Skip to content

Chapter 1

Chapter 1

Zazzafar Kauna Book One Complete Hausa Novels 1,207 words 0 views Progress saved
Download Book

https://chat.whatsapp.com/DH0EIIWNPnSICxsGgh2DSd *♡☆ZAZZAFAR KAUNA☆♡* *FREE BOOK* *CHAPTER ONE* Page_001 ___K'arfe 7pm ne na daren ranar juma'a, tana zaune kan er kujerar dake gaban mudubin ta hannun ta rik'e da waya er k'arama wadda wasu ke kira da rakani kashi, sassanyan murmushi ke tashi daga kyakykyawar doguwar farar fuskar ta, tana nan zaune har zuwa lokacin da wata mata wadda kana ganin ta kasan mahaefiyar tace, saboda tsananin kama da suke yi, ta yaye labulen d'akin ta lek'o tana kallan ta "AYRAH wae har yanzu jiran Abban kike?" Murmushi ne ya sake wanzuwa akan fuskar wadda aka kira da Ayrahn wanda hakan ya bawa dimple d'in dake gefen kowanne kumatun ta lotsawa sosae sannan tace cikin muryar ta me dad'in saurare "Ehh Umma.." ta6e baki Umma tayi tace "Ae se kiyi ta jira.." daga haka ta saki labulen ta koma tsakar gida. Tana nan zaune bayan wajen minti 10 ta jiyo sallamar mahaefin nata daga tsakar gidan su, seta ajjiye wayar da sauri akan gadon sannan ta mik'e ta yaye labulen d'akin ta fito, hasken farin wata da kuma na k'wan fitilar da suka kunna ya sanya ni ganin kyakykyawar fuskar ta da har zan iya kwatanta muku ita, matsashiya ce er kimanin shekaru 19 doguwa ce fara sosae, me idanu manya manya da dogon siririn hanci, se d'an k'aramin red lips d'in ta, sanye take cikin doguwar riga bak'a babu d'an kwali a kanta dan haka ta yafa mayafin doguwar rigar akan ta "Abba sannu da zuwa.." ta fad'a tana neman waje ta zauna "Yawwah Ayrah" Abban ya fad'a yana neman waje ya zauna sannan da murmushi kan fuskar sa ya sake kallan Ayrahn bayan ya amsa sannu da zuwan da Umma ke masa "Toh in gyara zama dae in sha labarin karatun kin nan, dan da alama akwae magana a bakin ki" murmushi ta sake yi sannan tace "Abba ae tun d'azu kae nake jira nazo muku da wani babban albishir" Umma ta kalli Abba tace "Ahh toh, tun d'azu tak'i fad'a min abinda yake ta sanya ta murmushi tace seka dawo.." Abba ya maeda duban sa kan Ayrah yace "Toh muna jin ki, Allah yasa alkhaeri ne" gyara zama tayi daga inda take zaune sannan ta fara magana har lokacin murmushi yak'i barin kyakykyawar fuskar ta "Abba na had'u da RAJ.." ta fad'a da mad'aukakin murmushi akan fuskar ta, cikin rashin fahimta dukkan su suka kalle ta, seta d'an tsaya itama tana kallan su kafin tace "Raj fa nake nufi, Umma Raj d'ina fa, kun tuna?" ta fad'a tana d'an murmushi dan ita in dae akan Raj ne bata da wata kunya, kallan juna Umma da Abba suka yi kafin Abba ya runtse idanun sa sannan ya fara k'ok'arin magana "Umma cewa yayi ma na fad'a tun wuri Abbun sa zasu zo wajen Abba" Ayrah ta fad'a kafin Abban ya fara magana, Umma dake lura da yanayin Abba ta furta a hankali tana kallan sa sosae "Abban su lafiya dae koh?" jinjina kae yayi kafin cikin er dakiya ya furta "Kina nufin Raj d'an gidan Kabeeru..?" seta jinjina kae cikin jin dad'in yadda Abban ya gane maganar ta ta tace "Ehh Abba, bama mu ta6a tunanin.." d'aga mata hannun da Abba yayi ne ya sanya ta dakatawa daga fad'in maganar da take k'ok'arin fad'a, ta cigaba da kallan yadda lokaci guda k'wayar idanun sa ta sauya, haka zalika Umma ma tak'i kallan ta, seda Abban ya sake runtse idanun sa sannan ya bud'e ya fara fad'in "Kar ki sake min maganar sa ko maganar wanda ya shafi ahalin su gaba d'aya.." Abba ya k'arasa maganar idanun sa na sake yin jawur, cikin rashin fahimta take kallan Abban nasu, ta kuma kalli Umma sannan tace a d'an rud'e "Abba ko dae ka bayar dani ne ga wani bansani ba? Abba cewa nayi fa Raj ke so azo a nemar masa aure na.." "Ayrah..ki tashi ki bar wajen nan idan baso kike zuciya ta ta buga ba" Fararen idanun ta dake d'auke da bak'a sid'ik d'in k'wayar idanu ta d'aga ta sake duban mahaefin nata, take wasu k'walla suka tarar mata tana jin yadda k'irjin ta ke bugawa da k'arfin gaske, "me yake faruwa ne?" ta tambayi kanta "Abba Raj ne fa, Abba Raj dae wanda ka sani fa, akan sa nake magana.." Abba ya runtse idanun sa yana jin wani irin zafi a cikin ransa cikin 6acin rae ya furta "Ki saka a ranki in dae ina raye, har abada ba zaki ta6a auren Suraj ba" da wani irin razana ta d'aga ido ta kalli mahaefin nata, tana jin yadda kalaman nasa ke sauka a cikin kunnuwan ta kamar saukar mashi, kafin takae ga cewa komae ta sake jiyo Abban nata yana fad'in "Ki kawo koma waye a fad'in garin nan gaba d'aya amma dae_dae da minti d'aya kada ki sake ki yaudari kanki kiyi tunanin zan aura miki Raj, bama Raj ba duk wani daya dangance su bazan ta6a aura miki shi ba" kuka ne ya k'wace mata babu k'ak'k'autawa tana jin wani iri a rae da zuciya har ma da gangar jikin ta, a hankali taja k'afafun ta da rarrafe ta k'arasa gaban mahaefin nata ta rik'o k'afafun sa sannan ta fara magana cikin kuka, kyakykyawar fuskar nan ta ta tayi jajir "Abba..ka tausaya min, Abba ka taemakawa zuciya ta, Abba ko da wannan ce zata zama alfarma ta k'arshe da zaka iya yi min a rayuwa Abba kayi min ita don Allah" ta k'arasa fad'a tana sake fashewa da wani sabon kuka, a hankali Abba ya zame k'afafun sa bugun zuciyar sa na k'aruwa ko ba'a gwada shi ba tabbas yasan ciwon sa na dab da tashi, ya d'an runtse idanun sa kad'an sannan ya fara k'ok'arin tafiya, ta sake rik'o k'afafun nasa tana kuka kamar wadda ranta ze fita "Abba ina k'aunar Raj, zuciya ta zata iya bugawa idan kace zaka rabani da shi, Abba kace wani abu don Allah" juyowa Abba yayi yana kallan ta kana a fusace yace "Ko mutuwa zaki yi ba zaki ta6a auren Raj ba.." daga haka ya wuce d'akin sa, mik'ewar da Umma tayi ne ya sanya ta d'ago fuskar ta da tayi jajir tace "Umma ya zaki tafi ki barni cikin duhu, Umma me Raj ya muku da Abba zece bazan aure shi ba, Umma Raj fa ko har yanzu baku gane wanda nake magana akansa ba.. Umma kiyi wa Abba bayani don Allah" ta k'arasa maganar sanda wani kukan yaci k'arfin ta, ko kallan inda take Umma ba tayi ba ta wuce cikin d'akin da Abba ya shiga.. A hankali ta cigaba da rera kukan ta, seda tayi me isarta sannan taja k'afafun ta zuwa cikin d'akin ta har lokacin hawaye yak'i dena sintiri akan kuncin ta, wayar ta dake ajje ta d'akko ta danno wata number ta kira... ... A hankali ya sako k'afafun sa farare tass dake cikin takalmin wanka, seda ya cire su daga k'ofar toilet d'in sannan ya sako kansa zuwa cikin kyakykyawan bedroom d'in, k'arasawa yayi bakin k'aton mudubin sa ya sanya hannu ya d'auki comb ya fara taje sumar kansa data sha gyara sosae, banda ruwan daya ta6a ta a gyara take tsaf se tashin k'amshi me dad'i da take yi, yanayin

Table of Contents

Chapters

70 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70