก *_home of expert and perfect writers_* โถ3โฃ8โฃ *_JIRGINSO ZAYA TASHI KE DAI AKE JIRA ...'YAR GATA DUNIYAR SO.... KECE DA SARAUTA_*๐ถ๐ถ *_na dawo gunki nazo baqo da sallama....kai kawo nayi qarshe...a qauna na tsunduma....kin jawo nayi roqo nazo ki ban zuma....na sawo dubi tufata mai kyau da karrama....ke naiwa kwalliyata shiga ta alfarma....._*๐ถ๐ถ *_soyayya gaskiya ce ya zanyi in raina....wanda yake aac cikintaaa nima don na zauna.......nayi dare ban masauki gidanki in kwana....zo ka shige har abinci zan maka kwadon rama....._*๐ถ๐ถ *_riqe sirri sai mai sirriiii....da fari a cikin taurariiiiii...._* *wannan waqar na sadaukarwa da readers don jin dadinsu kana iya sauraronta bayan kammala karanta wagga shafi* ๐๐๐๐ Matsowa kusa da ita ya sakeyi tattausan murmu kwance bisa kyakkyawan fuskarshi,duka hannayenshi ya ware da nufin ta iso gareshi,take jikinta ya soma bari,qwaqwalwarta so take ta tsaya cik da aiki saidai ta ware qwanjinta wajen hana hakan faruwa,bata da buqatar tsayawar tunaninta a yanzu,tama fi buqatarshi fiye da ko yaushe,ya sake matsowa gareta yana nufin janyo ta jikinshi wata hadaddiyar tsawa ta sakar masa bayan ta dira daga kan gadon jikinta na qyarma,tuni zuciyarta ta karye hawaye ya soma sintiri bisa fuskarta,dukkan tunaninta sun gama vata fyade abdallah yazo yi mata,tunda ba wannan ne karo na farko data taba ganinshi kebe da diya mace ba,amma wanne irin tsoro abdur rahim kewa abdallah da ua bashi irin wannan damar๏ผ,ko wani abu yayiwa abdur rahim din nsta har ya kai ga shigowa dakinta shi daya ba tare da wani qwaqqwaran motsi ko hayaniya ba. Abdallan ya sake motsawa don biyota qasan,cikin daga sauti hargagi fushi bacin rai da tashin hankali ta dakatar da shi ''dakata marar tsoron Allah,me kake nema da ni๏ผ,me ya shigo da kai dakina๏ผ,kana shirin tozarta sunnar ma'aiki๏ผ,kana shirin cin mutuncin matar da bata yi maka komai ba๏ผ,to Allah ya fika'' jikinta na rawa ra fara daddan na wayar dake hannuna tun dazun da aka kawota lubabatu ta danqa mata a hannunta Numbers din abdur rahim ne guda uku,saidai duka wadda ta kira sai taji ringin dinta cikin aljihun abdallah,cike da wani tsoron ta dago ta dubeshi,hawaye ne kawai ke kwaranya da sintiri kan fuskarta ''abdallah๏ผ,ina abdur rahim๏ผ,me kayi mishi๏ผme ka yiwa mijina๏ผ๏ผ''ta qarasa maganar cikin qaaraaji baisan sanda yayi alkafura ya diro daga gadon ba,gadan gadan ya nufeta don ya riqeta ganin yadda take kuka tuquru tana dafe bango,saidai kafin ya kai ga riqeta ta goce ''kada ka tabani,kaji tsoron Alkah kasan cewa ni matar wani ce''cikin cool voice dinsa mai cike da jarumta da mazantaka wadda a yau rauni ya cikata ya saje maidata sassanya yace ''pls cool down mana,ki natsu in miki bayani kinji,ki saurareni'' ''bazan nutsu ba,in nutsu ka cucu ne,me kake nufi abdallah,me nayi maka,ka shigo dakin aure na,banga mijina ba,na kira wayoyinshi suna jikinka,ka gaya min me ka masa๏ผ๏ผme kayi masa๏ผ๏ผ๏ผ'' duk yadda yaso tayi shiru ta saurareshi abun ya faskara,idanunta sun rufe bisa dukkan zatonta ko abdallah ya kashe abdur rahim ne ''ki zauna ki fahimceni...''' ''bazan fahimceka ba.....ina mijina.....ina ka kaimin mijina abdu........'' ''maryam๏ผni ne nan mijinki,ni ne mijinki ba abdur rahim ba,ni abdallah da ni aka daura miki aure๏ผ''ya fada yana nuna kanshi shima cikin daga murya har jijiyar wuyanshi na tashi sai kukan nata ya tsaya cak,ta tsaya tana kallonshi tamkar doluwa ko sakarya,jin maganar tayi tamkar cikin mafarki,da saufi ta kama hanunta ta mintsina sai ta tabbatar cewa gaske ne,girgizq kantq ta shiga yi tana fadin ''ba kaine mijina ba,bakai ka aureni ba ni zaka yaudara๏ผ'' ''bari in baki shaida don ki tabbatar''ciro wayarsa yayi ya kira wasu nimbers,ga mamakinta sai ga muryar abdur rahim radau ''kai,bakasan ganganci bane kiran ango daidai wannan lokacin ba๏ผ,ko baka shiga dakin marya bane๏ผ''yake tambaya cikin sigar zolaya ''hmmm,abdul maryam zata amince nine mijinta kuwa๏ผ'' dariya yayi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138