Chapter 35
Chapter 35
halayen mamin ne *karamci* da *kyauta* sabanin wasu masu hannu da shunin da sun gwammace su saida kayan maimakon 'yan uwanau su amfana furniture ne ko kayan sawa,ko me zasuyi da kudin oho,bayan Allah ya wadata su ya basu arziqin amma suna maida kansu baya ''na gode mami qwarai,Allah ya qara girma'' murmushi mamin tayi ''bakin maryamu ya saba da godiya,nasha fadi miki ba haka tsakani na da ke'' kafin tace wani abu an banko qofar an shigo,abida ce kanta tsaye ta tafi gurin mami ''mami,ki shiga tsakanina da house girl din nan,hala bata san koni wace ba,ta raina ni matuqa,wallahi idan bata kama kanta ba zanyi sanadiyyar qulle danginta kaf babu wanda ya isa ya fito da su,batasan ba'a raina ni ba,bana daukar rainiοΌ'' kama kai mami tayi tana kallon abida ''qara kika kawomin ko mataki kika zo daukaοΌ''cikin rashin iya magana tace ''duka mami'' ta riga da tasan abida rainon tabara ce,ta san ita har zuciyarta magana ta fada mai kyau,ta bar ta tata ta juya ga maryam ta tambayeta mai ya faru,a nutse ta gaya mata ''tashi kije maryam,sai da safe Allah ya bamu alkahairi'' ''ameen mami''ta fada tana ficewa,yunqurowa abida tayi gurin maryam mami ta dakatar da ita mamaki ne ya ishi maryam,tana shiga daki kiran abdur rahim ya shigo wayarta,murmushi ta saki ta isa gefan gadonta ta zauna sannan ta daga *mrs muhammad ce*π πππβπ»βπ»βπ»βπ» [9/17, 12:53 PM] 80k: πππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊπΊ πΊππΊππΊ πΊππΊπ πΊππΊ πΊπ π πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πππππππ *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* ππΊππΊππΊ ππΊππΊπ ππΊππΊ πΊππΊ πΊπ πΊ βΆ2β£9β£ *_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*π‘ *_home of expert and perfect writers_* Kimanin awanni biyu suka shafe kan layi ita da abdur rahim din,ta fuskanci ya dan san wasu abubuwa game da ita wanda hakan ke qara mata amanna da qaunar da yake iqirarin yana mata din,tuni ta yanke ma ranta abdur rahim na daya daga cikin batutuwan da zasu tattauna a gobe ita da mamanta,bai barta ba har sai da ya fuskanci ta soma jin bacci tukunna ya mata sallama cike da qauna da bege mai yawa ππππππ Abu na farko da ta fara cin karo da ahi cikin gidan nasu bayan yin sallamarta shine dambe tsakanin huwaila da haduza abinda zata iya cewa bata taba gani ba,daga gefan huwaila lubabatu ce da binta ke zuga uwarsu,yayin da kuna gefan hadizar kuma shamsiyya da yasira ne suma ke nasu aikin sai jamila dake zaune bisa dakalin qofar dakin mahaifiyar tata da uban akwati a gaba,idanu jajir wanda ke nuna bisa dukkan alamu kuka take sharba ko kuma take kan sharba din,mamanta ta hango na shirin fitowa daga dakinta hannunta ruqe da dankwalinta tana mai qoqarin daurawa hindatu na biye da ita tana fadin ''don Allah mama ki barsu'' Da sauri maryam ta taya hindatu tarar maman nata ''mama wanna ba sabgarki bace,kin taba ganin suna dambeοΌ,to ki qyalesun kamar yadda hindatu tace Allah ne yasan me ya hadosu,babu ruwanki mamana tunda koma mene lokacin da zasu qulla basu nemi shawararki ba,kiyi addu'a kawai Allah ya warware musu ita ta ruwan sanyi'' da dadin baki suka sanyata a tsakiya suka koma cikin dakin abinsu,har aka gama shigowa da kayan suna bala'i basu sani ba ''amma maryama gini irin wannan namun ai bai cancanci kayan gado na alfarma irin wannan ba'' dariya ma maman ta baiwa maryam ''haba mama,tunda Allah ya baki sun cancanta din kenan,yanzu aikin kawai zamu shiga yi har kitchen din'' hindatu dake tsaye wadda farinciki duka yabi ya cikata tace ''yauwa adda maryam,kinga zuwa gobe mun gama zama 'yan gayu,babu raini wallahi,don duk cikin gidannan babu mai arziqin siyan irin wadan nsn kayan'' dadiya duka ta basu don har yau hindatu shirmen auta bai saketa ba sai da suka soma fidda na dakin maman suna shigar da wadancan sannan suka ankara,lubabatu ce ta fara gani ta zunguri uwarta dake riqe da habar zaninta daketa kwancewa saboda azabar bala'i tana qoqarin daurawa ''huwaila tayani gani,kinga su kuma wadan nan ina suka samo kayan alfarma haka'' da sauri ta juyo don ganin abunda lubabatun ke nuna mata,idanunta suka sauka kan kayan fadon da buhun shinkafa catoon na taliya mscaroni da couse couse wabda mami ta hada mata da su irin kayan da Abdallah ke rabo na musamman duk azumi sadaka ga mahaifinsa mafigayi alh abdul kareem mai nasara ''kinga inda ake abu,kare ya san ana abu a gidansu,tunda gashi yana gani a qasa'' wannna zancan ne ya dauko hankalin hadiza kan kayan ''mtswew,aikin banza aikin wofi,kayam haram din da aka samu ta hanyar haram har wani abun fariya da alfahari neοΌ,kwadayi dai ai mabudin wahala ne Allah na tuba nawa akayi'' ''kamar ku kenan da ruwan ya qarewa dan kada koοΌ'' wani irin ashar hadiza ta lailayo ta narkawa huwaila ''ai wallahi qaryarki tasha qarya,tuni na gama fahimtarki dama huwaila,sai kima kinsan cewa ba'a ja da masu kudi'' tsaki ta ja kana ta turo daurin dankwalinta gaba ''yo Allah na tuba ina abun yake,ina qudan yake ballantana romonsaοΌ,game ce anyita kuma yau anzo game over din,sai kusa haquri masu rano su dara daga inda kuka tsaya'ta antaya qeyar yaranta daki ta bar hadiza abakin qofar tana ci gaba da zage zage kamar zata tada jinnu,ta gama da huwaila ta kalli qofar dakin mama ta yi nata,ita kadai ita da yaran nata tamkar wasu sababbun tabi hindatu kam babu abunda take sai sheqa dariya cikin dakin suna aikinsu maryam ta dan dubeta kana ta kau da kai ta ci gaba da ahimfida zanin gadon dake hannunta kan sabon gadon maman ''ko kema shirin bin sahun nasu kike irin wannan dariya haka''dariyar na ci gaba da cinta tace ''ai wallahi adda maryam ki gode Allah,kinsan wannan bala'in tun jiya ake zuba shi cikin gidan nan'' ''amma ina baaba,bai tsawatar baοΌ'' ''ya tafi gaya duba inna gwaggon baba,kuma ko yana nan ma ma zai tsawatar din akaiοΌ,mowarshi aka taba fa,jamila ce ta dawo gida jiya wujiga wujiga'' sai da gaban maryam ya fadi,a hanzarce cikin fuskar mamaki ta kalli hindatu ''garin yayaοΌ'' ''to yaya jabir yace baya yi ta taho gida har dactakardar sakinta kyawawa guda uku,a kuma karbe duka wani abu na dukiya ko kadara da ya mallaka mata,amma in fada miki baaba hadiza da yake jahila ce ba ilimi a take suka hau dan sahu ta maidata wai zata bashi haquri a daidaita,wallahi in taqaice miki ko zama bata yi ba bayan dawowarta sai ga jamilar ta biyo sahunta,da duka ya koro ta daga cikin gidan da qyar ta qwaci kanta,to kuma bala'i sai ya koma kan inna huwaila wai itace sila tunda dama ta taba cin alwashin sai ta wargaza komai'' hindatu ta sake qasa qasa da muryarta kada mama ta jiyota ''in taqaice miki adda maryam jiya dai har gun bokan da sukaje ya raba tsakaninsku da ya jabir sai da suka tona abinsu,cikin hargagin fadansu'' sai jikin maryam yayi sanyi,ta bar abinda take yin din tayi zaune gefan gadon,tabbas tasan ba'a yi mata adalci ba,saidai rabuwar aure ai ba dadi gareta ba,espicially yaran gidansu da dukkaninsu babu wani mai qwarin gwiwa kan aurenshi kullum cikin jeka ka dawo suke,to ga wata kuma sabuwata samu ''kinga ya maryam,kada kice fa zqki wani damu,sakayya ce Allah ya miki ita da gaggawa haka''ta fadi ita
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138