Skip to content

Chapter 132

Chapter 132

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,291 words 0 views Progress saved
Download Book

ake ciwon yunwa a gidansa,aiko wani ke neman taimako a guna bazan bashi garin kwaki ba bare iyalina''tuni qwalla ta cika idonta,ga qoshi ga kwanan yunwa,tana son ta kyautatawa abdallah amma wlh idan taci abincin ji take kamar numfaahinta zai dauke,ba bata lokaci hawaye suka fara silmiyo mata,idonshi ya runtse don babu abinda yaqi jinin gani irin hawayenta ''ya salamullahi,daga magana sai kuka?'' ''Kinga matsonan muci abincin ko yaya ne,idan muka gama sai ki gayan meye damuwarki,idan ma duka nau'ikan abincin ne baki so ki lissafa irin wadanda kike so kona wacce qasa ne in sha Allahu ni abdallah mai nemo miki ne kinji dear,amma wanann hawayen qona min zuciya yake''ya fada yana daga mata hannu alamum ta taho,ba musu ta matso jikinsa tana goge hawayen kanta a qasa,cike da son ta faranta ransa tasa cokali ta fara ci,loma biyu kadai tayi taji wani abu ya dunqule mata sai amai tun tana yinsa tana fidda abincin da taci,da garin kwakin da tasha dazun har ya koma bata iya harar da komai,gaba daya hankalinshi a tashe yake gani yake shine sila da ya takura ta,haka ya dauketa cak yagyarata ya gyara gurin,bai samu nutsuwa ba sai da yaga bacci yayi awon gaba da ita,duk son da yakewa alkubus din da qyar ya iya cin yanka uku 🍃🍂🍃🍂🍃🍂 cikin baccinsa ya dinga jin qamshin girki,da sauri ya farka ya mutstsuka ido,ya duba gefansa bata nan,kenan ita ke aikin girki a kitchen qarfe tara na safe?,da azama ya diro daga gadon ya doshi kitchen din tsayawa kawai yayi yana kallonta tamkar ba ita ta gama sheqa amai jiya ba?,tayi kwalliayarta tayi kyau kamar ka saceta ka gudu,ta matse cikin wata riga mai roba wadda iya qibarka iya yadda zata kamaka iya kacinta qauri an mata tsaga daga gabanta daga qaurin qasa zuwa gwiwa,ta gyara gashinta yayi kyau sosai,ji tayi kawai an rungumeta ta baya sai ta saki yar qaramar dariya ''kasan kuwa irin tsoron daka bani?'' ''nima ai kin bani tsoro baby,ke da baki da lafiya ina ke ina kitchen fisabilillahi''waigowa tayi suna fuskantar fuskarta qunshe da murmushi juna yana zagaye da qugunta,ta shafi sajensa kana tace ''ras nake jina shariky,ina mai tabbatar maka idan za'a saka tsere sai na wuceka''dariya ya saka ya sumbaci kumatunta ''babu musu don naga alama,wai baby meye sirrin ne?''ya fada yana kashe mata ido,itama maida masa martani tayi ''name fa?'' sai da ya jujjuyata ya sake kallonta sannan yace''gani nayi sai wani kyau kike qarawa,fatankin nan har tafi tawa laushi,kumatunki kamar kin boye qwai,brown oily eyes dinki kamar an kuma diga musu zaiba da oil,ke tsaho ne kawai har yau na fiki ba.....''kasa qarasa maganar yayi saboda manna bakinta da tayi cikin nashi,sai da ta dan birkitashi sanann ta cire tana duban bakin nasa ''wannan bakin nawa kada ya cinyeni''sake janta,jikinsa yayi yana dariya ''Allah am seriouse,meye sirrin'' ''matso na gaya maka''sai tayi dage don duk tsahonta abdallan ya fita ta kai bakinta kunnensa ta shiga jero masa lumshe ido ya dinga yi yana saurarenta tare da sake shigewa jikinta,banji komai ba face kalmarta ta qarshe ''kaga kuwa kaine sirrin''dukkansu murmushi suka saki mai,hade da dariya dariya,ya kamo fuskarta ya hada goshinsa da nata shima yana mayar mata da martanin kalmomin,sun kusa kwashe a qalla minti goma a haka har ruwan shayin da ta dora ya fara qonewa sannan ta ankara ta zame jikinta da sauri tana cewa ''you see,shi yasa idan ina abu mai muhimmanci banso kazo ka riskeni,don sawa kake ina mantawa da kowa da komai ciki harda kaina''shi ya qarasa hada kayan karin tana tayashi da wasu abubuwan kana suka,yi wanka suka shirya don yaune ranar da abdallahn ke raba tallafi gidan gajiyayyu da asibitoci wanann karon kuma tare zasu shi da mami,maryam ma ta kafe itama sai taje don baza'a samu ladan babu ita ba ********* tafe suke cikin motar gwanin sha 'awa don baka banbance waye danta,tsakanin abdallah da maryam,shike jan motar maryam na gefansa,yayin da motar security dinsa biyu ke gabansu biyu ke bayansu,yawanci indai tare da maryam ne cikin fitarsa bai yarda driver yayi tuqi wai don kada a gane masa ita,mami na baya tana duba wasu takardu jefi jefi suna hira da abdallah ''yauwa mami'' ''uhmmm''taje dashi kanta na kan takardunta ,tasan tunda ya fadi haka tambaya gareshi ''dama wani lokaci mata na daina cin abinci sai wani abun daban?''bata bawa tambayar tasa muhimmanci ba,don a zatonta shirmene kawai irin na abdallah din haka tace da shi ''kamar yaya kenan?'' ''mami maryam,na rasa meke damunta,safe rana dare garin kwaki mai tsamin nan,abinci saidai ta dafa min kawai ni nayita narka,jiya da na matsa mata sai taci amai tayi mami,ni tausayinta ma nake ji'' wannan karom saida ta dago ta dubeta,kunya kamar tayi me ta kama hannun abdallahn a sace ta matse cikin nata ''wayyo hannu na diyana''ya fada yana yamutsa fuska kamar qaramin yaro,da sauri ta sako hannun nasa taja hijabinta ta lullube fuskarta ''kada ka sake matsa mata kan cin abinda bataso,ka barta''cikin damuwa yace ''amma mami gari fa?,bazai mata komai ba?'' ''eh yana yi ne zata daina nan kusa''ta fada zuciyarta tamkar qanqara,addu'a take cikin ranta Allah yasa hasashenta ne zai tabbata Ya sake rausayar da kai ''amma mami ni gani nake kamar yana tsotse jinin mutum ko ruwa jikinsa'' ''ba daya,nace maka zata daina ne fa'' ''to Allah yasa''ya fada cike da hope,donshi har ga Allah abun na damunsa,gani yake wata cutar ce ta samu maryam dinsa,shi yasa ya sanar da mamin nufinsa idan ya gaya mata akwai wani maganin ta bata,kasa cewa komai maryam tayi,lallai ta yarda Abdallah gabuntar dan fari da tabarar auta na tabashi sosai,a hankali mamin tace ''ki kula kawai da kanki maryam,duk lokacin da kika ji wani sauyi a tattare da ke kumin magana,kada kuce zakuji kunyata,ni mamarku ce baku da kamata''kanta aqasa ta amsa da to,shi kuwa gogan cewa yayi ''ni dama maganin kawai kika rubuta mata mami Allah na tsani naga tana shan garin kwakin nan''murmushi ta dan saki ''bakasan komai nada qa'ida ba,ba'a rubutawa mutum magani kai tsaye,indai kawai kuka ga alamun canjin wani abu ko matsala to ku sanar da ni'' ''to mami''ya amsa mata yana ci gaba datuqinshi a gurin ajjiye ababen hawa suka yi oarking duka motocin nasu,mami ta riga fita saboda isowar shugaban asibitin din ya tarbeta,abdallah na qoqarin fita maryam tayi saurin riqoshi da qarfi har sai da ya dawo ya zauna don bai zata ba,ido ya kashe mata guda daya yana fadin ''ya akayi baby da magana ne?''kicin kicin tayi ''yanzu shariky don kawai ina cin garin kwaki sai ka gayama mami don Allah?''ido ya dan zaro ''to menene don mace kina shan gari dear na?,na tsammaci ciwo ne shi yasa na gaya mata ko zata rubuta miki magani'' ''kada ka sake don wallahi ka bani kunya''kiss ya bata a goshi kana yace ''is ok,afuwan my sister''dariya ma ya bata tana zaune ya zagayo ya bude mata side dinta ta fito bayan ya sake gyara mata zaman hijabinta,duk yama tasa gun tsayawa don gaba daya atsarge yake,gani yake wai kallonta ake,security din ma da suka saba binsa a baya yace suyi gaba su zasu biyo bayan nasu,don kada wai su dinga kallonsu ta baya kimanin su goma sha biyar suka kutsa kai

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138