Skip to content

Chapter 113

Chapter 113

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,291 words 0 views Progress saved
Download Book

falin qasa ta zauna saboda maryam din ta fara jiyo kakarin amai,da hanzarinta ta shiga dakin,ita ta wanke gun data bata din ta maidata gado ta kwantar tana mata sannu,ta taba jikinta kana cikin damuwa tace ''maryam anya ba ciki gareki ba kuwa?'' duk da tana cikin ciwo sai da tambayar tq bata kunya,tayi qasa da idonta tana girgixa kai,sake matsowa mamin tayi tana lallabarta ''kada kiji kunyata idan shine ki gayan kada na yita baki magunguna muyi asararsa don Allah'' nan ma kai kadai ta iya girgiza mata ta kasa hada ido da ita ''to shikenan,allura dama zan miki naji zazzabin yaqi sauka'' sam bata qaunar allura,da kayi mata allura gwara ka zabga mata mari,ita ta sani ciwonta ba na magani ko allura bane,da sauri cikin murya ta marasa lafiya tace ''don Allah mami ba yanzu ba,a barshi sai anjima zai iya sauka''ta fahimci allurar ce bata so don haka ta qyaleta ta sake bata wasu magungunan Ranar kam har kusan biyu na dare ana fama,qarshe dai allurar da bataso mamin ta mata,bayan tasha fama da ita kafin ta tsaya din,sai kusan uku saura na dare ta samu bacci ita kuma mamin ta koma dakinta πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒ A daddafe ta tashi tayi sallar asuba sakamakon baccin daya cika mata ido,duk da zazzabin ya sauka baki daya sai ciwon kai dake son matsanta mata kuma,da qyar ta gama sallar ta kwanta saman daddumar zuciyarta babu dadi,duk wani minti idan ya wuce sai taji kamar yana sake nesantata da abdallah ne A hankali taji an turo qofar dakin,ta daga kai tana amsa sallamar da akeyi,mami ce cikin hijabinta da carbi a hannunta da alama idar da sallarta kenan itama,tayi qoqarin tashi zaune don gaisheta mamin tace a'ah yi kwanciyarki,a haka suka gaisa ta duba jikin taji babu zazzabin,shuru tayi bata ce mata kan nata na ciwo ba din kada ta daga mata hankali ''yanzu maryamu jinkirin dawowar abdallah yasa kika matsantawa kanki da damuwa haka har da ciwo?,lallai ba shakka gaba guduwa zaki dinga yi kibi mijinki kuna barina kenan?''ta fada cikin tsokana da zolaya,kunya ta kama maryam sosai,ita kanta batasan tana misbehaving har haka ba,batasan ya akayi abun ya hudata haka ba har yake bayyana kanshi da kanshi ba tare da ta sani ba. ''a'ah daina jin kunyata,ni hakan dadi ya yimin sosai,Allah ya qara hada kanku,aikin da yayi ne ya tsaudashi jiya kafin na kwanta saiga kiranshi,amma alhamdulillahi an samu nasara ya kama dukkan jama'ar daya shirya kamawar sai mu yiwa Allah godiya'' hakanan taji wani sanyi na sauka tun daga kanta har tafin qafarta,a gida ko a waje abdallah jarumi ne tabbas babu kokwanto,a hanakali cikin zuciyarta ta dinga fadin alhamdulillah ''sai ki kwanta kiyi naccinki sosai,kiyi bacci harda minshari ko''ta sake fada cikin zolaya,murmushi tayi tana sake sunkuyar da kanta mamin ra mata sallama ta fice Ta lumshe idonta tana jin wani shauqi na kamata,duk da ciwon da kanta yake murmushi sai daya subuce mata,ta dan dafe kanta idanu a lumshe,a hankali bacci mai dadi ya sureta πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚ Sannu a hankali taji yanayin baccin nata na sauyawa,ta dinga bude idanunta a hankali har ta kammala budesu tas,yana zaune gefan gadon nata sanye da baqar jallabiya mai hula irin ta maza ya zuba mata idanu kamar wanda aka bashi aikin zana fuskarta,wani abu mai kama da farinciki taji ya ratsata ''welcome dear''ya fada a nutse ''an tashi lpy gimbiya?''ya tambayeta idanunsa har yanzu na kanta,kasa amsawa tayi sai cusa kanta da tayi cikin hijabinta,yayi maganar amma taqi dagiwa sabida haka ya tashi tsam ya koma gabanta yana qoqarkn dago fuskarta amma ta qiya,shima bai sakar mata qarfi ba ya qyaleta yana fadin ''kin daga min hankali da yawa baby,tun asuba na baro abuja duk sabida nazo na ganki amma kin min rowar fuskarki,shikenan na gode''ya fada yana miqewa zai fice a dakin,sai ta bude ido daya taba satar kallonshi tamkar ta tsaidashi tana kallo ya fice a dakin a hankali kamar wanda aka qididdigewa iya takun da zaiyi Kunya da tsoro ranar suka hanata sakewa ko fitowa,sai taci gqba da kwanciyarta kan gado abinta mami na kulawa da ita a tsammaninta jikin da saura,tana son ta fito ko zata sake ganin fuskarshi amma kunya ta hanata,tana jiyo muryarshi a falo lokaci lokaci shida mami suna maganar bangaren nene da ta ga ana sawa sababbin furniture _WASHEGARI_ Tas ta jita ta warke sosai,ko guntun ciwon kan ma babu shi,qarfe tara ta hada ruwa mai zafi tayi wanka,muradin ganin abdallah take,shi kuma kamar ya sani tun jiyan bai sake leqota ba duk da ya turo mata guntun sms _sorry dear na zama busy kan wani abu,see u later_,iya abinda ya turo kenan Ta shirya cikin atamfa riga normal da zani rafa,tayi lite make up kana ta feshe jikinta da turaruka masu dadi,ta daura dankwalinta bayab ta gyara gashinta kai azabar santsi ta hadeshi da ribbom madaidaici,haka nan ta tsinci kanta da yin kwalliyar,ba qarya ta mata kyau matuqa,muryarshi da jiyo a parlour ta haifar mata da fargaba,sai ta koma bakin gado ta zauna ta fasa yunqurin fitar da takeyi,ta dauki wayarta ta fara danne danne kanta a qasa Raliya take turawa tex don taga missed call dinta na kiran data mata tana bacci A hankali taji ana taba qofar kana aka turota,cikin qananun sakanni tattausan qamshi ya buwayi hancinta,qamshi ne mai kwantar da rai tamkad zai saka bacci a nata bangaren wani shauqi ya qara mata,kallo daya ta masa ta sauke idanunta qasa,kunya take ji sosai,ga wani maganadisu dake fisgarta cikin idanunshi,wani kyau na musamman taga an qara masa,gani take kamar mami ta gaya masa sirrinta,nauyin hada ido take da shi,yayi kyai sosai cikin light blue din shadda,babbar riga da yar ciki da wando,fadan irin kyawun da shaddar ta masa ma bata baki ne,shadda ce yar ubansu sai maiqo take tasha bugu,a hannunshi riqe da hularse,a gogone baqi a hannunshi na fata na kamfanin armani sai takalminsa half cover irin na maza,sai ya tashi sak dan kano don ba baya bane su wajen iya wankan shadda suna sahun gaba,ba qaramin amsarsa shigar tayi ba,do da wuya ya sanya kaya komai rashin kyawunsu suqi amsarsa ,fuskarsa cike da murmushi mai bayyana sirrin kyawunshi ''amincin Allah ya tabbata a gare ki baby,ina fata kin wayi gari cikin qoshin lafiya,af kice ma anko mukayi''ya fada cikin zolaya,sai a sannann ta dubi kalar atamfar da ta saka blue ce da baqi,duk da blue din ya dan dara nashi turuwa da kadan qarasowa yayi bakin gadon ya tsugunna kana ya dafa cinyoyinta,abinda taji a jikinta shima shi yaji,sai tayi saurin zame hannun nasa,dauke hannun yayi yayi murmushi yana yiwa hular hannunshi kari ba tare da ya dubeta ba ''am too busy jiya naso inzo in sake tozali dake,ina daya bangaren can ana jeran amaryata'' sai tayi dumm ta rasa yadda zara fassara maganarshi Ya miqe ya isa gaban madubinta ya daidaita hular bisa kanshi kana ya sake dawowa inda take ''wanne saqo kike da shi gun imna wuro,qauyen ni'ima zamu je,yau idan Allah ya nufa zan zama angon mero'' batasan lokacin da ta daga kanta ba,ta yi masa wani birkitaccen kallo ido cikin ido,wani irin zazzafan kishi baqinciki da takaici ya lullubeta ''naga kina duba na maryam idan da magana kiyi''ya fada yana sake matsowa kusa

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138