Chapter 19
Chapter 19
haka'' ''for god sake mami,ni babu wadda fa na taba cewa ina ina so duk cikinsu,yanzu mami anan kinga matar aure,kinga wadda ta cancanci zama surukarki matar danki qwaya daya abdallah,ni ban gani ba mami kuma kema na san baki gani ba'' ajiyar zuciya tayi don ta sani gaskiya abdallan ya fada ''amma wulaqancin bai da amfani abdallah,gwara arabu cikin mutunci da salama'' ''mami ai bani na kawosu ba,kuma ni ba wulaqanci na musu ba,zuciya sukayi suka tafi'' murmushi tayi cikin zuciyarta,idan banda abun abdallah ai kora da hali ka musu,tace cikin zuciyarta ''tunda kace duka basu maka abida faοΌ,itadai nutsatstsiya ce ai ko'' yadan yatsine fuska ''ai nutsuwa kam akwaita,amma ba kamun kai,itama ina tabbatar miki mami gobe ko jibi zaki ganta da uban tana tana sum sum sum,marabarsu kadan ce ai'' ''abdallah abdallah,Allah ya shirya min kai'' ''ameen mami na'' takaici ne ya rufeshi jin sallamar zubaida,ta qaraso tana wani satar kallonshi ''mami barka da dare'' ''yauwa zubaida''filet ya zara ya bude warmers ya zuba abincin ya haura saman mamin abinsa zubaidan binshi tayi da kallo yayin da ami ta dafe goshinta π€¦π½ββ abdallah na bata damuwa da yawa kan yaran mutane ''ya akayi zubaidaοΌ'' maganar mamin ce ta janyo hankalinta daga kallon saman inda abdallan ya haye ya barta ''bab....ba komai mami,cewa nayi dama sai da safe''tace cikin in ina ''Allah y bamu alkhairi,ki gaida nene yau duka bamu hadu ba,insha Allahu zan shigo gobe'' ''zasu ji''ta fice daga bangaren cike da takaici a kwance ta tadda ahi saman three sityer wanda saboda tsahonsa kansa na daya hannun kujerar qafafun na daya hannun har sun zarta sosai yasan qorafi zata yi don haka yayi saurin riga ta ''nidai,mami banji dadin dawowar nan tawa ba sam,duka yaran nan sun hanani sakewa,gaskiya daga yanzu kada wadda ta sake shigowa indai ina nan har sai na fita kawai'' ''to uba na'' dariya yake ciki ciki don yasan tunda ta fadi haka ya quleta ne kuma ba zata sake cewa komai ba π²ππ²ππ²π a fusace huwaila ta fito daga dakin nata,kai tsaye qofar dakin inna hadiza ta durfafa,a fusace ta saka hannunta ta yaye labulen tana fadin ''fito hadiza,wallahi na gaji na wannan iskancin da ake min cikin gidan nan ni da yara na'' inna hadiza dake kwance kan kujerarta da daurin qirji ta miqe ta soma qoqarin zama tare da jawo dankwalinta tana fagamniyar qulle danqararren kanta tare da fadin ''ai ni na girmewa fitowa saidai ashigo a sameni'' ba tayi wata wata na ta gado falon wanda saura ladan ta take qafar binta dake kwance saqe saqe,tayi saurin janye qafar tata tare da fadin ''Allah ya isa na wallahi''saidai bata ji ba kasancewar cikin masifa take da hayagaga ''hadiza,ki jawa diyarki binta kunne,iskancin da take cikin gidan nan ya soma isata,haka kawai sai ta kama lubabatu ta dinga jibga,babu dama ta dauki aron wani abu nata'' ''ahaf,kince haka kawai sannan kin dawo kin warware maganarki kince tana daukan aron abun ta,to ke da ita ku bude kunnuwanku da kyau,indai lubabatu bata daina daukar aron kayan binta bazan hana binta jibgarta ba,wutsiyar raqumi ai tayi nesa da qasa,mu yanzu cikin gidan nan babu sa'an mu don arziqi ba qarya bane'' kallon tara saura huwaila tayi mata,kana ta saki guda ''aikin banza....hara ra aduhu,arziqin nan fa da kike ta taqama da shi a sa hannuna ya samu,amma da yake butulu ce ke had kina da bakin goranta min,baya ga butulcin da kullum kwanan duniya kike min na hanani morar duka wani abu da jamila ta kawo cikin gidan nan,to bari kiji wallahi ki bini a hankali,don wallahi duk abinda kike taqamar da shi a yau idan naso sai na warware miki zarenki tas ta yadda baki isa ki maidashi ba'' hindatu dake parlour tana yiwa mama tsifa ta dubeta ''mama...kunnenki yana jiyo miki abinda nake ji kuwaοΌ'' duk da cewa,zamcan ya duketa amma sai tace ''ina ruwanki hindatuοΌmanzan Allah yace yana daga cikin kyawun musulincin mutum ya bar abinda babu ruwansa''gilma na cin hindatu amma dole haka ta ja bakinta tayi shiru tana addu'ar Allah ya kawo mata ya maryam,kai qila ma sai ta kira ta ayau din cikas din kawai mama da zata hanata sai kuwa inna hadiza ta hauro itama huwailan dake kusa ta bi mata,sai fada ua zama hudu,binta nayi da lubabatu,huwaila nayi da hadiza ,mama ta yunqura zata fita bada haquri hindatu ta tareta tace wallahi mama babu inda zaki,lokacin da suke 'yar dadin babu wanda auka dauka abanza ieinki saboda haka yanzun ma ba ruwanki,su kashe kansu''a haka malam mamuda ua sjigo ya tadda gidan nasa zancan ya bibiya amma daga qarshe sai ya goyawa inna hadiza baya,ko dama can itace mowar,balle yanzu da jamila ke satowa tana kawowa uwarta ita kuma take yagar masa,bayan sun shige daki ba qaramin ciwo abun ya yiwa huwaila ba,ta cizi yatsa yafi sau ashirin,lubabatu dake tsaye tana taya uwar tata takaici tace ''wallahi huwaila duk ke kika ja mana tun asali,da tuni nice kan matsayin jamila kika tsaya gina wasu kika qi gina kanki,ai da arziqi,a garin wasu gwara a garinku a garinku ma aunguwarku a unguwarma agidanku a gidanku ma adakinku'' ''duk banga haka na lubabatu sai yanzu,nayi dana sani wallahi yafk a qirga,tsinanniyar mata ta kuma samun power a gidaοΌ'' ''ato,shawara dai ta rage ga mai shiga rijiya,saiki zauna ki tuna bunyi'' kamar tayi mata allura ta figo mayafinta dake ajjiye saman qofar falon ta tace ''kinga zauna ki jiremin daki na,ba'a bori da sanyin jiki,bari naje gidan talatuwa'' saman tabarmar dakin ta zube tana fadin ''sai kin dawo''cikin zuciyarta tana addu'ar Allah yasa adace,tuni ta fara hango kanta a irin daular da jamila ke ciki,tana yin son ranta wanda tuni an maida jabir wani sususu,aure dai an yishi amma amma fa na cin abinci da cin kayan dadi da dibar kudi *mrs muhammad ceπ* πππβπ»βπ»βπ» [9/17, 12:51 PM] 80k: πππππππ πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πΊ *ABADAN*πΊπΊ πππππππ πΊππΊππΊ πΊππΊπ πΊππΊ πΊπ π πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ πππππππ *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* πΊππΊππΊππΊ ππΊππΊππΊ ππΊππΊπ ππΊππΊ πΊππΊ πΊπ πΊ βΆ1β£7β£ sama sama hadarin ke hadowa yana bajewa tun daren jiya,hakan ne ya sanya har safiyar yau garin yake da lullumi,lullube sama take da hadari mai duhu saidai sanyi sanyi yake bayarwa har yau ruwan bai kai ga sauka ba,qarfe goma ta kammala komai,wankanta tayi ta shirya cikin pskistan riga da wando daya daya daga cikin tsarabar da raliya tayi mata ta south africa,orange ne wanda aka yiwa adon dutsina dark blue daga gaban rigar da qafar wandon mayafinshi shara shara ne amma yana da dan girma shi ta saka ta yane kanta da shi,tun baiwai yau mami ta fita saboda ta cinye hutunta na kwanaki ukun saboda haka bangaren babu kowa sai ita daya,kusan tunda tazo gidan bata fita ko ina ba saboda hala tayo sha'awar dan zagaya wa,wayarta na hannunta ta saka flat shoes ta fito iya girma gidan yana da shi,ba ma wannan ba yanayin ginin ya burge maryam,bugu da qari yanayin da gafin yake ya qarawa maryam nishadi,lokaci gida hadarin ya yaso garin yayi duhu sosai,cikin qanqanin lokaci iska ta taso ruwa ya kece da sauri sauri take nufar hanyar sashen nasu don bata son ruwan ya tabata,su uku me ysaye a waiting parlour din,nene zahariyya sai wani
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138