Skip to content

Chapter 41

Chapter 41

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,282 words 0 views Progress saved
Download Book

har gida nan kusa,amma fa abida da saddiqa kowacce ta wuce gidansu,don wlh mami bazan iya auran kowaccansu ba'' ''naji,saddiqa dama gobe tace zata tafi,abida kuwa dole ayi haquri sai an samu visa,zata sake ko sati uku ne tare da mu'' ''shikenan mami,zan wa abokina magana harkarsu ce'' qememe yaqi fita yace zai je ko ina ba sai ya tabbatar ta gama hucewa haka suka wuni a gida gaba dayansu *mrs muhammad ce* [9/17, 12:53 PM] 80k: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’– 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’– πŸ’– *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’– πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ πŸ’–πŸŒΊ πŸ’– Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘ *_home of expert and perfect writers_* β–Ά3⃣2⃣ *Allahumma ya imada man la imada lahu,ya sanada man la sanada lahu,ya giyasa man la giyasa lah,ya karimal afwu,ya hasanat tajawuz,ya khaahifal bala'a,ya azimar raja'a,ya aunaddu'afa'ah,ya munqizal garqa,ya munjiyal halka,ya muhsin,ya mujmil ya mun'im,ya mifdil,antal lazi sajada laka sawadul laili wa nurun nahaar,wa dau'ul qamar wa shu'a ushshams,wa da wiyyul ma'i wa hafifushshajar,ya Allahu la sharika lak,ya rabbi ya rabbi ya rabbi,Allah ka shiga lamarin mutanen qasar burma,Allah ka shiga lamarin jama'ar musulmin duniya baki daya don sayyadis saqalain*πŸ‘πŸ½πŸ‘πŸ½πŸ˜”πŸ˜” Qarfe goma saura na dare mami ta shiga dakin nata,har ta gama shirin bacci tana kwance tana jiran wayar abdur rahim da yace ta jirashi kada tayi bacci zai kira ta,da sauri ta miqe tana maida hularta da santsin gashinta ya sa ta sabule,mamin ta dan bita da kallo qauna da tausat yinta suka lullubeta ganin ta takure ta kasa hada ido da ita gefan gadon ta qaraso ta zauna kusa damaryam don ta dafa gadon bayanta '.dago ki kalleni maryamu,mamanki ce fa''sai taji qwalla na shirin zubo mata nauyi da kunyar mamin takeji,gefe daya hauhi da tsanar abdallah na takura zuciyarta ''ki kwantar da hankalinki abdallah ya yimin bayanin gaskiya,ba laifinki bane laifinsa ne,kuma nayi masa gargadi insha Allah bazai sake faruwa ba kinji,ki i gaba da kame kanki maryam kamar yadda kike,daraja mace da mutuncinta yana tqfin hannunta,ruwanta ne ta riqesu su zame mata abun alfahar ruwanta ne ta wargaza,bazan so wani abu ya shafi mutuncinki ba maryamu don tamkar amana kike a hannu na,ko bayan haka ma unajinki har cikin zuciyata,haka za bazan iya yafewa abdallah ba idan ya maki wani abu da ya sabawa shari'a da mutuncinki,duk abinda kuma nayi nayi ne saboda kare martabarki,ina fata kin fahimce ni?'' gayada kai tayi tana share hawaye ''na gane mami,na kuma gode Allah ya qyara girma da lafiya'' wayar abdur rahim ta katse 'yar hirar da mamin ta fara janta da shi don ta saki jikinta,ganin maryam din taqi dauka yasa mamin ta dago wanda ke kiran ''bari in abku waje kinga ma shikenan ya fanshe ni sai ya qarasa lallashin,ki gaisheshi sai da safe''ta fadi tana miqewa cikin dariyar zolaya,kasa amsawa tayi ta sunne kanta saboda kunya mamin na dariya ta fice hira suke abinsu sosai irn ta masoya kamar sun shekara da sanin juna ''maryam ya kukayi da abban,nasan dai an bani dama ko?'' ta dan zaro ido tana fadin ''wa ya gaya maka,abdul irin wannan zumudi haka''ya marairaice murya ''maryam bani so in rasaki ne inaso a bani dama koda kudine a kawo'' ajiyar zuciya ta saki ''abdul dole dai ai mu danyi haquri ko,tunda yanzun dai kaga azumi saura kwana bakwai,mu bari bayan sallah idan Allah ya kaimu sai ayi dukka abinda za'ayi'' ''wa ya gaya miki azumi na hana kai kudi,akwai cousing dina safiyya hudu ga azumi aka kai kudin aurenta,so pls maryam ki barni na kawo kudin idan yaso bayan azumi asa mana ranar aure na qagu ki zama tawa,baki san ya nake ji ba duk lokacin da na kalleki ko naga kin fita a matsayin budurwa ba mata ta ba,bani da wani iko a kanki'' dariya ta saka ''yaushe ma kake ganin nawa ne abdul'' ''ina iya ganinki mana da idon zuciya'' ''shikenan yanzu mu bari zan sanar da mami na,duk yadda ta kama zaka ji'' da qyar abdur rahim ya barta bayan ya cikata da dad'ad'an kalmomin qauna πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚ Su hudu ne cikin lafiyayyar motar da idan ka shiga ba zakayi tsammani tafiya akeyi ba sai idan kaga kuna wulga gurare,mami ce da maryam a baya sai Abdallah da driver a gaba mami cikin shigar leshi dinkin buba orange wanda yasha adon lemin hreen,takalmi jaka da mayafi dukka toomatch masu dan karen tsada da kyau,ba qarya mami gwanar iya ado ce,ko cikin mata masu shekarunta da wuya ka samu irinta goma,shi yasa sam sai ka rantse bata haifi abdallah ba,zakayi tsammani yayarsa ce kawai maryam ma cikin cikin kwalliyar take amma zamu iya cea kwalliyar jiki don babu wani make up a fuskarta,material ne pich da kwalliyar sea green,tayi adon takalmi mayafi da fashion na dan kunne duka kalan sea green,ba gwanar jaka bace hakan ya sa wayarta ce kawai riqe a hannunta,abdallah dake gaban mota yake ta faman zuba mitar shi kam da an barshi bazaya je ba,ba gun zuwanshi bane idan ba kamawa tayi ba,sanye yake da shadda light blue dinkin tazarce da yaji aikin hannu na maza dan ubansu da baqar hula,takalmi sau ciki baqi da agogo,kallo daya zaka masa ka tabbatar kudin da jikin nashi ya lanqwame ya ishi mai qaramin qarfi jari ''ayita aure gab da azimi barna tayi ta afkuwa''ya fada yana yarfar da hannunshi wanda ke daure da agogon ruwan gold''nikam dai wallahi kam duk wanda yamin aure a irin wannan lokacin alhakin a kansa'' ''baka da kunya ka maidani kakarka,yaro duka ka gama mitarka,dinner ce dai si kaje,minti nawa anyi an gama,hajiya mai gado idan da halacci ba zaka mata haka ba,ita tayi yayenka abdallah,ba qaramib sonka take ba'' ya dan waigo yq dubi mamin ''ayyah mami me ya kawo maganar yaye na''ta dago shi qwarai wai shi baya son raini,dariya ta saka ''to meye kowa ma an masa yaye har ni kaina''kadan kadan take bashi labarin quriciyarsa gidan hajiya mai gadon,yana son ji amma baiso wani ya ji masa ya raina shi don haka ya canza topic din ''mami,cikin kwankin nan nake son kawo miki dear ta gaidaki,so kuma bata nan sunje umarar azumi,ni kuma na qagu mami in yi wani motsi'' murmushi ne ya subucewa mami ''ummm,abdallahhh......,yaushe ka zama haka?yaushe sonta ya maka irin wannan kamun?kai har naji ina sonta data iya sato zuciyar birkitaccen yarona haka ta farat daya'' murmushi yayi hadi da lumshe idonsa,ya jinginar da kansa jikin seat din motar yana tunata yana jin wani yanayi na shigarsa,mami ta sosa masa inda yake masa qaiqayi ''dis luv inside of me is strong mami,there ar no boundaries that it can hide'' Kasa daurewa mamin tayi har sai da ta dan daki kafadanshi ta baya dariya ta kamata,ringin din wayar maryam ya katsesu,abdur rahim ne,kamar ko yausheta kasa dagawa saboda kunyar mami shi kuma bai fasa kira tsaki abdallah yaja yana fadin ''du Alla a kaahe wannan culculator din ya damemu haka nan'' mami ta kalli maryam ''daga kiranki maryam,ba mai jinki hirar mu muke'' tsaki ya kuma j''idan ba zata daga ba asauketa ta kammala wayar ta biyo mu daga baya kota koma gida'' ''shut ur mouth,oya ina jinka,muyi maganar dake gaban mu''cewar mami Minti ashirin tsakani suk iso gun dinner din,ita dai maryam rava idanu kawai take don bata

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138