Chapter 56
Chapter 56
Sadeeq ya lumshe idanun sa sannan ya fara magana a nutse "Abba, Umma kada 6acin rae yasa ku man ta wacece Ayrah, Abba kada 6acin rae yasa ku aebata d'iyar da kuka haefa, Abba ina ji a jiki na akwae wani 6oyayyen al'amari dake faruwa wanda da zamu bawa Ayrah dama zata fad'e shi, amma Abba bamu bata ba, mun k'i bata wannan damar data nema, Abba Ayrah bata da wayo ko bud'ewar idon da zesa ta bi saurayi!" tashi zaune Abba yayi har lokacin hannun sa na d'ore akan k'irjin sa yace bayan ya girgiza kae "Shin baka ji abinda ta fad'a bane Sadeeq? Tun ina k'ok'arin k'arya ta abinda muke zargi yau Ayrah da kan ta tazo ta tabbatar mana harda k'arin wani abun ma" Abban ya k'arasa fad'a yana kallan Yah Sadeeq "Umma, Abba Ayrah ce fa, Umma Ayrah ce fa, kuna tunanin zata iya zuwa can wani waje tayi aure da wanda bakwa so? Ayrahn da kullum cikin son farin cikin ku take Umma?" shiru dukan su suka yi cikin nazarin abinda Yah Sadeeq d'in ya fad'a, kamar babu wanda ze tanka a cikin su se kuma Umma tace "Ya akayi hakan ta faru kenan Sadeeq? Me kake so ka ce mana? Dukan mu ba'a son ran mu muke zargin Ayrah ba Sadeeq, babu yadda zamu yi ne, mu iyaye ne ta yaya zamu aebata d'iyar mu? Abinda take fad'a yanzu ya zama dole mu shiga rud'ani, ta bar gida bayan maganar hana ta auren yaron nan, yanzu kuma ta dawo tace tana d'auke da auren sa, Sadeeq ya kake so muyi?" seda yaja ajiyar zuciya sannan yace "Umma, Abba don Allah mu bari naje na kira Ayrah tazo ta mana bayani, inaji a jiki na akwae wani abun.." ya fad'a har cikin ran sa yana jin abinda ya fad'a d'in, shiru na wajen minti 2 ya wanzu a wajen kowanne da abinda yake sak'awa a ran sa, se dae dukan su sun gamsu da zancen d'an nasu, a gefe guda kuma dukan su sun so su fahimci kamar sun yi laefi, k'in tsayawa suji abinda ze fito daga bakin Ayrahn, yanke mata hukunci tun kafin su san aenahin abinda ya faru, koma menene ya faru 6acin rae ne "Je ka kira min d'iya ta!" Umma ta fad'a tana kallan Yah Sadeeq lokaci guda kuma tana jin yadda wani nauyi dake k'irjin ta ya d'an ragu, seta saka hannu ta goge hawayen fuskar ta dae_dae lokacin da Yah Sadeeq ya saki murmushi kana ya mik'e yana kallan Abba yace a hankali "Abba in kira ta?" seda Abba ya runtse idanun sa sannan ya bud'e kawae ya jinjina kae, cike da farin ciki ya sanya k'afa ya fice daga cikin gidan yana d'an d'ingishi dan har lokacin k'afar ta sa bata ida warkewa ba. ... Dae_dae lokacin daya fito titi yayi dae_dae da lokacin daya hango Ayrahn cikin motar Rk, yana k'ok'arin k'arasawa wajen motar Rk ya tashi motar ya bar wajen, se yayi sauri ya tsaeda Napep ya sanar dashi yabi masa motar Rk d'in, babu musu me Napep d'in ya bi shi, dae_dae wani waje motar Rk d'in ta dakata wanda yafi kama da Hotel, Yah Sadeeq ya sauka ya biya me Napep d'in kud'in sa sannan ya cigaba da tafiya zuwa wajen motar. Saukowa Rk yayi daga driver seat ya zagaya zuwa wajen me zaman banza ya bud'e k'ofar yana kallan yanda take a cure waje d'aya, yanzu ta dena kukan se dae ita kad'ae tasan abinda take sak'awa a cikin zuciyar ta "Don Allah ki fito!" ya fad'a cikin rarrashi, idan motar da take ciki ta d'aga kae ta kalle shi toh itama ta kalle shi "Ayrah!" Yah Sadeeq ya fad'a sanda ya k'araso dab da motar, da wani irin sauri ta d'aga kan ta ba tare data shirya ba, nan take idanun ta suka sauka akan Yah Sadeeq, seda ta d'an lumshe idanun ta sannan ta bud'e dan tabbatar da Yah Sadeeq d'in ne ba gizo yake mata ba sannan ta sauko daga cikin motar a million ta k'arasa ta fad'a jikin Yah Sadeeq d'in tana sakin wani irin kuka, a hanzarce ya d'aga kan sa ya kalli wanda ta rungume d'in, ko wani be masa bayani ba ya fahimci wanene shi, amma me kuma ya kawo shi nan d'in? Shima Yah Sadeeq d'in rungume ta yayi yana jin yanda take kuka sosae, tana shirin fara magana duk dae cikin kukan yace "Ya isa! Ki bari mu zauna, ina buk'atar jin gaskiyar al'amari, bana son k'arya Ayrah.." kamar wata k'adangaruwa ta shiga jinjina kae har lokacin tak'i sakin sa, d'aga idanun sa yayi ya kalli Rk da har lokacin yake tsaye se dae basu yake kalla ba yace "Raj?" se a lokacin ya juyo ya kalle shi cike da mamakin yadda ya kama sunan sa, seya jinjina kae yana lumshe idanun sa, d'an murmushi kad'an Yah Sadeeq yayi kana ya furta "Sad..." "Sadeeq!" Rk ya k'arasa sunan yana nuna Yah Sadeeq "Ehh" shine abinda Yah Sadeeq ya furta sannan ya d'ago Ayrah dake jikin sa ya rik'e hannayen ta kana yace "Ina son magana da kae idan babu damuwa" "Why not?" Rk ga fad'a bayan ya d'aga kafad'a "Mu k'arasa can.." Rk ya fad'a yana nuna wani d'an madaedaecin waje dake d'auke da wasu kujeru masu kyau, babu wanda ya sake cewa komae cikin su Rk na gaba yayin da Yah Sadeeq ke a bayan sa suka cigaba da tafiya zuwa wajen, ita dae Ayrah babu abinda tace ta cigaba da rik'e hannun yayan ta dan tana ji kamar idan ta sake shi zata bud'e ido taga baya nan, a haka suka k'arasa wajen, Rk ne ya fara neman waje ya zauna sannan Yah Sadeeq ya zauna, ita dae Ayrah ko zaman ma kasawa tayi seda Yah Sadeeq ya kalle ta yace a hankali "Ki zauna kin ji?" kamar bata san da wata halittar a wajen ba taja kujera ta zauna har lokacin idanun ta na kan Yah Sadeeq, shiru Rk yayi kawae yana jiran jin abinda Yah Sadeeq d'in zece, kamar ya sani kuwa seya sauke ajiyar zuciya sannan ya furta "Menene gaskiyar barin Ayrah gida don Allah? Menene gaskiyar auren ka da tace tana d'auke da shi a kan ta?" shiru ya d'an yi yana nazarin tambayar Yah Sadeeq d'in, kamar ba zece komae ba se kuma ya d'an lumshe manyan idanun sa sannan ya bud'e yana tunanin tsayin adadin maganar da zeyi, amma ya zama dole yayi ko dan hakan ze wanke Ayrah daga wajen iyayen ta, sannan kuma su yafe mata koda ze samu kan ta ta dawo asalin Ayrahn sa, a hankali ya shiga labartawa Yah Sadeeq abinda ya faru, duk wani abu daya sani seda ya fad'a masa, yana kaewa k'arshe yayi shiru yana d'an aje numfashi kad'an, shiru Yah Sadeeq yayi tun lokacin da Rk d'in ya fara bashi labari, mamaki, tsoro gami da al'ajabin wannan al'amari yak'i barin sa, ya rasa ma me zece kwata kwata, ya rasa ma wane tunani ya kamata yayi, abin ya bashi tsoro da mamaki aenun, a hankali ya dubi inda Ayrah take zaune duk tayi wani iri da ita kamar ba Ayrah ta asali ba, se yaji wani
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70