Chapter 110
Chapter 110
data amshi wayar bayan ta maidata handsfree,sam maryam bata san ma ta iso ba sai da ta qaraso gabanta kanshi ya dafe ''shikenan mami nikam abdallah bawan Allah,naga ta kaina an hade min kai'' ''har hanci da goshi ma zamu hade maka indai zaka dinga matsantawa irin haka'' ''mami ina da kishi sosai kin sani,dole idan zata je mami driver ne fa zai kaita,mami banason wallahi yani ya kalleta'' ''oh abdallah,halin naka dai yana nan,to zuwa kam sai tajeshi haka kawai,wake raba da da uwa,yaushe rabon da tq gansu,haba abdallah'' ''shikenan mami na yarda mata taje,amma ba kwana ba,yauwa......baaba sule ne zai kaita,kuma don Allah ta saka hijabi don Allah''ya fada a sanyaye,wani mugun kishinta yake ji yana yi kamar yasan gyaran jiki ake mata dan ubansu kama bakinta mamin itama tayi kana tace ''iyeee,sannu fa ubana''marairaicewa yayi ''mami pleaseeeeee.......'' ''ya isa''tayi saurin tsaida shi ''taji zata saka,ince ko shikenan?'' ''i love u my mommy''ya fada cikin murmushi ''me too my son''ta fada itama,tana shirin katse wayar yace ''yauwa mami.....i need your prayer mami zami fita aiki kan mutumin nan kimin addu'a mami kamar kika saba,i know ita ke kaini ga yin kowacce iriyar nasara''maryam dake gefe duk dai taji ba dadi wani kewa da karayar zuciya na son kamata addu'a tayi masa sosai y hannayensa a sama kamar suna tare ta gama suka shafa su duka,sai yaji wata nutsuwa da dukka qarfinsa sun dawo. Miqawa maryam wayar tayi dom suyi sallama ''baby....ki kulamin da kaina'' ''kanka kuma?'' ''eh i mean you,nine ke kamar yadda kece ni,byee love u much more''ya fada ya katse wayar sai ya barta da waya a kunne,a sanyaye ta cire wayar bayan ta sauke ajiyar zuciya 🍂🍃🍂🍃🍂🍃 Cikin atamfa excellent ta shirya pure cotton,duk da mai qaramin kudi ce amma ta matuqar amsarta,kalar blue black dark blue and navy blue da sea green ce,sai ta samu kanta tana aiwatar da umarnknsa duk da ba'a tuna mata ba,hijabi ta sanya blur black wanda ya rufe ilahirin jikinta,mai hannu ne hakanan yayi matching sosai da atamfar ta,ita kanta data kalli madubi sai taga tayi masifar yin kyau,hakanan tana jinta compertable sabanin mayafi,duk da cewa dama ita gwanar hijabince musamman sanda tana gida baaba sule dinne kuwa tana fitowa suka gaisa da kanshi ya bude mata motad duk da bata so kunya ce take rufeta,don aqalla ya kusa sa'an abbanta Ta dinga kallon unguwar tasu,babu shakka gida akwai dadi,baka gane hakan sai randa aure ya daukeki daga cikinsa ya kaiki wani gu,komai rashin sukuni na gidanku randa ka barshi sai kaji kana kewa da begensa,ta samu gidan auren da ya ninka gidansu nesa ba kusa ba amma bata daina kewar gidansun ba,may b home is nothing but two arms holding you tight when you are at your worst Cike da zumudi ta saka kai cikin gidan da saurinta saboda yadda jama'ar unguwa keta binta da kallo,suna ganin ta sake zama ta daban,wata ma yaranta ke kai mata gulmar maryam tazo sai a hau leqe saboda ta tsaya suna magana da baaba sule ashe mami ta cika boot da kaya bata sani ba sai yanzu yace ta turo yara su kwashe Farinciki ya cika,zuciyarta ganin gidan qal a share sabanin da da iyakacin tsaftar qofar dakinsu ne zuwa,cikin dakin nasu,lubabatu ce kan tabarma zaune da qananun qannensu wadanda suke daki daya da da qatuwar farar takarda ta shimfideta kan tabarma ta zana alifun ba'un har zuwa ya'un manya manya da alamu tana koya musu ne shi yasa ko sallamarta basu ji ba,kafin ta sake maimaita sallamar ta hango isyaku ya fito daga dakin uwarsa kanshi tsaye yabi takan takardar ya take rubutun kana yayo hanyar waje,lubabatun ce ta yunquro da sauri ta cafko wuyanshi ta baya ''wannan iskancin naka isyaku ya isheni wallahi yau sai jikinka ya gaya maka'' Da sauri maryam ta qarasa don kada abun ya kwabe tana banbare hanunta daga wuyan isyaku wanda keta kici kicin qwace kansa cike da rashin kunya ''sakeshi lubabatu kinji sakeshi''sai a lokacin taga maryam din ba musu ta sakeshin ya kuwa fice abinsa da gudu,ta saki fuskarta daga daurewar da tayi tana fadin ''sannu da zuwa adda maryam'' ''yauwa lubabatu,karatu ake yi ne?''ta dubi yaran kana tace ''eh,makarantar dare suke zuwa malaminsu yace su tabbata sun iya zuwa anjima zasu je kuma naga basu iya ba''farinciki ya kama maryam ganin an fara samun ci gaba a harkar karatun yaran ''da kyau kin kyauta kuwa lubabatu'' yaran suka zuba mata ido suna shakkad zuwa gurinta,ko dama can ita ba mafadaciya bace bata dai shiga shirginsu ne saboda gudun rashin kunya irin tasu,su kuma suna ganin a yanzu ta zama yar gayu kada ta makesu idan suka matso gurinta tunda haka jamila ke musu sanda tana aure gidan jabir sai ta bude hannayenta tana fadin ''kamar baku ga yayarku bane,ku taso mu gaisa mana asiya'' ai kuwa har rige rigen zuwa suka dinga yi,sai taji farinciki ya rufeta,zaman lafiya babu abinda ua kasihi dadi haka dan uwa,baka da kamarshi cikin duniya,hamsin hamsin ta fidda ta raba musu su biyar tace su sayi alawa Ganin har suka gama budurinsu,aka gama shigowa da kayan da mama ta hadota da su samfurin kayan masarufi babu wanda ya leqo daga matan gidan ya sanyata tambayar lubanatu wadda gaba daya maryam ta karanci nutsuwa sosai a tattare da ita ''ina wai matan gidan ne?'' ''au...''ta fada tana murmushi tare da dafe bakinta ''na manta ban gaya miki ba,sun fara zuwa makarantar matan aure qarfe tara na safe zuwa daya na rana mamata da maman hindatu(maman maryam din)ke zuwa,ya hindatu ce ta sanyasu'' cike da nuna kara tace ''inna hadiza fa?'' sai da ta kalki qofar dakin nata kana ta tabe baki ''tana ciki tana bacci,tata makarantar kenan''ta fada tana bushewa da dariya,daquwa maryam ta mata ''mamarki ce itama''daki lubabatu ta shiga ta daukowa maryam maqullin dakin maman tace ''adda ga key din ko''ta karba kana ta budr dakin maman ta shiga ta bi dakin da kallo ya sake kyau ya canza,cike yake da tsafta da qamshi,wani kewar dakin ta kamata,sai ta cilla mayafinta da jakarta saman kujera,kai tsaye ra shige dakin maman ta fada gadonta data yi kewarsa matuqa Tana son gadon umman nata tana jin dadin kwanciya a kai,gadon da tasha dabdalar quruciyarta a kai har yanzu katifarshi ce a kai,duk da canza kayan daki da taga umman nata tayi amma bata canza abarta ba,ta sake juyawa tana tuna rayuwarta cikin gidan quruciyarta zaqi da madaci kala kala,a haka bacci yazo ya sureta. Can cikin barcinta taji kamar ana kiran sunanta,a hankali ta dinga bude idonta har ta budesu tarwai kan fuskar mamanta,farinciki ya kamata,yaushe rabon data ganta,tana tsaye cikin unifaorm ash colour doguwar riga da hijabi,sun mata kyau kuwa unifaorm din sosai ''ki tashi kiyi sallah kina ta bacci har anyi azahar''sai ta miqe tana mutstsuka ido ''ashe har kun dawo mama'' ''eh kina ta bacci har girki akayi aka gama baki sani ba,halan bacci kika koyo''murmushi tayi ta miqe zata fice a dakin tace ''sannunku da dawowa'' ''yauwa''maman ta amsa tana rataye jakar makarantar ta data daukota daga falo gami da cire hijabinta ta linke ta saka a sif Duk inda tayi maman kallonta take,godiya take wa Allah cikin zuciyarta,farinciki fal ranta,lallai addu'a bata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138