Chapter 23
Chapter 23
amsar da zata bawa mamin ''Allah ya tsare gaba to,amma ya kamata ka daina zuwa gun da ta samekan,don nasan bazai wuce cikin garden ba''ta fada tana hada allurai cikin syringe maryama tsayawa kawai tayi tana kallon yadda abdallan keta marairaita kamar qanqanin yaro,ita abun ma kunya ya dinga bata,amma shikam ta fuskanci ko ajikinshi wai an tsikari kakkausa ''wannan matarshi zata sha fama da shagwaba,mami duka ta sangartashi''tayi gulmarshi cikin zuciyarta,da sun hada ido sai ya maka mata harara hakan ya sanya ta dauke kanta ta maida kan dan wani qaramin frame me masifar kyau dake kafe kan table din mamin,hoton wani yaro ne wanda bazai haura shekaru takwas ba cikin shigar tazarce da hula da takalmi sawu ciki,ko shakka babu wanna hoton abdallah ne lokacin quruciyarshi,kyawunshi ba loka in girmanshi ne kawai ba kyawu ne na tun usuli ya lura hoton take kallo don haka ya miqa hannu ya tuntsurar da shi,ya dan bada qara sakamakon haduwarshi da table din har sai da mami ta dago ta dubeshi sannan ta dubi frame din,ta fuskanci abunda yake nufi don haka murmushi kawai tayi can qasan ranta taci gaba da abunda take bayan mamin ta kammala bashi duka wani taimako na kashe radadi da kuma tsaida dafin sai ta hada mishi da magani,minti goma tsakani mami tace ya taahi su wuce amma sai ya marairaice kan cewa bari ya huta,wayarshi dake gefan system din mami ta dauki kida,kamar bazai daga ba amma yana dubawa yayi hanzarin dagwa ''sir,munga alhj haladu uba mai qusa yanzu cikin asibitin nan''abinda aka fada kenan da ya sanyashi hanzarin miqewa,mami ta dubeshi ''lafiya abdallah?'' ''mami ina zuwa,just twenty minute''bai tsaya sauraron komai ba ya fice daga office din,yayin da mamin ta bishi da kallo cikin ranta tana masa addu'a,ita kanta mqryam din binshi tayi da ido cikin mamakin me ya sanya masa kuzari haka lokaci guda,mutumin da anyi anyi ya tashi a tafi gida ya qiya?ya tsaya shagwaba shudewar kusan sa'a biyu har mami ta soma nuna damuwa sai gashi ya dawo,zufa duka ta wankeshi,cikin kulawa mamin ta dubeshi ''lafiya dai abdallah?''ta sake tambayarshi karo na biyu ''mami na samu nasarar kama alhj haladu,saura alhj hamza naira''ya bata amsa yana tsiyaya ruwa mai sanyi cikin tambulan na glass ba mami ba,hatta da maryama dake zaune can gefe ba qaramin burgeta yayi ba,tana tsammanin dazun nan taji uana zancan neman mutumin amma har ya sami nasarar cafkeshi cikin abunda bai gaza awa daya da rabi ba,fuskarta qunshe da madaukakin murmushi take fadin ''masha Allah masha Allah,lallai dana daya da daya ne,baka tsinta aqasa ba abdallah,fata na Allah ya tsaremin kai yaci gaba da yi maka jagora,ya baka ikon ci gaba da tsayawa akan gaskiua,ya rabaka da aikinka lafiya'' yana kurbar ruwan sanyin yana ratsa qwaqwalwarsa sannan sanyin dadin addu'ar mahaifiya na sake shigarshi ''ameen ummi na,kullum addu'arki ita ce sirrin nasarata a rayuwa'' cikin mintina gona suka bar asibitin harda ummin don lokacin tashinta yayi Sashensa ya wuce mami ta haura sama itama don kintsawa yayin da maryam kuma ta koma kitchen don kammala masu abincin dare tunda tuni an fara ahirye shiryen kiran salla,fashin sallar da take ne ya bata damar ci gaba da ayyukanta shigarta kenan ta kunna gas tana shirin aza tukunya samanshi taga kamar anyi wuf an fice daga kitchen din,da sauri tabi hanyar fitan itama tana dube dube,bata ci nasarar ganin kowa ba sai adnan yayan zubaida dake shigowa cikin waiting room,wanda sairan qiris suyi karo da shi tayi saurin ja baya atsorace kallo yake qare mata hade da wani shu'umin murmushi wanda hakan ya sanyata ta tsargu,ta tsani namini mai kallo don a aqidarta takan fassara mutum ne kawai da dan iska ''yi a hankali mana baby kada ki jiwa wannan kyakkyawan jikin ciwo ko''babu abunda tace da shi sai juyawa da tayi cikin sassarfa ta koma kitchen shi kuma ya mata rakiyar idanu,sai da ta bace ya wani lashe labba kana ya shige bangaransu nene tayi saurin damqo wuyan rigarshi don ta fuskanci baima gansu ba a inda suke labe ita da zahariyya suna gano farfajiyar waiting parlour wucesu zaiyi,a razane ya juyo ''banza solobiyo kawai,harka wani tsorata,amma ka iya tsayawa kana qarewa jikin yarinya kallo'' kansa ya shafa yana fadin''to ai nene ba laifi bane'' ''kaga ni ba wannan ba,kaga alamun yarinyar nan ta fuskanci an shiga kitchen dinsu ne?'' ''eh to,ni dai na ganta a gurguje da alamu wani ta biyo'' ''hanyar ina kaga tayi?'' ''hanyar valcony'' ajiyar zuciya nene ta saki ''Allah na gode maka bata ga ko waye ba,kuma da alamu bata fuskanci komai ba'' ''ya?nene?''adnan ya tambaya yana dagawa uwar gira ''mun aiwatar da aikin mu,saidai mu jira sakamako kuma,indai kuwa sakamako yazo da kyau,to mafarkin kowannen mu ya gama cika,don wannan karon indai aikin mu yaje inda ake buqata to babu makawa burinnu sai ya cika'' tsallen murna yayi ''that's why nake sonki nene,amma....'' ya katse maganar jin takun saukowa daga saman bene,zubaida ce,itama dubansu tayi kamar yadda suka dubeta,ganin yanayin fuskartq bai sauya ba ya tabbatar musu bata ji komai ba,gurin t.v ta nufa ta kunna sanna ta kamo tashar da take da buqatar kalla ba tare da tace da su komai ba,haushinsu duka take ji don dazun sun dqn haura sama kan yadda take son abdallah yana yarfata _kuyi haquri da wannan sakamakon na wuni gurin mama na da bata jin dadi sosai,muna buqatar addu'o'inku,na gode_ *mrs muhammad ce*👑 📚 📚📚✍🏻✍🏻✍🏻 [9/17, 12:52 PM] 80k: *ABADAN*20 *WRITTEN BY* *SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA* Gab da isha'i ta kammala tuwon semovita miyar busashshiyar kubewa,kan dining ta jera konai yayi net sannan ta barwa baba uwani gyaran kitchen kamar ko yaushe ta shige bedroom dinta,wanka tayi ta shirya cikin atamfa doguwar riga ta haye gadonta don ba salla zata yi ba research ta shiga yi kamar yadda al'adarta take lokaci bayan lokaci idan ta samu kanta free kamar yanzun takwas da rabi da mintina hudu kiran mami ya shigo wayarta,a ladabce ta daga ''maryamu an kammala abinci ne?'' ''eh mami na kammala'' ''ok,taimaka don Allah ki shirya abincin cikin folding basket ki kawo nan sashen abdallah anan zamuci,nazo bashi magani kuma ya ruqeni'' ''to,amma mami ban san inda saahen yake ba'' ''idan kika fito cikin balcony gefen hannun damanki zaki miqehar sai kinzo qarshenta'' ''to gani nan'' tsaf ta shiryasu cikin basket din mai kalan ja da fari,hijabinta ta zura mai hannu ta sanya slipper ta dauki basket din ta fito a hankali take taka balcony din tana sake qara kallonta don bata taba yin area din ba tunda tazo gidan,sai taji kamar kada tafiyar ta qare saboda dadin da yanayin yayi mata,iskace take busawa mai mai sanyi hade da qamshin qasa wanda hakan ke alamta lallai yau wani sashe na cikin garin kano yana samun saukar ruwan sama,kasancewar shigowar yanayin damina,duk da cewa har yau tasu area din basu samu ruwan ba saidai yawaitar haduwar hadari da bajewarsa Qiris ya rage ta bangajeta Allah yasa tayi saurin cin burki,zubaida ce tsaye a gabanta tana huci,a zaton maryama bata da case don ita don haka tayi qoqarin gewayeta ta wuce,binta ta sakeyi ta sha gabanta ''lafiya?''maryam ta tambayi zubaidan cikin sanyin nan nata ''kiyi qoqarin kame kanki daga cikin lamuran abdallah,don na fuskanci wani
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138