Skip to content

Chapter 134

Chapter 134

Abadan Book One Complete Hausa Novel 1,289 words 0 views Progress saved
Download Book

kaini har gida,bqn boyewa mama komai ba din tana daga cikin wadanda sukaui silar fadawatq wanan mummunar rayuwar,abun mamaki qarara mama ta nuna qyamata atake agun,harda saiya mazauni sabanin wanda take a dazun da nazo gidan Tun daga ranar na fara ganin tsantsar tsana da qyama daga gurin mama na hatta da qannena ba'a barsu a baya ba,duka babana baisan me ake ciki ba shidai ya san cewa an sakeni kuma ya nemi engineer amma yaqi sam ya sanar masa dalilin da yasa ya sakenin,yanzu nan da kika ganni na taho ne domi amsar magani da yin jinya,saboda kaucewa idon jama'a da maganganunsu yasa na baro yaho garin da babu wanda ya sanni,don nan din ya fiyemin rufin asiri''kuka sosai zahariyya takeyi nadama kam babu kalar wadda batayi ba game da bitewa son zuciya da tayi,yanzu gashi ta kaisu ta barosu,ganin haka ua sanya mami tayi aumarni a dauketa a shiga da ita don yi mata aikin,haka aka dauketa aka turata zuwa dakin jira na kimanin awa guda sukayi wata nurse ta fito da yaron cikin zanin mamartashi saidai tuni rai yayi halinsa ya mutu sajamakon tun fari uwar bata samu kulawa mai kyau ba lokacin cikinsa da kuma wuyar da yasha lokacin haihuwa,ba qaramin haushi mami taji ba don bata iya shiru ba sai da tayi fada sosai,minti goma tsakani aka turo zahariyya iyama zuwa dakin hutu,da tambayar abinda ta haifa ra farka a bakinta mami ke gaya mata ya rasu,ajiyar zuciya ta saki ''gwara da Allah yasa ya mutu,haqiqa ya samu gata mai kyau da ya mutu din''mami ce ta tsawatar mata ''kada ki kuma fadin hak,kul''mirmushin yaqe tayi tace ''mami don bakisan dan waye ba,ta yaya aka sameshi ba,amma tunda kince haka bazan kuma fada ba,amma mami don Allah ku yafemin,ba shakka mun cika azzalumai,ba muyi muku sakayyar data dace ba,haqiqa samun mutum irinki mami sai an tona,mai saka sharri da alkhairi,mai saka mummuna da mai kyau,ke mutum ce mami,a yanzu nake kwadayin inama ace tun fari kece kika haifeni,na tabbatar da tuni yanzu ina rayuwa ingantacciya ba irin wadda nake kai ba yanzu'' ''ya isa duka mun yafe miki,ko Allah muna masa laifi ya yafe mana ballanta na mu 'yan adam'' ''na gode mami,ko yanzu na mutu nasan ''da ikon Allah zan samu wani sassaucin'' ''ba na ce miki ki daina maganar mutuwa bane zahariyya'' ''na daina mami''ta fada kana taja idanunta ta rufe ruf tana saukar da ajiyar zuciya Maryam tasa abdallah ya dauka shi da security dinsa taje su tafi gida itakam qnan zata kwana kafin gobe ta sanar da dangin zahariyya din a samu wanda zai dinga kwana da ita,ba maryam ba har abdallah da yasan mamin farin sani mamaki take bashi,wata iriyar kubutacciyar zuciya Allah ya hadata da iya,basu ce komai ba suka juya suka tafi ************ kiran sallar asuba ya sa mami miqewa ta ajjiye wayarta dake hannunta wadda ta bude application na qur'ani tana karantawa cikin zuciyarta,kwana batayi bacci ba kusan sabonta ne saboda kowa yasan ma'aikatan lafiya da iya kwanan zaune fara daura alwalarta kenan ta fara jiyo salatin zahariyya tana yi tana shaquwa,jade da ambaton sunan Allah,da sauri ta saki alwalar ta koma cikin dakin da gudu,shaquwa take sosai idanunta a qaqqafe suna kallon sama,da sauri,mamin ta fara bata duk wani taimako da ya kamata a matsayinta na likita,saidai duk yadda takai ga son ceton rayuwar zahariyyan wanda ya halicceta ya riga da ya wanzar mata da qaddararta,ta amsa kiran ubangijinta ta riga mu gidan gaskiya,duk dauriya irin ta mamin saida ta saki kuka,babi shakka mutuwa ishara ce izina ce hakanan abar tsori da fargaba ce ga duk wani abu ma rai,ba bil'adama kadai na hatta da sauran halittu dake numfashi a doron qasa ************* Gidan kawunta qanin mahaifinta can suka sada gawar din su suka fi haqqi da ita,cikin qanqanin lokaci aka mata sutura aka kaita gidanta na gaskiya,shikenan duniyar,zancan banza ce,idan kayi damara don ita ka kwance,don katsaham zata zo maka tace sai ka bar cikinta bata da buqatarka don wa'adinka ya cika na zama acikinta,kusan azahar mamin taga giftawar wata mace goye da yaro,tayi tsammanin daya dagq cikin dangin mahaifinau zahariyyan ne mutanen qauyensu yan gaisuwa,sai data sake ganin wulgawar matar ta saka ido sosai sai taga kamar zubaida,matar dake gefanta ta taba tana tambayarta ''waccan kamar zubaida ko?''da sauri matar ta amsa mata din cike da murna take,yau gata tana zaune daura da haj bintu ''eh,zubaidan hajiya nene ba, ita ce mana kema kin kasa shaidata ko ke da kuka zauna tare ma tun tana qaramarta,hmmm duniya ce ai budurwar wawa,wadda ta ishi kowa riga da wando,uwarsu ta gama bata su ta lalata su yanzu yau gashi yadda suka koma,dan ahege ne fa goye a bayanta,yanzu haka aikatau take wani guri tana ciyar da kanta,don babu wanda zai dauki jigilarta bayan lokacin da suke da ahi bani wanda suka morawa komai''ko kadan bayanan matar bai burge mami ba,jasalima haushi ta bata,cikin takaici tace da ita ''harshe yana iya kai mutum wuta nan da nan cikin qanqanin lokaci,anna bi yace idan kaga dan uwanka cikin wata musiba ka shiga aibata shi da yadashi,Allah yana iya yaye masa kai kuma ya jarrabceka da abinda ka aibata shi akai din,abinda aka umarcemu da cewa duk lokacin da muka ga wani da,Allah ya jarabta da wani abu ko cuta ce ko makamancinta shibe *ALHAMDULILLAHIL LAZI AAFAANI MIMMAB TALAKA BIHI,WAFADDALANI ALA KASIRIN MIMMAN KHALAQA TAFDILA*,daga haka mamin ta miqe ta bata guri Bayan zubaidan tabi wadda ta gani riqe da robar abinci ta zagaya can baya ta kunce qarmashshan danta daga goyo ta zaunar da shi kan cinyarta ya soma bashi abincin cikin robar,don tausayi sai da qwalla ta zubo mata,ta qarasa kusa da ita tana kiran sunanta,sai kuwa tq zabura ta miqe zata gudu ''kada kije ko,ina zubaida''sai ta kira sunan mamin hawaye,na bin kuncinta,inda take ta qarasa tasa hannu ta amshi dan ta jata gefe guda Tiryan tiryan ta debe abinda ya faru da ita bayan barinta gida,ashe gun mugu ta gudu wanda shine uban danta,ba dadeea ta ganshi ya sato,nene yazo ya hadasu,ashe abinda yasa ya nuna yana sonta,cikin jikinta yakeso ta haife ya dauke yaron ya saidawa qungiyar asiri,tun daga rqnar data fuskanci haka suka shiga tashin hankali ita da nene wadda ta dawo tamkar tababbiya,duk da haka wani lokacin idan abun ya lafa mata sai ka gantq ras kamar mai hankali,ruqon Allah suka dinga yi cikin ikomsa Allah ya kawo abokan gabarsu suka murqushesu shine su kuma sukayi amfani da wannan damar suka tsere,yanzu haka nene na gidan mahaukata ita kuma tana aikin wanke wanke fidan wani saida abinci da shi take dan taimakon kanta da nenen kuka sosai mamin tayi kana ta amshi adress din gidan aikin nata tace zata nemeta,itakam ko wani abu ne ai zubaida bata masu komai ba face kanta data zalunta ta biyewa son zuciyarta πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚ Zaune suke gabanta tana saman kujeravtana rubuce rubucenta,ta sake dagiwa karo na biyu ya dubesu ''uhmmm,idan kun shirya yimin bayanin ina jinku''abdallah ne da maryam kusan awa guda an rasa mai bayani tsakaninsu,sai kallon kallon,gaba daya ta fahimci sun maidata kakarsu,akwai surukuta tsakaninta da maryam don haka ta dubi abdallah ''gayamin meke faruwa?''mutsu mutsu ua shiga yi kana cikin inda inda yace ''mami,kince

Table of Contents

Chapters

138 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138