Chapter 50
Chapter 50
din saqon karta kwana kan bazata iya amsa waya ba a yanzun cikin yi masa sallama da bankwana,saida kamfanin layin sadarwa suka tabbatar mata da yake sanna ta sauke idanunta daga kan wayar,ta sauke siririyar ajiyar zuciya daidai kokacin da taji shi kuma anasan bangaren yaja tsaki qasa qasa ya furta ''fool'' dayar wayarshi data fara ringin taga ya janyo ya zura earpiece ''hello baby......muna jirgi yanzu zamu tashi.....ok...ok bye take care,i will missed you too''ya kashe wayar gaba daya ya ajjiyeta guri daya ''janye cat eyes dinkin nan daga kaina,yanzun zansa a canza miki gurin zama indai kika ci gaba kallona,bansin kallo kin gane?'' ji tayi kanar ta hukunta idon nata da har yayi kuskuren kallonshi ''me zan kalla wanda babu shi jikin abdul dina?''ta fada cikin dakiya kamar ma bada shi take ba,kanta na kallon wani sashin ''there ar many,ko skin dina kawai batayi kama data baqin mijinki ba mai zubin ta 'yan garuwa,after all ma kinsan da hakan kike qarewa mijin wata kallo,kinsan kina so tun farko bakiyi magana a taimakeki ko a qwarqwara kixo,yanzun kam its too late qwalelanki'' maganan ta mata baqi da yawa,tayi qoqarin control din bacin ranta don ta samu maida masa amsa yadda ya kamata ''shi dan garuwan ai Allah ne ya halicceshi......'' ''eh mana,da ke kika halicceshi''ya katsi numfashinta ba tare data idar ba da sauri ta dora don kada yaci da rabonta ba tare data samu ta rama ba ''ba kyau ko kudi nakeso ba mutunci nake bida da daraja,kai din kuma ai inama kallon mace ne 'yar uwata kaga babu yadda za'ayi ince inason jinsina,abdul dina yafimin kowanne namiji cikin jinsin maza,ko a mai min shara bazan iya daukarka ba da dai mai wankin toile......'' ''qarya kike wlh ya fada cikin fushi da dan daga sautinshi,ita kanta ta dan tsorata don qasa qasa suke maganar lokaci daya ya daga muryarshi,idanunshi data kalla kawai suka sake sata a zulumi,sai a lokacin ta tuna waye fa,abdallah ne,ta runtse ido tana jin zafin matsar da ya yiwa yatsunta kamar zai karya su ya kuma qi saki ''meye ne abdallah''mami ta fada tana dan leqo da kanta ''babu komai''yace ''ko baka jin dadi ne?'' mami ta tambayeshi cikin yar damuwa jin sautin muryarshi ya canza lokaci guda ''am fyn''ya fada a taqaice ''ok,to ku kashe wayoyinku''tace mishi bayan ta koma ta zauna daidai ksn sit dinta sai da ya fara hucewa da kanshi sannan ya sakar mata hannu,zuwa lokacin tuni ta fara share qwalla don azaba,jin hannun take kamar ba'a jikinta ba sanadiyyar taruwar jinin da taji ya mata,tuni har jirgin ya daidata a sama,da qyar ta janye hannun tana yarfar da shi tare da fatan jin ya sake daga daurewa da zugin da yaje mata,ko da aka tamvayesu abinda zasu ci cikin jirgin kasa ma mafa na tayi,tanaji yasa aka kawo baqin coffe aka ajjiye musu,itakam ko kallo ma bai isheta ba a hankali suke sauka daga jirgin daya bayan daya,gaba daya qafafunta sun mata tsami ga hannunta na damunta,itace a gaba abdallah a bayanta mami a bayanshi,rashin qwarin jiki ya sanya qafarta hardewa ta tafi luu zara gangara daga matattakalar a tsorace mami tace ''subhanallahi,abdallah tarota'' tuni ya tallafota ta dawo jikinsa ''kin zame mana kaya wallahi,dama so kike a rungumeki din an miki hankalinki ya kwanta,amma net tine kika qara sai nayi maganinki''ya fadi yana tureta daga jikinsa ''sannu'' mami ke ta mata har suka sauka,duk da yanayin rashin dadin jikinta baihanata ganin qawatuwar garin ba gida ne mai hawa ashirin cikin unguwar,gini ne qawatacce mai kyawu matuqa da gaske,cikin hawa na takwas nasu gidan yake,gida ne mallakinsu abdallan da suka siya da kudinsu,da fari falone madaidaici sai corridor daga damanka wanda idan ka shiga zaka tadda kitchen wani corridor dinne yake kallan kitchen din shi kuma dakunan bacci ne guda uku kowanne dactoilet cikinsa,sai valcony 'yar qarana mai kyau daga fuskar kowanne hawa na gidan wanda ta nan kana iya gano ainihin cikin unguwar da layinku da kuke an qawatashi da kyawawan kujeru guda hudu da yan shuke shuke daki daidai kowa ya dauka,tunda ta shiga dakin tayi wanka tayi akwala tayi sallah ta nade a gado sai bacci,tun la'asar dinsu sai da aka kusa idar da sallar magariba sannan mami ta tadata tayi sallah,tuni sunyi order din abinci an kawo musu har gida don haka shi kowa yaci,ba damar girki an dai siyo dan abinda zasu buqata kafin su gama kwanakinsu kamar ruwan roba qwai suger da sauran abinda zasu iya buqata,tana shirin basu guri don taji sun fara lissafe lissafen siyayyarsu mami ta tsaidata. ''maryam gaya min dame dame kike so,don gobe insha Allahu zamu fita bana son mu wuce kwana hudu,muje muyi kwana goma ko sha biyu a makka mu wuce gida lokaci na qurewa'' a kunyace tace ''bani da zabi mami,duk abinda kika zabarmin yayi'' bata ce mata komai ba ta miqa mata takarda da biro tace taje tayi mata list din duka abinda takeso nan da goma ko sha daya tazo ta kawo mata,hannu biyu tasa ta amsa ta koma daki sai ta rasa ma me zata rubuta,bata da layin qasar balle ta kiraliya ko hindatu suyi shawara,wani tunani tayi ta koma falon,nan ta samesu yadda ta barsu,saidai wannna karo sunyi kace kace cikin takardu,rubutu kawai kowannansu ya duqufa yana yi ''hmmm,gaskiya ne,ai dole ayi bikin da babu kamarsa,da daya tilo''maryam tace cikin zuciyarta ''ya akayi maryama,har kin gama?''mami ta tambayeta bayan ta dago kanta ta maida kan rubutun da takeyi ''ummm...mami cewa nayi don Allah ko zaki aramin wayarki in dan kira gida?'' ''ayya nima kuwa bani da layin qasar nan duk sanda muka zo sabo nake siya wancan faduwa yake,sai gobe idan Allah ya kaimu zan siyi wani'' har ta juya zata koma dakin mamin ta sake kiranta ''maryama zo....abdallah naga kai har ka hada naka layin ara mata tayi wayan'' yayi wani kicin kicin da rai ya saci idon mamin ya harareta kana ya ciro wayar daga aljihun trouser dinashi ya miqo mata ta miqo hannu zata karba ''idan kinsan wannna baqin basamuden zaki kira da wayata ma gwara kiyi tafiyarki ki barmun abata,don wlh kika sake kika cinyemin credit sai na zara asalary dinki,don shi na fuskanci baya da arziqin da zai iya biya na''ya fada qasa qasa yana kallon paper din hannunshi da yayi rubutu,sai ka rantse ba da ita yake ba,murguda mishi baki tayi bayan itama ta harareshi kana ta karba duk da cewa bai ganinta,shi baisan yadda ta tsaneshi bane,idan banda lalra babu abinda zai hadata da wayarshi ma. Ta loda numbers din raliyan ta kirata,sosai taji dadin shawarar data samu na abinda ya dace ta siya dim,ta kira hindatu ta zabi abinda itama takeso sai ta rage nata ta hada da na hindatun,kasa jurewa tayi don haka ta saka numbers din abdulrahim ta kirashi,sun taba hira sanna ta kashe,tana shirin ajjiyewa wani kiran ya shigo *my suger* ta gani a rubuce,ta zubawa numbers din ido tana kallo,sai ta tabe baki sanna tayi rejecting. ci gaba akayi da kira ita kam bazqta taahi ba sai ta gama rubuta duka abinda zata rubuta din ta fita gaba daya,kiran yaci gaba da shigowa ba qaqqautawa,tsaki ta ja ta janyo wayar ta daga kana ta kara akunnenta ''kada a cika
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138