Skip to content

Chapter 42

Chapter 42

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,278 words 0 views Progress saved
Download Book

saba zuwa ire iren guraren ba,bata da wannan rawar qafar sam,da dai su jamila ne su lubabatu tof babu na biyunsu uwar taron dakanta ta fito ta taresu ''masha Allah hajja bintu ina kika samu kyakkyawar diya haka,ko surukar taki ce'' murmushi tayi ta wauwaya ta kalli maryam da abdallah dake bayanta,sai taga sun mata kyau din kuwa tamkar wasu couples,abinda bata taba kawowa a ranta ba ta jishi lokacin,sai taji tana fadi cikin zuciyarta ina ma da gaske ne haka dinne,ya waiwaya ya danqarawa maryam harara sai akayi sa'a suka hada ido,ya dan matso gab da ita har tana sheqar qamshinsa kana yayi qasa da murya kamar mai fada mata abun arziqi ''yi gaba mamalama,kin wani jera da muta ne kamar sa'anninki,salon 'yan jarida su ganmu tare ki samu daukaka ni kuna ki bani kunya'',itakam tsoronshi take don neman tsari take da shi hakan ya sanya batare ce masa komai ba tadan ja da baya da yake ya fita sauri tuni ya dan zar tata mami ta kalli hajiya mai gado ''diyata ce ita din ma,amma surukar naku na zuwa insha Allahu,don shekaran jiya yaron naki ya min albishir,ya gama ruwan idon nashi da bani kunyar gun iyayen yara'' ''a'ah,a qyale yaro na,ai lokacinshi ne a barshi ya zaba ya darje,ai ya cancanci yin hakan'' ''um um kada ka ki fasa masa kai'' ''ba zancan fasa kai sai tsabar gaskiya''da daddan hirarsu irinta qawaye suka iso gurin da ka tanada don baqi na musamman irinsu anyi kiran iyayen amarya suzo su nuna tasu karar don haka mami ta miqe,ta dubi abdallah dake ta faman shan qamshi idanunshi na kan waya tunda sukazo ''bari muje nida martmyam liqi yanzun zamu dawo,kaima ya kamata ka qarasa ku gaisa da amaryar'' ''ina zan iya tashi an cika guri da sakarkarun 'yammata marasa kamun kai,duk inda ka motsa suna kallinka kamar wasu mayu'' ''kaji da shi dai,kallo kuma kayi abun kallin ne dole a kalleka,dukka abokan ango na gun stage suna liqi kaja ka zauna bayan kaima abokinka ne''mamaki ya cika maryam,yadda taji ana tababa da shi kan bazai je ba tayi zaton ma bai sanshi bane ''mami ni bazanje in kalli matar wani ba don nima babu mai kallarmin tawa'' ''haka za'ayi naka bikin kenan kana nufin'' ''ko za'ayi mami ba zata zo min da irin shigar da amaren yanzun suke ba,sai babballata in zubar'' hade rai mami tayi ''to ni kuwa bazaka balla 'yar muta ne ba ka barmu da jidali ba ka canza tunani'' murmushi ya subuce masa ganin yadda mamin ta hade rai kamr ma ya riga da ya aikata miqewa yayi ya karbi jakar hannunta yana dariya ''Allah ya barmin ke mamata ni daya,muje in rakaki,Allah ya huci zuciyar hajiyata'' ''hutsu ne abdallah''maryama ta fada cikin zuciyarta,suna hada ido ya daka mata harara ya kuma hade rai qyam tamkar bashi yake murmushi yanzun ba a baya suke binta har suka isa atge din,ya miqawa mami jakar yana fadin ''gashi mami,ayi liqi a hankali'' ''haba handsome,girman mami ne ai ta liqa ko nawa take so,babu ji tunda tana da kai''maryam da abdallah suka kalleta lokaci guda don mami bata ji ba tuni da kutsa ciki,wani sakaran kallo yayi mata gami da jan tsaki,ita dai maryam gaba tayi tana qoqarin bin sahun mami tana fadin cikin zuciyarta ''kin debo ruwan dafa kanki'' ji tayi an riqo tsintsiyar hannunta gam ana janta,babu shiri ta waiwayo abdallah ne tuni har ya fara tafiya,tilas ta saita wa kanta hanya ta bishi a baya tamkar raqumi da kala,don idan tayi tirjiyar bin nasa zata iya zubewa a qasa don da sauri yake jan nata bai saketa ba sai da suka iao teburin na su kana ya sakar mata hannu hadi da yi mata nuni da kujerar data tashi dazu a kai,tsareta yayi da idanunshin nan masu kaifi ''sit,dake aka hada kutingwilar zuwa na nan,shine kuma duka zaku fashe ku barni zaune ji daya kamar yaron mayu,ki zauna ki kula da ni har mamin ta dawo ta karbeki,daga nan ma idan club zaki wuce ke ya shafa'' Tuni hawaye sun cika idanunta,bata ce masa komi ba ta zame ta zauna,shi kuma yayi tsaye hannayenshi harde bisa qirjinsa yana qarewa gun kallo tamkar mai neman wani matashin saurayi ne yake dosowa gurin,kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewa ya gogu cikin duniyanci,sannu a hankali yake qarasowa har inda maryam din take,shigowarsa gurin kenan idanunahi sukayi tozali da ita,totally ta gama yi masa fatanshi daya 'yar hannu ce,zai iya kashe mata ko nawa ne matuqar zai samu hadin kanta,ta bayan kujerarta ya zagayo yasa dukka hannayenshi ya dafe makarin kujerar ''hello babe...'' gabanta ne ya yanke ya fadi,har ta kasa jiyowa taga ko waye,ga zatonshi bata ji ba don haka ya ranqwafo bayan nata yana shirin sanya hannunshi ya dafa kafadunta cafkar da yaji an yiwa hannunshi yasan bata wasa bace,tamkar tarko ya kama bera haka abdallah ya riqe hanun nashi tsam,bai gama qarewa abdallan kallo ba yaji saukar lafiyayyun mari guda biyu da suka gigita shi, hannu abdallah yasa ya yaye dogon hannun rigar t shirt din dake jikin saurayin,take wasu yan qanan rubutu da suka fi kama da na 'yan china suka bayyana a saman tsintsiyar hannunshi,a tare suka kakki juna ahi da mataahin tashin farko tsoro qarar ya bayyana idanun matashin,motsin da matashin ya fara yi da daya hannun nasa da abdallan bai riqe ba yana qoqarin cusa hannunshi aljihun bayan wandonshi ya ankarar da abdallan,cikin hanzari ya dunqule hannunshi ya daki hannun matashin take ya sagar masa da duk wata jijiya da zata taimaka masa ya iya motsa hannun,ya zura hannunshi aljihun matashin ya ciro 'yar qaramar bindiga ya cillata cikin nashi aljihun,qarar da ya saki ita ta janyo,hankalin mutanen dake kurkusa da su,cikin zafin nama da qwarewa da hannu daya ya tsinke duk wani maballi dake jikin t shirt din matashin ya finciketa daga jikinsa hade da juyo da bayan matashin ya kalla,zane ne kala kala a jiki wanda ba lallai kai ka iya ganewa ba ''anaconda isnt it?um?yaron alhj hamza mai qusa'' Abdallah ya fada bayan ya zagayo gaban matashin sunyi face to face,hannunshi daya ya sanya a aljihub rigarshi ya ciro qaramar wayarahi keypad qirar samsung,cikin qanqanin lokaci ya bada order turo ma'aikata inda suke din kana ya maida wayar aljihunsa,idanunshi qyar cikin na matashin yake tambayarsa ''ku nawa ne agurin nan?''shiru ya masa babu alamun zai amsa masa,hakan ya bawa abdallah damar yin tsai yana karantarshi,ba tare da matashin ya masa nuni ba ya karanci tabbas akwai abokin tafiyarsa ahannun daman abdallah,sai kuwa akayi dace shima ya yunquro da niyyar kubutar da dan uwanshi,duka daya abdallah ya waiwaya ya masa a dokin wuyanahi ya zube a qasa yana malelekuwa. minti goma kyawawa basu cika ba jami'an ss suka iso gurin ya damqa musu su yace su kira jamal hussain ya fara aiki a kansu kafin gobe ya iso office din,mutanen dake gurin kam kowa godiya yake ma Allah suna fadin Allah ne kadai yasan me zai faru badon zuwanshi ba,sai da koma cikin mota ya kira mami yace suzo su taci don baya son,jama'suci gaba da shaida fuskarshi ko cikin motar tamkar kace ket maryam ta zura a guje take ji,tsoron abdallah ya kuma cikata,ya dubeta da madubin

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138