Chapter 78
Chapter 78
rafin ya debeta tayi baya luuuu zata koma cikin ruwan ''maryam!'' muryar abdallah da take a shaqe ta daki dodon kunnenta ba zato babu tsammani,cikin ikon Allah ta turje bata kai ga fadawar ba ta dawo gaba ta kwasa a guje ta dira a gabanshi cike da tsananin mamaki,ko ina na jikinta rawa yake,sai hawayen idonta da take ta yiwa waigi ya balle baki daya,ta rasa me ma zata yi,hawan mero tayi da bala'i ta inda take shiga bata nan take fita ba,dn me tana gani zata barshi ya fado akan me?,duk masifar da take taqi kallonshi yayin da ahi kuma ya zuba mata ido yana karanta al'amura da dama daga gurinta ''shshshhhhh''din ta taji yace yasa ta rage masifar da take, a hankali a hankali,daga qarshe taja bakinta tayi shiru ''ki taimakamin na koma kan kujerar tukunna madam'' ya gaya mata karo na farko taji,muryarsa ta fita sosai,wani abu taji yana ratsa ta tako ina. har yanzu jikinta bai bar rawa ba don haka qarfinta ya gaza kaiwa har sai data haqura mero ta taimaka mata suka maida shi,bata sake cewa komai ba ta soma turashi suka fara barin gurin tana goge qwallarta lokaci lokaci,ta kasa tantance yanayin da take ciki,gaske ne koko mafarki,yau abdallah ke magana da bakinshi?. Dab da zasu fara shiga cikin mutane taji yace ''bai kamata ki shiga cikin mutane kina kuka ba ko?,dakat kadan ki daidaita yanayinki'' bata qi shawararshi ba ta tsaida wheelchair din din ta ciro dankwalin atamfarta ta goge fuskarta kana ta maida dankwalinta,amma maimakon hawayen ya tsaya sai wasu sabbi,ma dake bulbulowa har mero ta iskosu ya limshe ido ya maida bayansa sosai ya kare da kujerar yana fadin ''ya salam,to me aka yi miki?,idan don warkewar baki na ne ai godiya zaki ma Alah ko,tunda dama shine mai kowa mai komai,idan kuma don fdowar da nayi ne ai gani sumul,ba ba abinda ya gutsireni mijinki baiji ciwo ba'' batasan ta harareshi ba sai data ji yace ''maida idon kada kija min asara,don ba qaramar asara bace idan na rasa wadann nan golden oily eyes din ba''. A nutse suka ci gaba da tafiya kamar yadda suka zo,saidai canjin yanayi da aka samu,a dazu mero keta faman zuba cike da farinciki abunta abdallah na kalle kalle babu bakin magan,wannan karon kuwa tasbihi hailala da salatin annabi ke fita a bakinshi zalla,yayin da maryam ke cikin wani irin yanayi,jin ta take kamar an rage mata wani nauyi daga cikin nauyin da aka azawa zuciyarta,mero kuwa amsa kuwwa muryar abdallah ke maya cikin kunnenta,dadin muryar ya kasa barin dodon kunnenta,tsabar kulawa da qauna da take iya hangowa daga dukkan kallo da ikin abdallah da kewa maryamu,da gaka suka qarasa gida ana qwala kiran sallar magariba. *mrs muhammad ce*👑 📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽 [7:29pm, 9/25/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 🌺 *ABADAN*🌺 💖💖💖💖💖💖 🌺🌺🌺🌺🌺🌺 💖🌺💖🌺 💖🌺💖 🌺💖 💖 *WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* 🌺💖🌺💖🌺💖 🌺💖🌺💖 🌺💖🌺 💖🌺 💖 © *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *_home of expert and perfect writers_* 4⃣7⃣ *_Manzan Allah S A W yace:shaidanu suna nisantar gidan da aka karanta suratul baqra a cikinsa har na tsawon kwana uku_* *_mala'iku sukanyi duba izuwa sararin duniya,yayin da suka kalleta suna hangota ne baqiqqirin basa ganin komai face hasken gidaje ko guraren da ake karanta alqur'ani a cikinsa_* A bakin murhu suka tadda inna wuro tana kwashe tuwo,sallamarasu ce ta janyo hankalinta bakin qofar shigowar ''kun dawo kenan mer.....'''sauran maganar ta maqale wa inna wuro ganin har da abdallah cikin masu sallamar,marar hannunta da take kwashe tuwon ta saki ta miqe tana fadin cikin dafe qirji ''Allah qaadiran ala mai yasha'u,bawan Allah?''ta fada tana kallonsa tare da qarasowa gabansu. murmushi yayi yana kallon innar ganin ta kasa magana ''babu mamaki cikin ikon Allah inna,nine da bakina nake magana,yau Allah ya amince min'' kiran sallar magariba ya katse su ''inna muyi sallah tukun''ya dubi maryam dake tsaye guri daya tana faman goge qwalla lokaci zuwa lokaci ''gimbiya a dauran alwala,inna ki mata magana tun dazun nace tabar kukan nan taqi''inna wuron dake daura da maryam din ta dafa kafadarta ''haba meramu,farincikin da zaki nunawa ubangiji shine ki masa godiya ba wai kika ba,share hawayenki ki daurawa mijinki alwala'' ''to inna''ta fada cikin rawar murya tuni har mero ta debo ruwa cikin buta tazo gaban abdallan ta ajjiye ta koma bakin rijiyar ta ja wani ta fara daura tata alwala,dukkansu nan bakin qofar dakin innar suka shimfida karauni biyu sukayi sallar magaribar,shiru ya ratsa tsakar gidan kowanne na tasbihi cikin zuciyarshi banda mero da moysa bakinta kawai takeyi duk motsin abdallah ta cikin hasken qwan solar na kan idonta,har maryam ta fuskanci haka,dauke kanta tayi don ji da tayi ranta na aon baci taci gaba da tasbihi da yatsunta. Ranar har sha daya na dare suna zaune suna hira,hiransu suke sosai shida inna wuro da yake jinta kamar maminshi. Yana jin kewar mamin nashi sosai har bazai iya fadar adadi ba,mero ma tsakiyarsu tana sanya musu baki yayin da maryam taja bakinta ta tsuke,lokaci lokaci abdallah yana satar kallonta,ji yake tamkar ya jawota jikinshi ya rungume ko ya shiga zuciyarta ya jiyo damuwarta,shirun nata bai masa dadi sam,don haka sha daya na cika yace da inna wuro yana jin bacci zai kwanta ''nikuwa kamar mu kwana nan hirar yau tayi min dadi abdullahi,gashi yau kaima da bakinka akeyi da kai''mero ta fada yana kallonshi baki a washe,murmjshi kawai yayi ya girgiza kai,bata bar gidan ba sai da taga sun shige dakin kana ta waiwayo ta yiwa inna wuro sallama ta fice cike da jin dadin jin daddadar muryar abdallah da yau ta morewa. sanye yake da jallabiya milk mai gajeran hannu yana zaune saman katifar tasu hannunahi dauke da qaramin al'qur'ani,daya hannun kuma riqe yake da wayarshi ya kunna torch din yana haskawa,ya sake satar kallonta sha biyu har da kwata amma bata da niyyar kwanciya,hakanan kuma ta kashe musu qwan solar dakin saboda ta lura da yadda yake ta nacin kallonta,tana zaune dirshan bisa dadduma sanye da hijabi da carbi a hannunta tana ja,ya saka zare kan shafin da yake na karatun qur'ani ya shafa addu'anshi,ya tabbata koya kirata kam ba zuwa zata yi ba indai ba cewa yayi yana buqatar wani abu ba. ''madam,a ataimakawa bawan Allah da ruwa mana''ya fada murya qasa qasa kamar mai rada har yasa tsigar jikinta tashi,ta ajjiye carbin kana ta miqe ta isa inda catoon na ruwan gora ke ajjiye ta ciro daya tare da cup ta hawo gadon,ta tsiyayo ta sake matsowa gabanshi ta miqo masa,jadawa yayi harda hannun nata ya riqe gam yana son saka qwayar idonshi cikin nata,ta soma qoqarin qwace hannun nata saidai ta kasa garin hakan har fiye da rabin ruwan ya zube a katifar. Ta dago da niyyar dubanshi idanunta cike da qwalla da ya rasa ta meye,take idanunsu suka hadu,da sauri ta janye nata idanun don bata iya dauke nauyin idanunshi cikin nata ''ka sakemin hannu kaga duk ka.....'' ''bazan sakeki ba,sai kin gayan meke damunki,tunda bakina ya budu baki,barni nayi magana da ke ba sai wasu ke tayani hira?'' ta sake kau da kanta kana tace ''to me kake so muce ko ince maka ne?'' ''bana tunanin baki san me zaki gayan ba maryam,nasha hango maganganu da dama boye cikin idanunki,kin hana bakinki ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138