Skip to content

Chapter 108

Chapter 108

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,295 words 0 views Progress saved
Download Book

zauna tana tuna abubuwa masu yawa a wancan lokacin,tasha ganin abubuwa masu yawa da suka sa ta dinga jin tsoro har take ganin ko jinnu gareta Wayarta dake silent taga tana haske,ta miqa hannu ta daukota daga gefan pillow,baquwar number ce,sai data daga kai ta kalli agogo qarfe sha biyu da minti goma sha biyar na dare ,ta maida kanta kan wayar tuni har kiran ya tsinke,tana shirin maida wayar wani kiran ya sake shigowa,da tayi kamar ba zata daga ba daga qarshe ta daga din ta kara a kunnenta kana tayi shiru don tantance waye ''assalamu alaikum''muryar abdallah ta daki dodon kunnenta,kasa zama tayi sai ta sulale ta kwanta ruf da ciki saman gadon saboda wani makami da ya aikowa zuciyarta,sake maimaita sallamarsa yayi wanda wanann karon sai da ta lumshe idanunta,lebanta ne suka amsa ba tare da ko wane harafi ya fita ba ''baby nasan kina jina,zuwa yanzu na tabbatar kin karanta saqona''itama so take ta dan rama ko yaya ne kafin ya dawo kano,muryarta low sosai wanda ko kai dake dakin babu lallai kaji me take fadi ''ban duba ba,don bani da time na duba takardu''murmushi ya saka mai sauti da wata 'yar shashsheqa wanda har sai da ta jiyo shi,tsigar jikinta ta zuba ''baby,baby,baby,kullum kina yiwa kanki qarya me yasa?,i know tuni saqona ya isa,ko kice eh ko kice a'ah,na kira ne dama naji muryarki ko zan iya bacci,sai nakejin dama mu koma qauyen ni'ima muyi zamanmu,atleast acan zamu dinga kwana daki daya,idan da rabona ma sai in kwana cikin ni'imtacce jikinki,baby na kasa mance moment namu na dazun ina jin kamar ya dawo,i want feel you beside me,i want to feel your lips......on my neck and.....baby i want.... Iwant''ya fadi kamar mai tsoron magana ''i want to run my head along your chest,kiss your lips....''ai bata iya jumurin sauraronsa ba ta katse kiran nasa ta jefa wayar gefanta bayan ta tsura mata ido Tana kallin kiran nasa amma bata jin zata iya dagawa yaci gaba da horata babu gaira babu dalili,shi dole sai ya tada zaune tsaye,sai da ya hada mata missed call kusan goma sanann ya haqura,qarfe saya da kwata ta sauka a gadon ta shiga bandaki ta daura alwala tayi nafila raka'a biyu ta kwanta,tunani ne fal kwanyarta ta kama wanann ta saki wancan,cikin haka tunanin mero ya fado mata,sai taji ranta ya baci,tana son sanin haqiqanin me tsakaninsa da ita kafin komai ya daidaita,a uziyya tayi ta kori tunanin daga ranta don haka dabi'arta take bata kwana da kowa cikin ranta 🍃🍂🍃🍂🍃🍂 Ta makara sosai gun tashi kuma mami bata tayar da ita ba,bakinta ta wanke da fuskarta ta fito falon bata tadda mami ba sai baaba uwani tana ta gyara kitchen,nan ta tsaya sunq gaisawa har mamin ta sauko,tayi adonta cikin dogowar riga mai zubin buba saidai ready made ce wannan,bayan sun gaisa mamin ta gaya mata ta shirya hajiya laila na zuwa anjima zata fara mata gyaran jiki,ita gaba daya kunya ma kamata take duk da ta sani mami bata dauketa suruka ba amma akwai kunya tsakani,ta amsa mata da to sannan ta koma daki. Ta daura towel tana shirin shiga wanka saqo ya shigo wayar sai ta dawo ta duba,number din dazu ce wadda ta tabbatar ta abdallah ce ''baby jiya kin kusa kasheni wlh,sauran qiris na gayawa mami yadda kike gara mata yaro,ina gaya miki damuwa ta kika gudu kika barni,me yasa baby?,i need your help baby'' bata shirya ba amma sai da murmushi ya subuce mata,ya tuna mata ma,take ta kira mamanta,hira sukayi sosai wadda ta qara mata kewar gidansu Cikin kwanakin gyara sosai maryam kesha wanda ko bazawara aka yiwa hakan sai ta tsere ma sa'a,itadai maryam nata ido,wannan qauna da mami kewa abdallah ba kadan bace 🍃🍂🍃🍂🍃🍂🍃 Zaune suke su biyu cikin fallen dakin nata wanda yafi kama da kango,idan ba kyakkyawan sani kayi mata ba zaka tsammaci mahaukaciya ce sabun kamu,tuni ta saje da su tabi sahunsu kamar yadda habiba ta shaida mata,ta tsotse ta rame kamar wadda kullum ake diba ana kada miya,ga uban ciki a gaba ya fito yayi tsororo kamar dosana shi akayi babu kyawun gani. ''yanzu habiba babu wata hanya kenan ta kubuta''ta tambayeta cikin damuwa ''bana zaton zahariyya akwai'' dariya sukaji ana babaka musu a razane suka daga kansnsu,malam na hayi ne tsaye bakin qofar dakin yana shigowa ''kuna batawa kanku lokaci ne amma babu wadda ta isa ta kubuta daga gareni,mutane ne ku masu son zuciya,kun bijerewa Allah kuna neman biyan buqatarku kan wani mummunan qudiri naku,yadda kuke da baqar zuciya nina haka nake,kunga kenan zamu je ta tadda da mujemu,a sannu sannu mata ire irenku zasu ci gaba da shiga masibu kala kala,walau a nan duniya ko a lahira,irin mu muna nan da yawa Allah ya ajjiyemu saboda ire irenku,haka gaba dayq mu da ku kuma sai munje lahira za'a hukunta mu baki daya,ni dama na riga na sani bani da rabo a lahira,kunga ai gwara naci nawa tun anan''ya juya ya fice yana sheqa dariyarsa. Hada kai sukayi suka fashe da kuka kowacce da irin tata nadamar,sun qi Allah bayan ya musu ni'ima,idanunsu ya rufe basu ganin baiwar da yayi musu da tarin ni'imominshi a garesu sai yanzu da ya karbe abinsa,dama ya fada cikin littafinsa mai tsarki''idan kuka gode min zan qara muku,idan kuma kuka kafirce to haqiqa azabata mai tsanani ce'',sun yarda sun dauki hudubar shaidan,wanda dama bashi da burin da ya wuce batar bayan dama ya sani cewa tun can dama shi batacce ne,kuma dama yayi wa Allah alqawari sai ya batar dq bayinsa kamar yadda yazo cikin wasu surori na qur'ani lokqcin da Allah yace ya fita daga aljanna la'ananne ne shi ''kuma la'anata tana tare da kai har zuwa ranar qarshe'' sai shaidan din yace ''ya ubangiji ka jinkirta min izuwa ranar qiyama''sai Allah yace an jirka maka,har uzuwa rana da lokaci sananne,sai shqidan yqce da ubangiji ''na rantse da isarka da buwayarka sai na batar da su gaba daya,saidai bayinka daga cikinsu tsarkakakku''sai Allah yace da shi ''haqiqa bayina baka da wani iko a kansu sai wadanda suka bika dagq cikin batattu,kuma haqiqa jahannama ce makomarsu gaba dayansu,tana da qofofi guda bakwai''a wani gurin kuma shaidan din yace ''zanzo musu ta tsakaninsu data damansu data hagunsu mafi yawansu zaka samesu marasa godiya'' haka ya sake fada a wani gurin cewa ''sai na batar da su,sai na sanya musu buri sai na umarcesu su canza halittar Allah(kamar bleeching yana daya daga ciki) shi yasa Allah da kansa yake fada mana ''haqiqa shaidan abokin gabarku ne ku ruqe shi abokin gaba'',muna mantawa ne da ranar mutuwa ranar tonon asiri ranar hisabi,ranar da duk wata rai saita bi ta saman siradi ta wuce wanda qarqashinsa wutar jahannama ce,aikinka mai kyau gaskiyarka zumunci da ruqon amana ne kawai zai qetarar da kai cikin salama Son zuciya ya mana yawa,muna biyewa soye soyen zuciyoyinmu baka iya hana zuciyarka aikata mummuna wanda hakan ke kaimu ga halaka,Annabi muhammad S A W yana cewa''an lullube aljanna da abinda rai baya so(kamar salla azumi zakka,zumunci,da sauran ayyukan alkahairi da bamu son yi ko muke jin wuya gun aikata shi)an kuma lullube wuta da sha'awe sha'awe(kamar zina,caca,cin dukiyar marayu,annamimanci,sata da sauran abubuwa da rai kejin dadi yayin aikashi)'' Allah

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138