Chapter 8
Chapter 8
Raj, fitar yayi ya kalli Raj da Ayrah ke kalla tana fad'in "Ka taho mu tafi" ya kalle ta yayi murmurshi sannan ya maeda duban sa kan Yah Sadeeq daya fito daga motar "Ka shiga Abban na ciki" "Tohm" ya amsa da hakan yana k'arasawa ya shiga gaban dake a bud'e ya zauna "Barka da wannan lokaci" ya fad'a kansa a k'asa, cigaba da kallan kyakykyawan yaron Abba yayi wanda yake sa'an d'an sa Sadeeq, tun kafin ya kaega cewa yaron komae yaji wata nutsuwa tattare dashi amma duk seya watsar yace "Barka dae..yaya sunan ka?" Abba ya fad'a yana gyara zaman sa a inda yake zaune, har lokacin be d'ago ba ya furta "Suraj.." "Kaee Raj dae.." Ayrah dake baya ta fad'a tana waro idanun ta, dukkan su murmurshi suka yi kafin Abba ya sake cewa "Mahaefin ka fa?" "Kabeeru" jinjina kae Abba yayi sannan yace "Baka zuwa makaranta ne?" se a lokacin ya d'ago kae ya kalli Abban sannan ya maeda kan nasa k'asa yace "Ehh" d'an shiru Abba yayi yana tunanin tambayar da zata fito daga bakin sa haka dae ya cije yace "Suraj meyasa baka zuwa makaranta?" "Abba Raj ne fa" Ayrah ta sake fad'a, girgiza kae Abba yayi da d'an murmurshi akan fuskar sa kafin yace "Toh shikenan Raj" Yah Sadeeq dake gefen ta shima murmurshin yayi yana girgiza kae "Abbu bashi da kud'in saka ni.." "Shikenan kawae, idan nace zan saka ka zaka ji dad'i?" da sauri ya d'ago kae ya sake kallan Abban, ya lumshe idanun sa yana jin dad'i har besan sanda ya jinjina kae ba murmurshi na wanzuwa a kyakykyawar fuskar sa ba, Abba ma yayi murmurshi yace "Ka fad'a wa Abban naka idan yana da lokaci ya same ni a gida akwae maganar da zamu yi.." amsawa yayi da "Toh angode, Allah ya saka da alkhaeri" "Ameen" Abba ya fad'a yana sake yabawa da hankalin yaron, be bar cikin motar ba seda Abban ya bashi number sa yace ya kaewa Abban nasa ya kira shi.. (_A gurguje zanyi wajen nan pls, saboda idan nace zan ja nan d'in da nisa gaskiya zamu dad'e ne bamu matsa gaba ba, so shys nayi deciding kawae nayi briefing wajen amma yadda zaku fahimta_) ... Sanda Raj ya jewa da Iyayen sa maganar Abban sosae suka yi mamaki, dan da farko ma daya fad'awa Ummeen sa cewar mutumin yace ze sanya shi a makaranta bata yarda ba k'aryatawa tayi kuma ta rufe shi da fad'a dan lokacin ma tun safe babu abinda suka ci kuma har zuwa lokacin Abbun nasa be dawo ba, dama shine me fafutuka ya fita yayi er buga buga ya samo musu abinda zasu ci amma takamaemae bashi da tsayayyiyar sana'a, shiyasa idan ya fita ma ya samo wani abun gaba d'aya suna amfani dashi ne wajen samun abinda zasu ci "Toh hayaniyar me nake ji kuma da rana tsakar nan" maganar da taji daga tsakar gidan ne ya sanya ta dakatawa daga fad'an da take wa Raj, Malam Kabeeru ya k'araso hannun sa d'auke da wata leda, seta k'arasa ta kar6a tana fad'in "Sannu da zuwa Abbu" "Yawwah sannun ka dae" ya fad'a yana kallan Raj dake fad'in "Abbu sannu da zuwa" amsa sannu da zuwan yayi kafin yaja kujera er tsuguno ya zauna a tsakar gidan yana sauke numfashi "Meya faru ne kike ta fad'a tun daga soro nake jiyo muryar ki?" "Gashi nan yaron nan yazo min da wani zance wae wani mutumi yace ze sanya shi makaranta wae kuma ya bashi number sa ka ganta ma yace wae kaema kaje yana neman ka" ta fad'a tana mik'a masa wata takadda dake d'auke da number Abban, kallan su su duka Abbu yayi cikin mamaki, se kuma ya tsaeda idanun sa akan Raj yace "A'ina ya san ka?" d'an shiru kad'an yayi sannan yace bayan ya d'auke kae "A makarantar da nake zuwa" jinjina kae Abbu yayi yana mamakin yadda d'an nasa kullum burin sa shine yayi karatu amma shi kam ya rasa yadda zeyi ya cika masa wannan burin nasa, shi kansa sa yana sa kud'i zeyi k'ok'ari wajen cikawa d'an nasa buri ne ta hanyar kae shi wata k'asar ma ba Nigeria ba yayi karatu "Kuma ka tabbatar da gaske kake?" Abbu yayi k'arfin halin fad'in hakan duk da shi shaida ne akan d'an nasa duk da k'arancin shekaru irin nasa amma da wuya yayi k'arya a cikin lamarin sa "Ehh Abba Allah kuwa da gaske nake" "Ikon Allah" Abbu ya fad'a yana jinjina kae, Ummee tace "Toh zaka je d'in?" kallan ta Abbu yayi kana yace "Me ze hana, kika sani ko alkhaeri ke kiran mu?" "Toh Allah yasa, bari na tashi na d'ora mana shinkafar can mu samu mu ci" Ummee ta fad'a tana mik'ewa. Washe gari da wuri Abbu ya shirya tare shi da Raj, ya kira Abba da er k'aramar wayar sa yayi masa kwatancen gidan nasa sannan suka tafi gidan, daga gidan nasu akwae d'an nisa sosae dan haka suka d'an rage tafiyar a k'asa kafin suka tari adaedaeta ta k'arasa dasu da ragowar chanjin daya ragewa Abbu, a k'ofar gidan suka tsaya Abbu yayi wa Abba flashing a wayar sa saboda kud'in wayar sa daya k'are, ganin kiran nasa ya sanya Abba kawae ya fito dan ya fahimci yazo ne, suka gaesa cikin mutuntawa sannan kowannen su ya gabatar da kansa ga d'an uwan sa, tun a lokacin Abba yaji Abbun ya kwanta masa dan kana ganin sa kaga mutumin kirki gashi ko had'a idanu da Abban ya kasa yi, magana ta k'arshe data wakana a tsakanin su shine Abba yace bayan yaji yadda rayuwar su ke kasancewa, se yayi buga buga yake samu suci abinci, wani lokacin idan be samu komae ba haka zasu wuni da yunwa, shi gashi ba karatu yayi ba dududu iya secondary school ya tsaya, sana'a kuma ta k'i shi, shiyasa ma har lokaci be saka Raj a makaranta ba, saboda komae suka samu cikin su ne, kuma gashi Raj d'in ya tashi da k'aunar makaranta a ransa shi kuma be san yadda zeyi ya saka shi ba, dan idan yace ze saka shin zasu matuk'ar takura ne "Allah sarki, kar ka damu In Sha Allah kamar an saka Suraj a makaranta ne an gama, maganar sana'a kuma dama inaso na bud'e wani shago ne a cikin satin nan, toh idan zaka iya seka dinga zuwa muna zama tare ina sallamar ka" daga inda Abbu ke zaune kan wata kujera ya zamo kamar ze tsugunna yace muryar sa na rawa "Nagode sosae Alhaji, Allah ya saka da alkhaeri, ya biya buk'ata, yasa ka gama da duniya lafiya, nagode nagode sosae Alhaji" "Ya isa haka, babu komae Allah ya taemake mu.." Abba ya fad'a yana rik'o Abban, seya mik'e ya koma ya zauna dae_dae lokacin da Abba ke fad'in "In Sha Allah zuwa gobe se kazo mu fara shirye shirye.." "Toh Alhaji babu damuwa" ya fad'a yana cigaba da kwararowa Abban addu'a cikin matuk'ar farin ciki da jin dad'i. Sanda ya koma gida ya fad'awa matar sa zancen tayi matuk'ar farin ciki, haka suka had'u suka dinga yiwa Abba addu'o'i kala kala. Shima Abban daya jewa Umma da maganar taji dad'i sosae ta kuma yi addu'ar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70